Showing 90001 words to 93000 words out of 184071 words
Chapter 31 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
yane... kike min magana kamar wani danki,
in zaki jira motar karfe shida na yamma ki jira in baki iya jira wareee,
Cike da mamakin rashin ganin tsufanta tace
"kai da uwarka baku da tsofaffi a gidanku ne,
yaran yanzu sun fitsare kafarsu, basa ganin girman na gaba dasu, gaskiya anyi asarar haihuwa wallahi,
ta karashe tana kokarin jan jakar gana most go dinta,
"tare ta yayi da sauri ya busa ma fuskarta hayaki hade da cewa,
wallahi bazan duba tsufanki ba zan yaga miki chuna,
zigidir zan miki anan gurin kika sake sako sunan gyatuma ta,
A fusace tace "nace kaci uwar ubanka,
kaji min dan iskan yaro,
ni nan da ka ganni bani da mutunci, zan iya yi maka mummuna illa in baka maida hankalinka ba,
"ehhhhh yeeeeeeee,
ya saki ihu hade da chukumar jakar Goggo yayi wurgi da ita,
nan jakar ta yage kayan ciki suka firfito,
wata katuwar kwalba wacce take nade a zani ta tarwatse ruwan cikin ya bata sauran kullin dake cikin wasu takardu,
ďaga hannu yayi zai kai mata mari drivern motar yayi saurin rikeshi,
"kyaleta GARO,
barta ta shiga bayan boot din ta zauna,
kallon Goggo yayi wacce ta tsurawa kayan da ta kwana tara a hanya tana nemansu,
wani irin tukuki taji a zuciyarta tayi kukan kura ta kama wuyan Garo,
Dagewa yayi iya karfinshi yayi wurgi da ita gefe hade da zaro zarbebiyar wuka mai kyalli,
nan take Goggo ta maida hankalinta ta mike tana kukan wayancewa hade da cewa mutanen dake rike Garo
"yanzu dan Allah in ba sauyin zamani ba wannan yaron banyi jika na uku dashi ba,
"Na sha tara kikayi dani dan mai cin-----
toshe mishi baki drivern yayi yace
"yi hakuri Garo,
nasan laifinta ne,
ka barta ta shiga mota mu tafi,
maida wukar yayi yana ta muzurai hade da hararar Goggo,
sum sum ta wuce tana kallon jakar da ta sha wahala ta kashe makudan kudi dan samo su,
"tuno kashedin da bokan yayi mata na ta kula da kayan domin a shekara sau daya ake samun sa'ar samunsu,
wasu zafafan hawaye ta share zuciyarta a dagule ta nufi bayan motar inda kayan mutane suke,
"tana zama taji kukan talotalo a cikin wani kwali a bayanta,
Tagumi ta zuba saboda shiga wani yanayi da tayi,
yanzu ya zatayi ta sake samun wannan sa'ar,
bazata ta taba bari tayi wata daya da Anni da papy ba tare da ta illata su ba,
so takeyi taga bayansu dukkansu,
so takeyi ta mallaki zuciyar Baffa da gidanshi baki daya ita kadai kamar yadda tayi a baya,
daga ita sai yarta da jikokinta,
Tana cikin wannan tunanin mai cike da takaici drivern yace ta bashi kudi,
"nawa ne?
, jaka goma sha biyu,
"jaka har goma sha biyu, abin na sat-----
ganin Garo a bayanshi yasata saurin sauya maganar zuwa
"abin har yayi sauki haka,
fito da lalitarta tayi ta bashi kudin ciff,
irin kallon da Garo ke mata yasata saurin sunkuyar da kanta, shaff ta manta da yar posan kudinta a gefe,
tana jin motar ta fara tafiya, ta dago kanta,
tunane tunane ta shiga yi marasa dadi har bacci yayi gaba da da ita....
Mikakkiyar tafiya sukayi ta tsawon awa 8 saboda ana yi ana tsayawa Sallah da cin abinci,
Suna daidai *kawo* suka fara shelar kowa ya hada kan kayanshi domin yanzu yan kaduna zasu sauka,
Goggo da bacci yayi gaba da ita sam bata san sunayi ba,
haka drivern baisan kaduna tace ba,
da yake yan kadunan basu da yawa ko minti biyar basuyi ba suka daga zuwa garin gaba da zasu,
saboda tsabar baccin gajiya ko kuma ince hakki, saida suka kai bus stop din tafiyarsu da Goggo,
Nan drivern ya tasheta a gajiye dan bacci yakeji matuka,
a firgice ta tashi tana laluben poss dinta tana fadin har munzo Kawo?
Wani kawon? drivern ya tambayeta cike da kosawa,
"Kawo ta kaduna ďan nan,
tsaki yaja yace "dan Allah Baba fito kar in miki rashin kunya,
fitowa tayi cikin rashin fahimta tace "ban gane ba, ina ne nan,
rufe boot din yayi yace "je ki tambayi wadancan, ya nuna wasu gungun mashaya a gurin ya wuce yana mika hade da wakar dan kwairo ta "mai dakin gabas,
Zaman dirshan Goggo tayi a garin da bata san ko ina ne ba,
saboda baccin da ta tika idonta ya soye sam bata jin shi,
ga muguwar yunwa tana ji,
ga bakin cikin satan da akayi mata,
Tashar cike take da mashayan da basu da aiki sai na shaye shaye duk minti,
mayafinta ta cire tayi matashi dashi, ta rasa yadda zata fassara irin hau din da hauta a wannan rana,
saboda tsabar takaici har sambatun bacin rai takeyi,
ga tsabar ciwon kai da ya sata a gaba,
Wani mai butar shayi ne ya gifta tayi saurin kwala mishi kira,
dawowa yayi da sauri dan a tunaninshi siya zatayi,
"sannu ďan albarka,
nan wani gari ne dan Allah?
"Tashar Akwanga!
bakisan a Nasarawa kike ba,
wani kululu Goggo taji ya taso mata,
nan take hawaye ya wanke fuskarta,
da yaron yaga ba siya zatayi ba yayi saurin mikewa ya nufi gurin wadanda suka kirashi,
kuka mai hade da majina Goggo tayi shi a daren ranar,
maimakon ta saduda tasan hakki ne ya fara dawainiya da ita sai ta kara kullatar bayin Allahn da zata sake ninka zunubbansu akanta....
Motar dake tashi da asuba zuwa kaduna tabi tanata roko su sata ko a sama ne,
tana cikin wannan magiyar taji muryar da ko a mafarki taji ta zata ganeta,
"Rilwanu ta fadi bakinta kamar gonar auduga,
daga ina kake?
Nuna mahaifinshi yayi yace daga Benue muke zamu wuce kaduna,
wannan Mahaifina ne,
kamar yadda na fada miki zan dawo dashi kaduna in nema mishi magani,
da yake a cikin duhun subahi ne sai basu samu damar ganin fuskar juna ba,
nan dai Goggo ta shiga aljihun kaskastaccen bawan gidanta Rilwanu......
Firgai firgai ta shigo gidan yunwa kamar zata kasheta,
a lokacin har masu ginin sunzo,
da masu gyara mata daki da masu karasa ginin da ake buga kwano,
goge idanuwanta tayi dakyau ta fara dubawa ko ba gidanta ta shigo ba,
dakin waje shi ya tabbatar mata da gidan ta shigo,
zagaye dakunan tayi hade da fadawa dakinta,
wani irin ja baya tayi cikin firgicin rashin ganin ko tsinke a dakinta sai ma hake haken kasa da akeyi ana sa tiles masu kyalli,
nan take yunwar da takeji tayi murabus a cikinta ta fara fadin,
"uban waya saku fasa min daki, ina kuka kai min kayan daki?
Tabdijam,
wallahi hukuma ce kadai zata rabani daku,
ashariyya ta fara kundumo musu babu kakkautawa,
Muryar Papy tajiyo daga tsakar gidan yana sallama,
fitowa tayi da sauri har tana tuntunbe,
tana fitowa Baffa ya murda kofa ya fito yana amsa sallama,
baki ta saki tana kallon yadda muhammadunta ya canza a cikin yan satittikan da ta tafi ta barshi,
gaba daya an aske farin gashin dake gemunshi da kanshi,
tsufanshi ya boye sai wani annurin kyau da yake fitarwa,
Bugaggiyar shadda blue ce a jikinshi sai hula da takalmi masu matukar kyau, ga wani uban kamshin turare da yake fitarwa,
duk su biyun ta kalla taga kayan nasu iri daya har dinkin ma,
bata kara shan mamaki ba sai da jiyo sallamar Daddy,
kallon hanyar shigowar tayi taga ya shigo da danyar gezna ash,
bayanshi Musaddiq, Hafeez da Jamal ne suma sunyi kyau sosai,
*Zuri'ar Atika*
ta fadi a hankali,
wata juya ta fara ji wacce ta sanyata yin zaman dirshan,
Papy ne ya fara isa gareta yana fadin
"subhannallah, Inna lafiya?
ina kika tafi har wannan lokacin kika barmu da jimami,
bata iya yin magana ba sai kukan takaicin da ya kufce mata,
taruwa sukayi akanta harda Baffa suna mata sannu, dan yanayinta na marasa lafiya ne,
dakin waje suka shiga da ita Baffa ya tsaya a kanta yana mata tambayoyin inda ta shiga,
kureshi da ido tayi alamar tuhuma,
ga mamakinta murmushi yayi kamar yaro karami,
haibarshi ta lokacin samartaka ta tariyo kanta,
shi ma ita din yake kallo amma fa a tsorace yake dan yana tsoron abun da zai canza ra'ayinshi akan auren nan,
dan kwanakin da ya jera yana haduwa da Anni yaji tayi matukar kwanta mishi a rai,
yana fatan suyi zaman tare har mai rabawa ta raba,
"Biki akeyi na ganka da sababbin kaya?
yadda ta jefo tambayar sai ta bawa mai kallonta tausayi,
"Gyada kai yayi yace "eh bikin Muhammadu da Hanne,
agogon bango ya kalla yace
"goma daidai za'a daura,
yanzu tara da rabi,
bari muyi saurin zuwa gurin, akwai kayan abinci a cikin drawer can kiyi kokari kici kafin mu dawo, sai ki fada min inda kika je kuma da izinin wa,
*IZINI*
Goggo ta maimaita kamar me koyon magana,
yana gab da fita tayi karfi da jikinta ta damki babbar rigarshi hade da fadin
"wallahi babu inda zaka,
kai baka isa ka wulakanta ni ba Muhammadu,
ko kunya bakaji,
banda jika har tattaba kunni gareka amma dan budurwar zuciya irin taka harda yin anko kai a dole zaka angance,
to wallhi saidai in ka kasheni ka ka fita,
saboda rashin kuzarin da take ciki yasa shi kwace rigar yace
"Raya sunnar ne abin kunya, bazan kasheki ba,
kuma aure babu fashi mutuwa ka raba,
yana kaiwa nan yasa kai ya fice,
"aiko zaku mutu,
wallahi tallahi kaji rantsuwar da bata da kaff------
ido cikin idon da sukayi da Daddy ne ya hanata karasa mummunan furucinta,
ciki ta juya hawayen ido suka kafe sai na zuci da suka dinga kara kaini,
kasa zaune tayi tanata safa da marwa tana tunanin ta inda ta kuskuro har wadannan abubuwan suka cakude mata haka,
ga kayan dakinta duk an fitar dasu bare ta samo wasu cikin surkullenta tayi amfani dashi,
dakyar ta zauna tana maida numfashi kamar zata mutu......
Foiling naman walima Nadeeyah da Husnah sukeyi a cikin tray suna hira,
Mummy na bayansu tana hada coleslaw na dole dan ba yadda zatayi Daddy ya dauki nauyin walimar a gidanshi,
suna gamawa suka jere komai a inda ya dace,
rissinawa Nadeeyah tayi tace "Mummy akwai wani abun ne?
gyada tayi kawai alamar a'a kamar me ciwon baki,
Daki suka wuce dan yin wanka,
kaya kala daya Papy ya dinka musu harda su Anty Raly,
lace ne dark purple mai ratsin manyan pattern pink flower,
dinkin riga da skirt mai matukar kyau,
ko ina an sanya farin stones wanda ya kara kayata lace din,
*Bismid cream* Husna ta dauko tana shafawa tana dariya,
wayaga Baffa ango,
wallahi ni abun kunya ma yake bani,
su Daddy kuma harda wani daurewa karya ...... wai harda walima,
dariya Nadeeyah tayi hade da jan zip din rigarta tace
"ni kaina abun jinshi nake wani iri,
saidai ba yadda za'ayi da hukuncin Allah,
Badar sarkin nukufurci tana kwance cikin bargo tana latsa waya bata ma san suna shiri ba,
light make up sukayi wanda ya dace da fatarsu,
sunyi kyau sosai saboda lace din kalar farare ne,
dauri sukayi mai matukar kyau iri daya suka feshe jikinsu da turaruka masu kamshi da saukin karfi,
kara wayar Nadeeyah tayi alamar shigowar sako,
da sauri ta dauka dan tasan wanda yayi text din,
"baya kiranta a waya, amma text duk minti biyar yinsa yakeyi,
ko ya rasa abin cewa sai ya nemo write up na yaudarar maza, ko yadda zata kula da kanta, ko adduoi ya tura mata,
reply dinta koda kalma daya ce means the world to him,
*Yunwaaaaaaaa, plss ku kawo min abinci kar in mutu*.....
Dariya sosai tayi dan ganin mai sakon, ta mikawa Husna wayar,
itama dariyar tayi tace acici,
kinsan yau ya tashi da wuri to fa kowa ya bani a gidannan,
flat shoe suka saka suka wuce kitchen,
flask Nadeeyah ta dauka da hot chocolate da ta san yafi san karyawa dashi,
ita kuma Husnah ta dibi naman kaza cikin pepper din da sukayi foiling,
wani sakon ne ya sake shigowa..
*Nadeeyah so kikeyi in mutu ko, ba komai... ya sanyo alamar kuka*
Reply tayi mishi tana murmushi tace
*Sorry, kana ina ne*
Yana ganin reply din yayi saurin kiranta
"ina BQ, yanzu muka dawo,
plss kiyi sauri cikina na ta kiran sunanki,
yasan ke kadai zaki taimaka,
kashe wayar tayi tana dariya suka wuce BQ din,
Murda kofar Husna tayi saboda ita ke da rangwamen kaya a hannu,
karo tayi da mutum shima ya sako kai zai fito,
subhanallah ta fadi hade ja baya tana kallon tray din da ya fadi kasa,
kallon shi tayi taga shaddarshi ta baci da source
"Ya salam.. Ya Hafeez dan Allah kayi hakuri,
wallhy bansan zaka fito ba,
Murmushi yayi yace "haba karki damu,
da kinsani bazaki shigo ba nasani,
ke da gaisuwa ma sai na roka, yaushe zakiso kiyi karo dani,
dariya tayi sosai tace
"kiji sharri Nadeeyah,
bari in duba maka kayan Ya Musaddiq ka canza,
"inyi yawo dai a ciki ya fadi yana goge jikinshi hade da kallon Musaddiq da yayi fuskar tausayi,
dariya yayi ya kalli Nadeeyah yace
"saura kiris a zare ran fa,
maza kije ki bashi break fast..
Da sauri ta zare takalmin kafarta ta shiga da sallama tana fadin "sorry pls,
rike cikin yayi ya kara bata fuska yace
"naki sorryn na koshi,
bude flask din tayi ta zuba ruwan zafi ta hada mishi tace
"gashi kayi hakuri dan Allah kar a zare ran,
in aka zare bamu san inda zamu sa kanmu ba,
"Dadi zakuji mana ku huta da acici,
sosai sukayi dariya Nadeeyah ta gimtse tata dariyar tace
"ai ci dole ne yayana,
kowa ma acici ne,
gashi kaji, plssssss, ta fadi tana karkace kai gefe,
"badan ni zansha ba sai dan tausayin hanjin cikina,
Saboda dariya saida Nadeeyah ta durkushe a gurin,
"dan Allah karka kashe ni,
bari in kawo maka wani abinci me nauyi,
kallon Husnah yayi dake kara jaddaddawa Hafeez suje ta bashi kayan shi ya saka,
"in kinje ki bashi riga kadai ta isheshi,
kinga sai kuji dadin zagin halitta ta,
ya karashe yana kai kofin bakinshi,
dariyar ma kin fitowa Husnah tayi suka fita tare da Nadeeyah,
Dariya Hafeez yayi yace
"manta da ita kaji,
gida zan koma in canza kaya,
bari in kira Jamal ya kawo min mota,
ciro key Musaddiq yayi yace "ga tawa kaje ka dawo kafin a fara walimar,
karbar keyn yayi yace "ka dai ajiye min nawa abincin kar ka cinye kai kadai,
"Haaahaha...
zan daina cin abinci kwata kwata a idon mutane,
gara in rage wannan kibar,
da zan iya ma harda tsawo zan rage,
"dariyar Shirmen Musaddiq Hafeez yayi ya fita yana jin dadin yadda al'amura suke kasancewa kamar yadda Mamma take so,
Allah sarki Mamma,
ina ma ana mutuwa a dawo kiga yadda wuya take neman rikide mana ta zamto dadi,
kiga yadda dan uwan da baki sani ba yake gatata mu kamar shi ya tsuguna ya haifemu,
Allah yayi miki Rahama ya fadi ya shiga motar zuciyarshi a dagule saboda tuno iyayenshi da yayi.......
Ana idar da sallar isha'i su Nadeeyah suka fara shirin barin gurin su Anni,
hankalin Nadeeyah a kwance ta gama shiri dan tasan yanzu su Anty Radiya sun bar gidan,
"kallon banza da habaicin talauci hade da rashin asali da suke mata yana sosa ranta matuka,
kalmar da Anty Raudah ta fadi na "anyi clean fata ta murje da abinci akan kari sai kace wata yar shugaban kasa,
a dai dinga tuno asali dan kar garin iyawa a wuce gona da iri!!
Wadannan kalamai sun matukar tsaya mata,
dan ma Musaddiq dake bayanta wanda dan shi Anty Raudah tayi mata habaicin yace
"Haba Anty, sai kace sa'arki,
dani take magana bada ke ba,
ku ke jawa kanku raini wallahi, yayi tsaki a hankali hade da cewa Nadeeyah ta kira Husnah su tafi...
Hannu ya kyasta mata a kusa da idonta,
a firgice ta dawo daga tunanin abubuwan da suka gifta dazu a gidan,
rage Murya yayi yace
"Tunanin su Anty ko?
Abin da ya kamata ki saba dashi ne tunda saidai in basu zo gidan ba,
in kika kula mutum a kullum burin shi ya bata miki rai to sai kiyi fatali da duk abin da yace, domin shi kadai zaiyi dakon bacin ransa,
"Zuciya is very special my sister,
fill it with love,
karki bari bacin rai ya samu kofar shiga cikinta, dan bacin rai na destroying duk abin da aka tanadarwa zuciya, dan haka bana san ganin tunani ko bacin rai nan a tare dake,
kinji ko?
gyada kai tayi hade da murmushinta mai kyau,
"Thats my lovely sis,
oya kira mana Husnah mu tafi,
kafin ta kai ga amsawa suka hango Husnah sun fito tare da Hafeez da Ruwaidah a tsakiya,
gefe kuma Jamal ne sanye da kayan bacci shima yana dosar inda suke,
"Badai bacci zakayi ba,
Musaddiq ya tambayeshi yana mishi kallon mamaki,
jingina jikin motar yayi yace
"in banyi bacci ba ai sai in kasa moruwa,
yau ko tamola bata kaini garuwa ba,
wahalar da Baffa ya bani yau ba kadan bace,
"duk wani abokinshi da yazo gurin daurin aure wanda baida mota saida na maidashi gida,
just imagine kaine,
hmmm thank Goodness akwai ruwan zafi,
da yau sai na tashi aiki, ya karashe yana danna bayanshi,
"Lazy youth!!
Ruwaidah ta fadi tana boyewa a bayan Hafeez,
dariya ta basu dukkansu Nadeeyah tace
"duk kokarin nan da yayi ki kirashi lazy,
murya cakwai tace
"Allah Adda he is very lazy and he can exaggerate,
yanzu haka gida uku yaje,
haka Mami ke fama dashi baya san a moreshi,
Rai a bace Jamal yayi inda take yana fadin
"ni sa'anki,
wani irin ihu ta saki hade da rugawa ciki,
bayanta yabi da gudu dan yaci alwashin ko a gaban Papy ne sai ya gurji bakinta,
Dariya Hafeez yayi yace ku shiga mota ku tafi dare nayi,
indai su Jamal ne kullum sai sunyi sau ba adadi,
ya kasa gane dadin tsokanarshi takeyi,
saboda bata da abokin wasa shiyasa ta maidashi abokin wasanta, shi kuma san girma yasa baya wasa da ita,
" haushin hakan yasa ta rainashi sosai,
motar suka bude suka shiga suna dariyar Ruwaidah da Jamal,
Sallama sukayi ma Hafeez da