Showing 111001 words to 114000 words out of 184071 words

Chapter 38 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt

karfin gwiwar bada tashi amsar,

farin ciki marar misaltuwa Papy ya shiga..

sallamarsu yayi hade da kiran Daddy ya labarta mishi,

Daddy cike da jindadi yace to ai bazamu jira ba,
gara a hade bikin ayi shi rana daya,
nan suka gama tsara yadda zasuyi sannan sukayi sallama cike da jindadi....




Kwanciya Daddy yayi yana kabbara da girmama hukuncin ubangiji,
wato ubangiji ya hanashi auren Suwaiba saboda wannan ranar da auratayya zata bullo a tsakanin jinin da suka yi tsaftattaciyar soyayya ta tsakani da Allah,


lallai
*kaddara*
itace jigon rayuwar dan Adam,
domin da ita yake yawo duk inda zashi....
ina ma Suwaiba zata dawo taga hukuncin ubangiji,
taga yadda rayukan 'yayanta suka canza,

wata yar kwallar murna ya share yayi adduoinshi hade da runtse idanuwanshi......




Hauka ne kadai Mummy bata yi ba da taji labarin hade auren harda na Husnah da suka gama maganarta da kawarta Hajiya Safara'u,
babu irin masifar da batayi ba,
shiko Daddy ko a jikinshi kudin kayan kitchen ma yayi mata transfer zuwa account dinta dan sauran da kanshi zaiyi su,


Sa kai yayi ya fita ya bar gidan dan lagos ma zai tafi da daddare akan maganar gidan da aka samu...




Kuka ta zauna a parlor tana yi sosai kamar an mata mutuwa,
bakin cikin da take ciki yau har gwammaci dama bata taba sanin Daddy a rayuwarta ba,


Badar ce ta fito tana hamma,
duk wainar da ake toyawa a gidan bata da masaniyarsu dan ba zaman gidan takeyi ba,
da sauri ta isa gurin Mummy tana tambayar abun da yasa ta kuka,


Ganin da tayi wa Badariyya ya sa hankalinta dan kwanciya,
dan wani abu da ya darsu a ranta,
tasan Badariyya ce kadai zata iya yi mata maganin damuwarta...



Hannunta ta rike ta sake rushewa da kuka tace

"Badar na shiga uku,
Musaddiq zai auri Nadeeyah, Hafeez kuma Husnah,

kinji a inda zan kare a ya'yan da basu da asali,

yayan mai gadi ni zainab.....



Wani irin ihu Badar ta saki tace

"Whattt?

Nadeeyah zata auri Musaddiq dina....
ta fadi hannu na rawa tana dafe kirji.......




Mrs Tijjani Shattimah........
[11/04 12:07 AM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣6⃣
By *Aysha Ya'u kurah*





Mikewa Mummy tayi zuciyarta ta fara sanyi na yadda taga Badar ta harzuko, tasan tabbas Badar bazata taba bari auren nan ya tabbata ba koda kuwa zai zama ajalin Nadeeyah...



Hannunta ta kamo tace "Musaddiq dinki Badar,
mun gama magana da wani malamina akan halascin aurenku, da murnata nazo na fadawa Daddy,
shine yake cemin wai ai Papy Saif yazo mishi da maganar yanason hadin auren Nadeeyah da Musaddiq,
shi kuma nan take ya amsa mishi saboda kinsan yadda Daddynku yake da s-any-in haaa--li,
ni yanzu bansan yadda zanyi da raina ba,
ta karashe da kuka sosai wanda yake nuni da tabbas tana bukatar taimakon Badar...




Furzar da huci Badar tayi murya a kausashe tace
"Wallahi bazai yiwu ba,
na dauki alwashin saidai Musaddiq ya zauna babu aure in har ban halasta a gareshi ba a baya lokacin da kika ce ba aure a tsakanin mu,,
bare kuma yanzu da na tabbatar na halasta a gareshi zan yarda ya auri wata,
watar ma Nadeeyah,

wallahi Mummy saidai ayi auren nan babu raina,
bazan ma mutu ba,
sai dai ita ta mutu,
hannu ta daura kan kafadun Mummy tace
"ki kwantar da hankalinki,
kima daina kuka,
kisa ma ranki salama yau zuwa gobe zakiji sabon labari,


zaunar da ita Mummy tayi cikin tsorota da yanayin kalamanta tace
"Badai kauce hanya zakiyi ba?

Dariya Badar tayi tace "karki damu nace,
badai kin yarda da batun aurena da Yaya Musaddiq ba?

Gyada kai Mummy tayi tace
"eh,
a zuciyarta kuwa tana jin tsoron karyar da tayi ma Badariyya, tasan sarai in auren nan ya lalace wata rigimar ce zata sake bullowa,
kauda zancen tayi a zuciyarta, dan tasan yadda zata tafiyar da Badar bayan maganar auren Nadeeyah ta lalace......




*KUNGAMAR GARZAR*



Washhhhh....,
na taka qaya,
duba min kigani Lawisa Lawal,
hannunta Lawisa ta kama tace "sauri fa zamuyi Badar,
kina ganin har la'asar tayi bamu karasa ba,
dajin nan is very dangerous, nima Anty Laurah ta taba kawo ni, ban taba tunanin ma zan gane ba,
dan Allah ki dago kafa,

"dingisawa Badar tayi ta sake yin ihu hade da tsugunawa ta cizge kayar,
bata damu da jinin da ke bin kafarta ba tabi Lawisa suka dinga sauri cikin dajin,

minti talatin suka kara suka isa gaban wata katuwar bukkar fulani,
almajirai ne kewaye da ita suna kara kaini da alluna,
sai gungun kyawawan yaran fulani daga can nesa suna wasan kasa, matan na yar gala gala...



Suna shiga gidan suka bangaji wata yar budurwa da ta arto a guje tana ihun kuka,

wata katuwar farar mace fuska duk kalangu na biye da ita da bulala a hannu tana zaginta da fulatanci,
ramawa budurwar takeyi tana fadin

"Allah ya isa muguwa, azzaluma, bazan yi wanke wanken ba,
in kinga dama ki kashe ni,
ganin su Badar ya sanya matar yar da bulala tana fadin "marabanku,
ku shigo daga ciki,
a darare Badar ta kalli matar sannan ta kalli Lawisa dake kokarin janta zuwa ciki,
zatayi magana kenan Lawisa tayi mata alama da tayi shuru su shiga daga ciki,
a tsorace ta fara bin Lawisa da matar har suka isa wata lafiyayyar bukka dake kawace da adon fulawoyi,

"babu abin da ke fitowa a bukkar sai hayaki mai karfin kamshi wanda ka iya buga kan mutum in ya shakeshi na tsawon minti goma,
da sauri Badar taja gyalenta ta rufe hancinta gabanta na tsananta faduwa,
a zuciyarta tana dana sanin biyo Lawisa gurin nan da tayi..


" *Lawisa ta dade tana bata shawara akan tazo suje inda zata karkato da hankalin Musaddiq da Mummy su yarda da aurensu koda kuwa bai halasta ba Badar taki, saboda a ganinta zata iya shawo kan komai saboda irin soyayyar da Mummy ke mata, jin batun auren Nadeeyah da Musaddiq shi ya harzukota ta nemi Lawisa suka taho ba bata lokaci, bata san azal ke kiranta ba*

katse mata tunani Lawisa tayi tace
"ance mu shiga Badar,
firgigit Badar tayi ta cire takalmanta suka fada cikin bukkar,


Suna suka saka kafarsu a ciki hankalinsu ya gushe suka manta inda suke,
sai ganin kansu sukayi a cikin wani kayataccen parlon da duk iya maitar mutum bazai san ta inda yabi ya shigeshi ba,
jiki na rawa Badar ta damki hannun Lawisa suka zauna a gaban wanda Badar tafi zaton shine bokan,
gefenshi kuma saurayi ne dan shekarun da basu fi talatin da biyar ba yana zaune shima da kayan tsubbun a gabanshi,
dago kai saurayin yayi ya kallesu yace

"Badariyya da Lawisa barkanku da zuwa,

nan cikin Badar ya duri ruwa saboda tsabar tsoron da taji,
a ina yasan sunan su?
Tambayar da ta dinga yi ma kanta kenan,


"Nasanki tun ranar da kika duro duniya Badariyya,
babu motsinki da ban sani ba,
har wannan zuwan da kikayi na sani,
dan ni na shiryashi,
gefen da Lawisa take ta kalla nan da nan ta saki hannunta saboda wata iriyar dariyar da takeyi mata mai cike da ban tsoro,

mikewa lawisa tayi tana dariyar da ta ke amsawa a cikin dakin, sannan ta Kalli Badar tace

"ke matar dan sarkin mu ce, wannan shine

*Sarkin bokaye Shahalu*

sai danshi
*Yareemah Suhailu*
karki damu Badariyya,
ni kawarki ce kamar yadda kika dauka,
amma ki sani na zo gareki ne saboda wannan ranar da zan cikawa Sarkin mu burinshi,

"ni ba mutum bace,
amma sarki da yareemah mutane ne kamar ke,
kyakykyawar mu'amalar dake tsakaninmu dasu ita ta janyo har na taimakeshi,
ki kwantar da hankalinki yau kinzo inda kaddararki take,
zaki ji dadin zama dashi da yan uwanshi,
bissalam kawata Badariyya....
ta karashe tana daga mata hannu tana dariya har ta bacewa ganinta,


wani irin ihuu Badar ta saki tana bin gurin da lawisa tabi,

"wayyo Allah Mummy ki taimakeni,
wayyo Allah Daddy,
na shiga uku na lalace,
wayyyyyo Allah na,


keeeeeeee!!!


Wata irin tsawa taji daga bayanta wacce ta sanyata dunkulewa guri daya,

murya a kausashe Sarkin bokaye yace
"Karki sake yi min ihu anan,
kin san Allah dama?
In kika sake kiramin sunan Allah anan zan cire idon ganinki,
na rantse da abun bautarmu *GARGAZ*,

Kee... *Kande*
ya kwala kiran katuwar matar da ta shigo dasu,
Da sauri ta karaso ta tsuguna a gabanshi tace
"Ranka ya dade gani,

"Maza ki dauketa ki kaita cikin gida dakin da *Halyo* ya gyara jiya,
an sa gado da katifa dama,
jiran zuwanta kawai akeyi, sannan ki jawa
*Gimbiya Sailuba* kunne,
babu ruwanta da kishi da ita,
domin wannan itace matar Suhailu ta farko,
tun kafin tazo duniya Mahaifiyarta ta bashi,
sai yau *Garzar* ya bamu ikon dawo da ita gurin mijinta,

cike da girmamawa Kande tace "to ranka ya dade,
an gama,
nan ta damki hannun Badariyya tana janta a hankali Badar na turjewa tana ihun neman dauki a inda babu mai jinta sai Sarkin sarakunan da biyayyarshi bata dameta ba,
sarkin da a sati baifi ta gaisheshi sau daya ba,
sarkin da ya hore mata lafiya da kuma abun da lafiyar zata ji dadi...
*ALLAH AZZA WA JALLAH*

shi kadai zai fidda Badar daga kangin da take ciki......
*SHIN INA BADAR TA FADO*


_(fadan da yafi karfin ka ya kai dan uwa, bar wa Allah yayi maka shi, domin shine mai dukkan karfi.......)_





Tun Mummy na jiran Badariyya a daki, har ta koma leke ta window da kofa,

karfe 11 agogon parlon ya buga,
a tsorace ta sake kiran Badar karo na ba adadi,
har lokacin wayar a kashe take,


zama tayi akan kujera ta Shiga jero salati,

"Ina Badariyya ta Shiga har wannan lokacin,
ya ilahi kasa ba wani abun bane ya same ta,
tagumi tayi tanata sambatu dan hankalinta Sam yaki kwanciya,


Har karfe 1 na dare babu labarin Badar,
sai a sannan ne ta fara kiraye kiraye waya tana kuka Dan gaba daya ta gama tsurewa,
duk wanda ta kira wayarshi a kashe,
wayar Daddy ce kadai ta shiga,
shi kuma bai dauka ba saboda gajiya da yayi,

yar da wayar tayi ta fashe da kuka tana dana sanin barin Badar ta fita,
gaba daya idonta ya rufe burinta kawai a fasa auren Nadeeyah da Musaddiq,
Sam bata hango matsala a fitar da Badar tayi ba,


sai gurin hudu bacci barawo yayi gaba da ita,
ana idar da sallar asuba Daddy ya kira ta saboda ganin misd calls dinta da yayi,


firgigit...
ta farka tana fadin Badariyya,
"Hello Badariyya kina ina?,
gyaran murya Daddy yayi yace "ina Badariyyar ta tafi?

Wani irin kuka Mummy ta fashe dashi tace
"Badariyya bata kwana a gida ba,
na rasa inda ta tafi,
na kira wayarta har naji ba dadi na kasa samunta,

cikin halin ko in kula Daddy yace
"kinsan duk inda take zata dawo, ki kwantar da hankalinki, ai ba yarinya bace, big girl ce..
na turo miki kudin kayan kitchen,
zuwa anjima kuje ku siyo,
bana son muyi abubuwa cikin kurarren lokaci,
yana kaiwa nan ya kashe wayar,


Ajiye wayar tayi ta cigaba da rero kuka,
"da wani baki zata fada musu cewa tana da masaniyar inda Badar taje,
wa zata fadama ya fahimceta har ya taimaketa,

Goggo ce ta fado mata a rai tayi saurin kiranta,
saida wayar ta kusa katsewa sannan ta daga dakyar,
yanayin muryarsu daya ko wannensu cikin kunci yake,

Mummy ce ta fara fada mata damuwarta,
nan take Goggo tace
"rabu da ita zata dawo da kafarta,
kin manta haka uwarta ma tayi,
kina zaune zata dawo,
ke dai kije kisan yadda zakiyi wadannan matsiyatan kar su shigo cikin zuriarki, dan babu alkhairi a duk inda suka sa kafa..
da kalaman Goggo hankalin Mummy ya kwanta ta mike tayi wanka tayi sallah sannan ta zauna tana tunanin ta inda zata bullo,


kawarta Hajiya Martai ce ta fado mata,
nan ta kirata ta kora mata matsalolinta,


minti talatin Hajiya Martai ta bata tace ta sake kiranta zata sa wani malami yayi bincike akai,


ko minti daya bata kara akan minti talatin din ba ta kirata,

a sanyaye Hajiya Martai tace

"Hajiya zainab wannan auren babu abinda zai hana shi sai mutuwa,
akwai rabo mai karfi a tsakani,
kuma akwai wani babban al'amari da zai taso marar dadi wanda Allah ne kadai ya barwa kansa sani,

saboda haka shawara ce zan baki,
in dai ba so kikeyi ki mutu ayi ba,
to ki kwantar da hankalinki ayi kina da rai,
bayan an daura sai ki shigeta kuyi mata illa har su rabu,
amma tabbas akwai aure a tsakaninsu,

Ajiyar zuciya mummy tayi hade da share kwallar takaicin da ta ziraro mata tace
"to Hajiya martai nagode kwarai,
in shaa Allahu naji shawararki, kuma zanyi amfani dasu...

shawarwari ta dinga bata marasa amfani na yadda zata kori Nadeeyah cikin kankanin lokaci,

sunfi minti talatin suna waya sannan sukayi sallama,
sai a lokacin Mummy taji wasai ta mike da karfinta ta shirya zuwa kasuwa......



Shirye shiryen biki sukeyi ta ko wani bangare,

Mummy da ahalinta sun danne bakin nufinsu sunata kankajere suna hidima da jikinsu da kudinsu,
kowa ya manta da lamarin Badariyya saboda Mummy tayi musu karyar ta tafi cotonou makaranta,
amma a zuciyarta kullum sai tayi tunanin inda Badar take da har wannan lokacin bata ziyarci gida ba,
in ta tuno kalaman Goggo sai ta kwantar da hankalinta ta cigaba da cigaba da zuba idon ganin dawowarta...



Anni itace ta dauki nauyin su cincin da dublan da sauran tarkacen garar amare,

ita kuwa Goggo ba baki dan mugun tsoron Anni yanzu Allah ya daura mata,
ta kan ce
"ina zata iya da wannan matsafiyar,
saboda duk asirin da ta dunkulo sai dai ya koma mata ko ya wargaje,

ita a ganinta tsafin Anni ne yafi nata,
bata san dogaro da Allah yafi tsafi karfi ba....




Tun ana saura kwana uku daurin aure Anty Reemah da Papy suka iso,
babu yadda basuyi da Hilal ya biyo su ba, yace sai daren daurin auren zai shigo,
hakanan suka kyaleshi sukayi gaba abinsu...




Duk yadda suka so suyi bidi'a Mummy ta hana a cewarta Daddy yace bayason komai sai daurin aure,
kawayenta ma babu wanda ta gayyata sai makota na kusa da ita,


Bikin ya kasance na yan family kawai sai kawayen su Anty Raliya da yan Gombe da yan maiduguri dangin Daddy...





Ranar jumm'a ake kamun amare,
a cikin gidan akayi decoration wanda ya kawatu da kore da kumbo,



Blue kayan kanuri suka sa dukkansu,
fuskar nan tasu ta dau kwalliya gwanin kyau da sha'awa,

kawayen Husna da yan tsirarrun na Nadeeyah sunyi ankonsu wanda ya dace da kayan amaren,
sai su Anty Reemah suma sunyi nasu lafaya mai kyau da tsadar gaske,
babu abin da ke tashi a gidan sai kidan piano da wani kwararren mawaki keyi,
kida ne taushi mai ratsa zuciya,


Ruwaidah da Zainab ne kadai a cikin tsakiyar filin suna rawarsu ta yaran da basu da wata matsala a rayuwarsu,
sai gefe yaran makota suma suna rayawa dan kar a barsu a baya,



Muryar inna Surayya (M.C Surry k mata) ce ta karade gidan da barkwancinta,
nan manya da yara suka hau dariyar labarin da take bayarwa,



Hinad...

Anty Reemah ta kwala kiranta da karfi..
da dan gudu ta karaso gurinta bayan ta amsa tace
"Mum gani,
wata leda ta mika mata tace "maza ki kaima Uncle links dinshi, nasan yana can bai gama shiryawa ba,

cire dankwalin kanta tayi ta karbi links din ta wuce dakin Musaddiq...





A zaune ta sameshi ya tasa kaya a gaba yana tsaki,
ya rasa taka mai mai kayan da zaisa cikin sabbin kayan da ya dinka,
gashi sai kiran wayar Nadeeyah yake taki dauka,
rabonshi da ya sata a ido tun ranar da ya koma lagos,
sai jiya da suka iso daga Gombe, shima daga nesa ya hango ta,
gaba daya ta toshe duk wata kafar da zata hada da shi,
a waya ma saidai in ya kira Hafeez sannan ne zata amsa,
shima bawani maganar kirki, zata kashe...




"Uncle baka shirya ba?

tsaki ya sake yi yace
"Hinad ban shirya ba,
zo ki zabar min kaya,
banason inyi shigar da zata banbanta da ta matata,


"Ummm ta fadi tana dariya hade da janyo wata danyar blue shadda taji aikin dark blue,
tace "wannan is okay uncle,
tun dazu uncle Hafeez ya shirya kai kana zaune,
plss hurry up,

kayan ya kwasa yace
"i hate Hilal,
shi ya kamata yayi min wannan ya wani ki zuwa,


"kunfi kusa ta fadi hade da ajiye links dinshi a kan kayan ta fita waje.....




Laaaaa Ya Hi----
toshe mata baki yayi hade da rungumeta yace
"nasan yayi fushi,
karkiyi magana yaji,
jeki kawai,

sakinshi tayi ta wuce tana dariya..



Makale lnks din yakeyi yana tsaki hade da mita,
shi kanshi in ka matseshi baisan me yake fadi ba,
yadai san rabin mitar akan Hilal da Nadeeyah ne da suka barshi all alone...


karin hular dake ajiye akan gado Hilal ya gyara hade da matsowa cikin sanda ya daura mishi a kanshi...
*Kyari is nw Complete*
ya fadi hade da saita fuskarsu ta kalli mudubin,


wani irin farin ciki Musaddiq yaji wanda a iya rayuwarshi bai taba jin irinshi ba a ganin Hilal sai yau,


Da sauri ya rungumeshi yana fadin
"idiotic being, sai yau kaga daman zuwa,
komai ni kadai nayi,
from lagos to kaduna haka na dinga wahala sai Zubair dake dan tayani,
i hate you banza kawai,
ya karashe yana dukan kirjin Hilal,


dariyar yake Hilal yayi yace
"da haka zaka zama jajirtacce mr Soft,
maza da wahala aka sansu,
kaga yanzu zaka shiga sahun cikakkun maza,
dole komai kayi ma kanka,

"amma akwai support ko? Musaddiq ya fadi yana hararar Hilal,

dukan kafadunshi Hilal yayi yace
"nd here i am,
kasan bazan taba barinka kayi komai kai kadai ba,


"na nawa kuma,,
muje kasa kayanka gasu can a drawer,
Musaddiq ya fadi yana jan hannun Hilal,


Hannunshi Hilal ya rike sosai ya tako har inda yake ya kalli cikin idonshi yace

"Musaddiq promise me one thing,
alkawari daya kawai zakayi min,

"nayi maka alkawari dan uwana,
fada min menene,
nan idon Hilal ya fara kokarin canza kala yayi saurin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login