Showing 42001 words to 45000 words out of 184071 words
Chapter 15 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
takeyi saboda yadda ta dauka Suwaiba zata iya barin mata komai take bukata a rayuwa,
lallai a yanzu ne ta fahimci cewa uwa daya ya wuce wasa,
tayi imanin da Leemah ce zata yarda ta barta Mukhtar dan kar ta kunyata,
wata irin tsanar Suwaiba ce ta darsu a zuciyar zainab wacce dama ta dade ana mata aikenta, sai yanzu shaidan ya samar mata mazauni a zuciyarta,
barka da hutawa yaya, suwaiba ta fadi tana cire hijab dinta,
uhmmm!!
kawai taji tace sannan ta mike kafarta a kan gado,
gabanta ne ya fadi dan bata saba ganin hakan a gurin yar uwarta ba,
gefen gadon taje ta tsuguna tace "yaya ko na miki wani abu ne,
juya mata baya tayi tace "karki dameni suwaiba,
kaina ke ciwo,
nan take idonta ya ciko da kwalla ta mike ta fita kofar dakin,
kuka sosai ta zauna tana yi, zuciyarta sai kai kawo takeyi akan maganar da Goggo tayi mata,
sam bata damu da sanin cewa ba ita ta haifeta ba, dan ta dade da sanin uwar da ta haifeka baza tayi maka irin wannan tsanar ba,
abin kawai da ya daga hankalinta shine rashin sanin uwarta da kuma rashin adduar da bata samu daga gareta a matsayin sadaka a kabarinta..
yanzu kuma babban tashin hankalinta bai wuce na rashin walwalar da ta gani a gurin yar uwarta mai kaunarta ba,
tana wannan tunanin taji Ma'u tazo ta wuce cikin dakin...
Yanzu dai kinga halin wacce kika fifita akan yar uwarki,
kindai gani da idonki,
kuka zainab ta fashe dashi tace "Wallahi Goggo ina mutuwar kaunar muntari,
na dauka zan iya hakuri in bar mata shi,
amma yanzu da naga aski yazo gaban goshi walhy bazan iya hakura ba,
duk abinda da kika ga ya dace kiyi Goggo, nima ko meye zan yi walhy,
murmushi Goggo tayi a zuciyarta tace "wuya makarantar kare, waya fada miki borno a gabas take,
kwantar mata da hankali tayi tace gobe zatayi komai da tasan zatayi ta rabasu,,,
wani sabon kuka ne ya kufcewa Suwaiba da ta gama sauraren kalaman Goggo,
mikewa tayi ta je bakin pampo tayi alwala ta dawo dakin,
a zaune ta samu Leemah da yaya zainab suna magana kuskus,
darduma ta dauka ta fito waje tayi raka'a biyu ta zauna a gurin tana kai kukanta gurin ubangiji....
Baffa na fasa auren muntari! Wata iriyar faduwar gaba Baffa yaji wacce zata iya sanya zuciyar bawa tsayuwa,
hade rai yayi kamar bai taba dariya ba yace "wace irin magana ce kin fasa aure?, dama yardar aurenki da rashinshi duk a hannunki suke,?
dama ke kike da ikon zabawa kanki miji bani ba,
dan Allah ya kawo miki miji shine har kike da bakin butulce mishi,
lallai suwaiba ban taba tunanin baki da hankali ba sai yau,
idan kika sake furta min wannan kalmar walhi sai na lahira yafi ki jin dadi,
tashi ki bani guri sakarya kawai..
tashi tayi ta fita tana kuka a ranta tana fadin nima ba asan raina bane Baffa,
ina gudun a sabauta rayuwata da ta muntari ne,
ya zanyi in fahimtar dakai akwai matsalar dake shirin bullowa,
ya zanyi ka fahimci matarka wacce na dauka uwa marar kaunata Guba ce a cikin rayuwarka,
da wadannan tunanin ta isa zauren gidansu ta zauna akan dakali ta cigaba da kuka,
saida ta dauki kamar minti talatin a gurin sannan ta tashi ta wuce makaranta...
A dimauce ya dago kai ya kalleta sosai yace "maimaita abin da kika fadi,
cike da dakiya tace "kayi hakuri dan Allah ka janye batun auren mu da kai,
wallahi zuciyata ta kasa aminta da yin rayuwar aure dakai,
share zufar da ta keto mishi yayi yace "karyane! Wadannan kalaman ba naki bane,
ko kina da ciwon aljanu ne ban sani ba?
Hawaye ne ya fara zuba a idonta tace "Gaskiyar magana nake fada maka daga cikin zuciyat---- karya kikeyi! Ya daka mata tsawar da sake sanya ruwan idonta ambaliya,
sauke muryarshi yayi yace " baki da lafiya suwaiba,
kin gane ko, jeki gida ki kwanta,
"lafiyata kalau ta fadi murya na rawa,
ka fahimceni, rayuwar aure bazata yiwu da zuciyoyin da basu gama yarda da junansu ba,
nayi duk iya kokarin da zanyi in tusa sonka a raina na kasa,
kallonta yakeyi da manyan idanuwanshi da suka rine zuwa jajaye,
"me yasa kike kuka?
Karki damu share hawayenki,
share hawaye tayi da sauri, yauwa ya fadi hade da cewa kar in sake ganin kukan nan kinji ko?
Gyada mishi kai tayi tace "na daina,
"kin min alkawari?
Eh "Nayi!
Yauwa matar Muntari, kin gane ko,
dama ni bana son ki soni,
son da nake miki ya isa,
ni fa ina sonki ne badan ki soni ba,
so karki damu zanyi maneji,
ko ba komai in na dawo gidana nasan da abin da nake so zan fara tozali, gyara tsayuwa yayi yace "baki san ke din sarauniyata bace, in kina gurina a killace to bani da wata damuwa,
dan haka bana san jin komai je ki gida ni zan tafi,
ko kina son wani abu?
Wani kukan take kokarin sake yi yace "mutum dai yasan hukuncin mai saba alkawari! Nidai ba ruwana, kamun Allah bana mutum bane,
share hawayen tayi da sauri ta ruga gida..
Kwantar da kanshi yayi akan sitiyarin motar zuciyarshi na azalzala da kalamanta,
ya zaiyi in da gaske ya rasa Suwaiba,
da wace mace zai iya rayuwa in ba ita ba,
sake kallon kofar gidan yayi sannan ya tada motarshi ya wuce gida jikinshi duk a sanyaye....
Abu kamar wasa karamar magana ta zama babba,
Suwaiba ta daina fita gurin Mukhtar,
ko yazo saidai ya karaci tsayuwarshi saboda rashin baffa a gari,
Ana jibi daurin aure ne ta fito ta sameshi,
a wannan ranar saida ya nuna mata irin nashi bacin ran kafin ya tafi ranshi a bace,
yana mata uzurin yarinta da kuma bata san meye kalmar so ba,
gidan su Abbakar ya wuce direct,
cikin bacin rai yake magana yana fada mishi yadda al'amura suka sauya cikin kankanin lokacin,
"Abbakar kai kadai zaka mata magana,
wallhi ina shiga cikin matsanancin hali in naji tace "bazata aureni ba,
yarintar ta bata gaya mata gaskiya, in ba haka ba sai ka kalli mutun kace baka kaunarshi,
Shiryawa Abbakar yayi suka wuce gidan su suwaiba,
dakyar ta sake fitowa, har saida ma'u tace ta fita,
ita duk tunaninta asirinta ne ya kama Suwaiba,
bata san kauna ce ta sanyata hakura dashi ba,
tasani tunda sukayi alwashi zasu iya rabasu kuma ta zauna a gidan su gasa mata aya a hannu,
gara ta hakura dashi ya auri yar uwarta ko zasu samu maslaha da ita,
dan a yan kwanakin nan ta jigata da rashin kulawar da Zainab take bata..
"Abokina yayi laifi ko?
Rufe fuskarta tayi murya na rawa tace "A'a,
to meya faru?,
fada min a matsayina na uncle dinki,
kuka ta fara yi kamar yarinya karama tace "nidai kawai bana sanshi ne, kuma yaki ya taimakeni yace ma Baffa bazai aureni ba,
runtse ido Mukhtar yayi kirjinshi kamar zai fado kasa,
matsowa kusa da ita yayi kamar zaiyi kuka yace "nasan bakya sona,
kiyi hakuri ki bani amanar rayuwarki,
nayi alkawarin koya miki sona,
wani abu taji tun daga kanta har tafin kafarta,
"meyasa Ya Allah,
meyasa na samu gatan da zaisa in zama lele kuma yanzu gatan zai subuce min,
meyasa,
wannan shi ake kira da Dandani haukaci,
a fili kuma kukan dai ta cigaba dayi tace "ni bazan iya jure zama dakai bane,
uncle Abu dan Allah kace yayi hakuri ya nemi wata,
"bazanyi hakurin ba,
Abbakar yarinyar nan bata da hankali,
rabu da ita kazo mu tafi,
in an daura auren ta mutu,
kafadunshi Abbakar ya dafa yace "calm down kyari,
hannun ya ture kafadun shi yace "dan taga ina lallaba ta ne, wallahi abinda zai hanani aurenki saidai mutuwa,
ko kuma dama bani da rabon zama dake har mu samu 'ya'ya, amma in har inada jini a jikinki sai kin aureni (Rabon yayi muku wannan farraqun),
yana kaiwa nan ya fita yana huci kamar zaki,
Duk irin lallashin da uncle Abu yayi mata ta kafe akan ita bata sanshi,
har yaji haushi sukayi sallama,
kafin yakai kofar fita yaji ta rushe da kuka mai ratsa zuciya, tsayawa yayi yana kallonta a ranshi yace tabbas akwai matsala, haka nan bazata ce bata son kyari ba,
koma menene Allah ya kawo mata mafita....
*RANAR AURE*
Tun da suka idar da asuba Suwaiba ta wuce islamiyyarsu ta zauna can wani lungu da babu mai zuwa gurin,
kuka takeyi sosai hade da karatun qurani,
tasan in har ba'a ganta ba to tabbas baza'a daura mata auren ba...
Zufa Baffa ke sharewa yana fadin "ina tace miki zata,
kukan munafurci Ma'u ta kirkiro tace "bata fada min ba,
nidai naji Leemah na cewa Suwaiba tace "in aka mata aure saita kashe kanta,
salati Baffa ya saki yana fadin yarinyar nan so takeyi ta kunyata ni,
duk irin mutanen da muka tara a kofar gidannan so takeyi lallai sai na kunyata,
Matsowa kusa dashi ma'u tayi tace "tunda tace bata sanshi a hakura mana,
Wani kallo baffa yayi mata yace "so kikeyi in zama karamin mutum,
kinsan adadin manyan masu kudin dake zaune a kofar gidannan suna jiran a daura auren nan,
kawai kuma sai inje ince musu amarya ta gudu,
Sake matsowa tayi tace "to ya zakayi, saidai ko dan mu fita kunya a hada auren da Zainabu,
kaga shikenan asirinka a rufe,
ita kuma tunda rayuwar da ta zabarwa kanta kenan shikenan sai taje can tayi,
dan taga tana da farin jinin ne,
in kayi tafiya itace wannan saurayi itace wancan,
cike da bacin rai Baffa ya hau kan zancen Ma'u ya zauna,
ya fita yanata sababi cikin zuciyarshi..
bai nemi shawarar mukhtar ba dan baisan samm ya rasa shi a matsayin siriki saboda tarin hidimar da yakeyi mishi,
gurin daurin auren yaje ya zauna aka fara gudanar da auren kamar yadda addini ya tanada,
saida aka daura aure akayi komai sannan maroki ya fara fadin, "Tuwon girma miyarsa nama,
yau naga auren da ban taba ganin irinsa ba,
jama'a ku shaida an daura auren *ZAINAB* DA *MUNTARI* akan sadaki naira na gugan naira har naira Dubu Uku....
Ba Mukhtar bane kadai ya girgiza, hatta Mahaifinshi saida ya tafi tunanin Zainab ko Suwaiba......
Mrs Tijjani Shattima.....
[07/03 2:02 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣0⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Alhaji ku yafe ni!,
na yanke hukunci ba tare da neman yardarku ba,
dan Allah ku gafarce ni,
nayi hakan ne dan in fitar damu daga kunyar jama'ar da muka gayyata,
Baffa ne ke jero musu bayanan ban baki lokacin da suka kebe da Alhaji Garba yayi mishi tambayar dalilin sauya akalar daurin auren,
share hawaye yayi ya cigaba da cewa, "yarinyar nan taso ta wulakanta ni, sai Allah yasa ina da 'ya'ya matan da basuyi aure ba,
kuma bana son mutum kamili kamar Muntari ya subuce min,
da zainab da Suwaiba duk daya ne, uwa daya uba daya suke, dan haka kaga wanda yazo daukar suwaiba kuma ya samu zainab ai duk daya ne tunda tsatso daya suka fito,
kasa Magana Mukhtar da zuciyarshi ta kai kololuwa gurin bacin rai yayi,
har lokacin baiji ko daya daga kwatan son da yake ma Suwaiba ya fita a ranshi ba,
da yaji Babanshi na kokarin amincewa da batun yayi saurin cewa "Abba, dan Allah kuyi hakuri,
ni suwaiba kadai nakeso,
in aka daura mana aure da ita nasan zata hakura ta zauna dani!
"Naso yin hakan,amma abin yaci tura saboda guduwa tayi tabar gidan, Baffa ya karashe cike da damuwa,
wani abu Muntarin yaji ya soki kahon zuciyarshi,
har kiyayyar ta kai haka,
ta ina ya gaza da ya samu macen da ta nuna mishi irin wannan kiyayyar,
me ya rasa,
babu abinda bai mallaka ba na daga dangin kyau, ilimi, gayu, uwa uba arziki na jama'a da kuma na dukiya,
me yasa Suwaiba zata rusa tanadin da yayi wa rayuwarsu, yanzu kenan dukkan mafarkinshi zai zamto cikakken mafarki, kenan babu ko daya a cikin mafarkinshi da zai zamto gaskiya,
baisan Hawaye ya fito a cikin idanuwanshi ba saida yaji duminsu a kuncinshi,
mikewa yayi ya fita zauren hade da share hawayen fuskarshi,
motar da suka zo shi da abokanshi ya shiga hade rufe fuskarsa dan hawayen sunki daina zuba,
Allah ya sani ba karamin so yake yi ma Suwaiba ba....
Godiya sosai Baffa yayi wa Baban muntari saboda fahimtarshi da yayi,da Kuma alkawarin da yayi mishi na yarshi bazata wulakanta a cikin zuri'arshi ba,
ko yana so ko baya so dole ya karbeta hannu bibbiyu a matsayin matarshi,
dan zuri'armu kaff babu me wulakanta mace...
Sai dare suwaiba ta dawo gida lokacin Ma'u na buduri da makota ana shirin kai Zainab dakin miji,
kallo ne ya dawo kanta,
daga mai yi mata habaici,
sai mai yi mata kallon marar hankali,
dakin Baffa ta shige a darare, zaune ta sameshi yayi tagumi yana tunanin ta inda zai fara neman suwaiba,
jin muryarta ne ya sanyashi waigowa da sauri,
sanyi yaji a zuciyarshi da ya ganta lafiya kalau,
a fili kuwa fada ya rufeta dashi, saida yayi mata cin mutunci sannan a karshe yace "Wallahi, wallahi, kinga rantsuwar nan, bata da kaffara, bazaki kara daga kafarki kije makaranta ba,
kina cikin gidannan har sai na samu wanda zan bawa ke sadaka, ke ba takamarki kinada farin jinin samari ba,
kin daukesu kamar rigar canji,
to ki sani kin jawa kanki a gurina,
fita ko nan da kofar gida ne ban yarda kiyi ta ba,
sai ki zauna a gidan tunda kin zabi butulcewa Allah da ni'imar da yayi miki,
tashi ki fita ki bani guri mutuniyar banza mutuniyar hofi,
tashi tayi ta fita da gudu tana rusa kuka,
a kofar dakin tayi karo da masu kai Amarya ana wakar "Ayye mama",
ta gefensu tabi ta shige dakinsu ta kara bude wani sabon babin kukan.... (oyoyo talauci inji Meela)
Rayuwar auren Zainab da Muntari kadaran kadaham,
sam baya wulakanta ta saboda ya karanci hakkin mace akan miji, kuma mahaifinshi ya sake tunasar dashi,
Da fari ta dan samu matsala da mahaifiyarshi domin sam bata san zainab,
gani takeyi an lika mishi ita ne dan a cuceshi,
saida "Abba" yayi mata nasihar cewa matar mutum kabarinsa, kuma wata bata auren mijin wata,
sannan ne ta dan sakko,
amma duk da haka bata cika bata muhimmanci ba,
biyayyar da zainab ke mishi ne ya sanya shi sake sakewa da ita,
wani lokaci yakan tuna suwaiba wani shashin zuciyarshi yaji yayi mugun tsanarta,
wani shashin kuma yaji ta ciki a killece,
ya sha in zai ambaci sunan zainab yace suwaiba,
in ko yayi tafiya to fa sai ya cirewa suwaiba tsaraba,
kome zaiyi da ita yake hadawa yayi,
wannan abu shi ya kara dungunzuma zuciyar Zainab taji gaba daya Suwaiba ta fice a ranta,
kullum cikin kulli Goggo take dan dai kawai kar auren yarta ya mutu,
a irin zaman da sukeyi Zainab ta samu ciki har ta haihu, haihuwarta ita ta kara daraja ta a idon iyayenshi da shi kanshi,
sannu sannu ya fara fitar da Suwaiba a cikin ranshi, saboda samun zuri'a da ya farayi.
Saida Zainab ta jera mishi 'ya'ya Mata uku a karancin tsakani (gwarne ) cikin shekara hudun aurensu,
Reemah ce Babba,
sai Radiya
Sai Raudha,
a lokacin da take da cikin na hudu ne Muntari ya saduda ya mika mata ragamar rayuwarshi,
domin yasan yanzu indai za'a kirashi to itace ta biyun da za'a kira a rayuwarshi....
Ita kuwa suwaiba baiwar Allah ta zama baiwa ta gidi,
komai na gidan ita takeyi,
babu makarantar islamiyya, babu fita cikin gari,
iyakarta shagon buzu Adamu mai gadin jikin gidansu,
duk irin kyawun da ta ke dashi ya disashe,
rayuwar dai yinta kawai takeyi saboda Allah a hakan yaso ya ganta,
kullum saidai tayita yi mishi Godiya da bai daura mata ciwo ba....
Leemah kuwa ta zama yar gayu sosai,
university take zuwa Abu zaria,
babu abinda zatace tana dauka a makaranta,
ita dai kawai ta shiga gayu,
yau ta tsaya da wannan gobe wancen,
Baffa daga yayi niyyar yi mata magana Ma'u zata hanashi,
takan ce in ba'a barta taje makaranta ba ina zata samu mijin aure,
dole badan yaso ba ya barta tayi abin da taga dama..
"Bani omo malam Ado, !
dauko mata kullin bulan omo biyar yayi yace "jeki kiyi amfani dashi, na bar miki kudin ki siya silifas naga naki ya tsinke,
murmushi tayi tace "nagode Adamu,
"ba komai suwaiba kedai ki daina yawo ba takalmi,
gyada mishi kai tayi ta wuce cikin gida,
kallo ya bita dashi hade da girgiza kai cike da tausayawa,
duk wannan abun da sukayi a idon Baffa wanda yazo shiga da mota gida,
wani abu ya darsu a ranshi ya shiga gida yayi parking...
"Kanason 'yata Suwaiba?
Daburcewa Adamu yayi da yaji tambayar yace "a'a Alhaji,
ai tafi karfina,
in ba cutarwa ba ta yaya zan auri mace cikin gata alhali ni din ba kowa bane,
dariya Baffa yayi yace "in dai kanajin zaka iya zama da ita to zan aura maka ita,
washe baki Adamu yayi yace "suwaiba mace ce mai kawaici da hakuri Alhaji,
waye zai kita a matsayin mata, bana tunanin akwaishi,
murmushin farin ciki Baffa yayi yace "kaje ka shirya,
rana ita yau zan daura muku aure,
godiya sosai Adamu ya tsuguna yayi ma Baffa sannan ya wuce cikin gidan da yake gadi dan sanar dasu....
Koda ya fada ma Suwaiba nan take ta amince saboda a ganinta gara taje tayi bauta mai dalili, domin ta gaji da aikin jakin da takeyi....
Ranar da aka daura auren duk wani masoyin Suwaiba saida yayi mata bakin cikin karewa da kaskantaccen mutum irin Adamu mai gadi,
shi kuwa Muntari gani yakeyi Hakkinshi ne ke bibiyarta shiyasa ta dade batayi auren ba a karshe ta auri mai gadi...
Rayuwa mai cike da jin dadi da rufin asiri daidai gwargwado sukeyi,
gidan da ya dade yana tari ya siya mai dauke da daki biyu da kitchen nan aka kaita,
sosai take jin dadin zama dashi dan dama sun saba,
shekararsu biyar da aure ta samu cikin Hafeez bayan