Showing 39001 words to 42000 words out of 184071 words

Chapter 14 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt

tana kunkuni dan kar Ma'u taji,
tana gama wanke mata jiki ta goyata ta shiga daki ta samu Ma'u na kankarewa Boddo kai tana bacci,

Haba Goggo (sunan da yaran makota ke kiranta dashi) yanzu kina ganin yarinyar nan tafi awa zaune a kan pou baki wanke mata ba,
wallahi kiji tsoron Allah,
kullum a islamiyya ana fada mana muhimmancin rikon maraya,
nawa Suwaiba take da ta cancanci wannan azabar,
bakya t---- katseta tayi ta hanyar bige bakinta,
sai kizo ki dukeni,
nace kizo ki dukeni uwata,
sauke ta a bayanki dan ubanki,
fita Bingel tayi ta dauki hijab dinta ta koma islamiyya da suwaiba a bayanta tana share hawaye,
ta rasa irin wannan tsanar da take nunawa Suwaiba in suna kebe su hudu,
amma a gaban mutane da Baffansu bata da yar lele kamar suwaiba..

A kullum nunawa Baffa takeyi ita fa Suwaiba ta fiye mata ya'yanta, kuma koda wasa bata san kowa yasan ba ita ta haifeta ba,
shiyasa Baffa ke tafiya neman kudinshi a duk fadin nigeria hankali kwance,
ko ya dawo gidan baya samun damar daukarta saboda yadda Goggo ke makale ta a bayanta, saidai daddare in suna kwance ya shafa mata kanta yayi yar kwallar tausayin maraicinta da tunanin uwarta....


●●●●●●●●

Shekaru masu yawa sun shude cikin dadi ga masu sa'ar samun dadin,
sannan cikin radadin azaba ga marasa galihun rayuwa,
cikin wadannan shekarun Baffa ya samu cigaba sosai a rayuwarshi,
dan sana'arshi ta maidashi Kaduna inda yake tsara atamfofi a kamfanin yar masaka,
a lokacin yakan kasance da iyalinshi duk dare,
a nan ne ya dan fara dan fahimtar zaman da Ma'u ke yi da suwaiba,
a ko yaushe in ya fara wannan tunanin sai ya kauda shi saboda baisan sanya wasi wasi a zamanshi da Ma'u,
in ya ga suwaiba tayi shuru sai yayita kallonta ya rasa bakin da zai tambayeta,
wani lokaci in Ma'u ta lura da hakan sai ta sameshi ta fashe mishi da kuka tace "yarinyar nan bansan meyasa take yawon zama shuru ba, ni kaina inason a koda yaushe ta sake kamar yadda Halima take yi,
na rasa me ke damunta,
Baffa yakan yi murmushi yace "yanayinta kenan, haka Allah yayi ta shuru shuru,
mu bamu isa mu canzata ba...






*HADUWAR ALKHAIRI*


_Muna Haduwa da mutane ta hanyoyi daban daban, to kenan ta yaya muke haduwa da waďanda zamu gudanar da rayuwarmu tare dasu ma'ana *MASOYA*_



"Leemah Muhammad",
meye position dinki?,
harararsu tayi tace "meye naku a ciki, kowa yaji da kanshi,
dariya suka kece mata dashi hade da cewa bench warmer, daga ke babu wani,
Suwaiba dake tahowa da Akwatinsu na gwangwaro tace "Haba Amina Sa'ad, babu kyau fa, ilimi Allah ne ke bada shi kuma yayi hani da gori akanshi,
basu fasa dariyar ba suka ce barmu mu ci ma yar rainin wayan nan mutunci,
ita a ganinta tafi kowa,
sai anzo jarabawa ido ya raina fata ta fito da ziro me katon kanta,

Wasu gungun mata dake bayansu a karkashin bishiya suma suka kece da dariya hade da cewa su Leemah gayu ba brain,
sai ki dawo first term da juniors dinki, muko ay sai candy,
kukan takaici ta fashe dashi ta ruga bakin gate din makarantar, bin bayanta Suwaiba tayi da kayan niki niki masu masifar nauyi,
hakuri ta fara bata tace "karki damu, kisa ma ranki zaki iya next term din,
dan an miki repeating ba yana nufin bazaki iya bane,
zan tayaki addu--- katseta tayi cikin kuka tace "rike nasihar ki da adduar ki,
ba na ja miki kunne akan babu ruwanki dani ba?, wai ma ban hanaki jerawa tare dani ba,
ni sa'arki ce da zaki dinga jerawa dani har kiji abinda ake cewa a kaina,
wallahi bari muje gida,
sai na miki dukan tsiya,
yar iska matsiyaciya kawai,
Ajiye kayan suwaiba tayi tace "kiyi hakuri dan Allah, wallahi bazan kara ba, kinga in zaki min hukunci kiyi min anan, amma dan Allah karki bari Goggo taji,
tsaki taja mata tayi gaba a zuciyarta tace "wallahi bazan sake dawowa makarantar nan ba, tunda karatun ba dole bane...



Abokina!!
irin wannan kallo haka, ai sai kasa ta fadi, ji yadda ka kafeta da ido,
in dai wadancan biyun ne, to sun saba,
kullum leemah cikin masifa take ita kuma suwaiba tayi ta tausarta,
i think immediate ne,
dan uwa daya uba daya suke, dalili kenan da yasa na daina sa musu baki,
karka shiga fadan yan uwa,
and kasan me ke yawan sasu fada,
ita waccen,, ya nuna suwaiba, tana da masifar kokari, ita kuma dayar in kana neman dakiki ajin farko in ka sameta to ka rufe kofa,
ja motar muje na dauko takardun,
tada motar yayi har lokacin idonshi nakan Suwaiba,
yana isowa saitin da take ya kashe motar ya fito,
kallonshi abokin wanda ya kasance malamin makarantar yayi yace "Lafiya ina zaka,
bai saurare shi ba ya zagaya gurin Suwaiba dake tsaye a gurin kamar an kafeta,
tana tunanin irin hukuncin da zasu yanke mata a gida,
addua takeyi a zuciyarta na Allah yasa yayarta na gidan, ita kadaice zata iya taimkonta daga ukubar da zasu mata,

kamar daga sama ta jiyo sallamarshi,
kallonshi tayi ta kauda kai tace "Ameen wa alaikum salam, ina yini,
wani sanyi ne yaji ya ratsashi na jin daddadar muryarta,
Amsawa yayi yace "lafiya kalau malama Suwaiba,
dago kai tayi cike da mamaki tace "laaa sunana,
a ina ka san sunana?, daga kanshi sama yayi yace "wahayi akayi min da sunan,
kuma aka ce inzo nan in sameki, rike baki tayi ta daga kai sama tace "a can sararin samaniya?
Gyada kai yayi yana murmushi yace "kwarai kuwa, ko kina tantama ne,
cike da nutsuwa tace "kwarai ba tantama nakeyi ba,
yarda ce banyi ba saboda na karanta a littafi,
manzanni kadai ake wa wahayi, kuma nasan a cikin duniyar nan da azzalumai sukayi yawa babu tabbacin samun wani annabi,
kuma ai annabin Allah shine karshen annabawa,
dan Allah in ma gatse kakeyi to ka daina domin ina tsoron wani ya samu zunubi ko yayi shirka domin ni,
"Ya ilahi ya fadi a zuciyarshi ya kalli Abokinshi dake cikin mota yace "kaji Kalamai daga bakin fasihiyya ko Abbakar,
kallon motar tayi tace "laa uncle Abu ina wuni,
fitowa yayi a motar yana dariya yace "lafiya kalau Suwaiba,
anyi hutu ana jin dadi za'a koma gida ko,
murmushi kawai tayi a zuciyarta tace wani hutu, ita da za'a barta ta kare rayuwarta a makaranta ai da taji dadi,
katse mata tunani Abbakar yayi yace "wannan abokina ne, sunanshi *MUKHTAR KYARI* ganin irin masifar da yar uwarki take miki ne yasa shi tsayawa ya baki shawarar ki dage ki dinga ramawa,
kyawawan mata da tsiwa aka sansu, ke kuma hakurin naki yayi yawa,
kallonshi Mukhtar yayi yace "to sannu koma mota,
nagode da ka tayani fada,
dariya sosai Abbakar yayi ya wuce cikin mota yana fadin 5mins na baka,
kasan we have alot to dzoo,
a gaugauce ya tambayeta ko zai iya sauke su a gida daga nan sai yaga gidan nasu,
kallon Leemah tayi da ta waigo tana hararar su tace "bari in tambayi yar uwata,
ajiye akwatin tayi a kasa yayi saurin daukarsu ya zuba a boot, ya shiga motar yace "abokina kai zaka musu magana su shiga dan dakyar waccan masifaffiyar ta yarda su bimu,
magana daya Uncle Abu yayi musu suka shiga motar,
a kofar gidansu yayi parking,
da sauri Leemah ta bude motar ta shige gida gudu,
jiki na rawa Suwaiba ta bude motar tace "ina akwatinan mu? Bude boot din yayi ya fito da akwatinan yace "muje in rakaki, nauyinsu yayi yawa,
a'a tayi saurin cewa, hade da mika hannu,
Dan Allah ka rufa min asiri, fada za'a min a gida,
"let her go kyari,
bakasan condition din da take ciki ba,
sakin akwatinan yayi tayi saurin dauka ta ruga cikin gidan da gudu,
bin ta yayi da ido har ta kure cikin gidan sannan ya shiga motar ya tada suka wuce....




Mrs Tijjani Shattima.....
[04/03 12:44 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣8⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*





Tun daga zauren gidan take jiyo masifar Ma'u hade da kukan Leemah,
sharri kala kala tayi mata sannan tace "ta hadu da saurayi tanata shige mishi har ta rokeshi ya kawo su gida,

innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai suwaiba ke furtawa a cikin ranta,
da sallama ta shigo gidan ta ajiye akwatinnan ta tsuguna har kasa ta gaida Ma'u,
matsowa kusa da ita tayi ta daga hannu ta kwada mata mari,

Halima sa'arki ce da zaku hadu da kawayenki kuyi ta cin mutuncinta,
ke dan uwarki ke kika bawa kanki kokarin,
au dan na yarda kun shiga makaranta daya,
shine zaki nuna zakewa ki nuna kinfi ta iya komai,
bulala Leemah ta miko ma Goggo tace "ga yaren da tafi ganewa nan Goggo,
karbar bulalar tayi ta fara zuba mata tana cewa uban waye ya saukeku a kofar gida,
yanzu dan rashin kunya kina ganin yayunki basuyi aure ba ke har kina da tsaurin idon tsayawa da saurayi,
to wallhi in na kara ji da ganin kin tsaya da saurayi tun yanzu sai na miki illah,
banason rashin ido a gurin y'a mace wallahi,
bulalar da zata kai mata na karshe ne ya sauka a jikin yaya zainab (Bingel) da ta shigo gidan a lokacin,
dago suwaiba tayi tana share mata hawaye itama hawayen take tace "haba Goggo, kowa ba rabonshi yake samu ba,
yanzu wannan abun da kikeyi shine Allah zaisa mu samu miji ko me,
ki duba kiga yadda na girma na rika a gida babu mashinshini, haka Halima babu wanda ya taba furta mata kalmar so duk ko da irin kyan da muke dashi,
a cikin mu Allah ya sanya suwaiba nada farin jinin da duk ta fita sai ta samu mai cewa yana sonta, ai sai mu godewa Allah,

wani kukan ne ya kufce mata na tuno saurayin da tayi arangama dashi a bikin Nafisa jiya mai cike da barkwanci da halin kirki,
a zuciyarta tana takaicin yadda yayi mata nisa ta ko wani irin bangare saboda matsayin shi,
daki taja suwaiba suka shige ta bar Goggo nata banbamin bala'inta,
itama tana takaicin bakin jinin da yaranta suke dashi,
babu irin maganin da batayi musu ba dan su samu mashin shini amma a banza,
to ita kuwa ta yaya zata yarda ta bar suwaiba ta kula samari alhali yaranta duk ba mashin shini, masifar ta cigaba dayi kamar zautacciya zuciyarta na mata zafin balbalin wuta.....





Albishirinki Ma'u!!!
Kai yau cikin farin ciki nake wallahi,
Goro ta fadi tana zuba mishi ruwa a kofi,
baibi takan ruwan ba ya kwala kiran suwaiba,
da sauri ta fito yace "akwai bako a waje kira Yayarki kuje ta rakaki, kuma kar ku dade,

cike da faduwar gaba Ma'u tace "baka ce min komai ba kuma kace yara su fita,
yanzu sai aga yara sun fita zance kai ba abin kunyar ka bane,
"shiyasa nace Zainabu ta raka ta ai, saboda idon mutane,
zuciyar ma'u kamar zata fito tace "to meye albishir din,
gyara zama yayi yace "kinajin labarin Alhaji Garba Kyari mai fata ko?, gyada kai Ma'u tayi kirjinta na tsananta bugawa,
yace "to danshi ne yaga suwaiba yake so,
kuma da aure, nace yaje ya turo magabatanshi mu tsayar da maganar aure,
wallahi Ma'u bakiji dadin da nakeji ba,
ko ba komai zan fara aurar wa, mutanen unguwa zasu bar zundena,
yake ma'u ta shiga yi tana fadin madallah Allah ya sanya alheri, Ameen.. Baffa yace ya mike ya wuce daki zuciyarshi wasai bai ko lura da yanayin ma'u ba,
shidai a yadda yakeji a ranshi, yasan suwaiba ta gama samun gatan duniya saidai kuma ta roki lahira....



Tun da suka fito Bingel tayi tozali da Mukhtar cikin kayanshi riga da wando fela,
gashin nan Afro ya tajeshi ya mike sosai, hankalinta yayi kololuwar tashi,
shine,
shine wanda ta ganshi a gidan Nafisa,
karasowa yayi gurin kafin su iso yace "barka da fitowa sahibar ruhina,

ya ilahi, suwaiba kamar zata nutse ta damki hannun yayarta hade da rufe fuskarta cikin hijab,

no, no, no,
wannan kunyar cutar dani zatayi,
kiyi hakuri ki dago kanki ki kalleni,
sakin hannun Bingel tayi ta ruga cikin gida da gudu ta barsu a waje da Bingel da tayi tsaye tana kallonshi kamar mutum mutumi,
Hannu yasa yayi kasss a fuskarta yace "ina wuni yar uwarmu,
firgigit tayi tace "ni ya kamata in fara gaisar dakai,
murmushi yayi yace "kuma sai kika barta ta gudu baki rike ta ba,
dariya tayi tace "kasan yarinya ce, kunya gareta,
amma bari in tayata tadin,
cikin nutsuwa ta dinga tambayarshi halayarshi da abubuwan daya kamata ta sani,
sun dade suna hira yana fada mata yadda yake ji a cikin rashi game da kanwarta,
da zai tafi ya bukaci ta kira mishi ita su yi sallama,
sallama tayi mishi ta wuce gida ta iske suwaiba a zaure tace "jeki kiyi sallama dashi, ko so kikeyi yayi fushi,
dakyar ta fito ta tsaya nesa dashi tace "ina wuni,
jingina yayi jikin stalet dinshi yace "bazan amsa ba,
ashe ma dai ni dodo ne ban sani ba,
rufe fuskarta ta sakeyi tace a'a kayi hakuri,
murmushi yayi yace to nayi, ya bude gaban motar ya dauko leda yace "gashi inji mamanki tace wai a kawo wa yarta,
dakyar ta karbi ledar ta ruga cikin gida da gudu,
murmushin shaukin samun farar mace kamila yayi sannan ya shiga mota ya tada ya wuce....



Bayan zuwan magabatan Mukhtar aka saka ranar aure sati biyu,
babu irin hidimar da baya ma Baffa saboda so da kaunar da yake yi ma suwaiba,
ita kuwa Bingel ramewa ta soma yi saboda tunanin mukhtar da ta sanya kanta ciki,
bangaren Ma'u kuma sai hada tuggunta takeyi wanda zai hana auren,
gori kuwa babu wanda bata sha daga makota,
da abun ya isheta ta zauna wani dare ta dinga rusar kuka, Halima da itama kishin suwaiba ya dameta ta zauna tana tayata kukan,
a haka suwaiba da ta dawo gurin mukhtar ta samesu,
kudin da ya bata ta fito dashi ta mikawa Ma'u tace "Goggo gashi yace in kawo miki kudin walima,
amsa tayi ta ajiye a gefe,
cike da fargaba tace "Goggo me ya sameki,
rungumar munafurci Ma'u tayi mata tace "Suwaiba ya zanyi da raina,
ya zanyi da gorin mutane,
yanzu kina karamar kanwar yayarki ace kinyi aure ita bata yi ba,
kinsan dole abun ya dameni,
dole ne in shiga cikin kunci da takaici saboda nasan babu wanda zai aureta yanzu, matso da ita ta kuma yi tace
"kinsan dai ni na haifeku dukkanku ko? Gyada kai Suwaiba tayi tace "eh, to yar albarka ina umurtarki da ki janye auren nan akanki ki barwa yayarki,
nasan Allah zai dubi abin alherin da kikayi ya baki wanda ya fishi,

jiki na rawa suwaiba tace "Goggo, dan Allah kiyi hakuri,
wallahi ina sonshi,
kuma shim--- ya isheni,
yanzu duk halaccin da Bingel tayi miki tun kina yarinya har kawo yanzu baki gani ba,
duk irin kaunar da ta nuna miki bazaki dubashi ki sadaukar mata da mijin da zaki aura ba,
kuka ne ya kufcewa suwaiba tace "hakkinta ne Goggo,
Hakkinta ne a matsayinta na yayata ta kula dani kuma ta sadaukar da komai nata a gareni,
wallahi da zan iya da na rabu dashi na bar mata shi amma bazan iya---- wani wawan mari Ma'u ta kai mata,
tace "lallai rashin kunyarki ta tumbatsa,
a gabana kike cewa kina son namiji,
lallai ďan da baka haifa ba dole ya nuna shi ba naka bane,

dammmmm....

suwaiba taji a kirjinta,
kalaman Goggo suka sa zuciyarta ta fara yawo a cikin ma'ajiyinta........




Mrs Tijjani Shattima
[05/03 11:10 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* 2⃣9⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*




*_Duniya kurkukun mu'imuni, kuma Aljannar kafiri, akwai mutanen da Allah swt yake Halittarsu a cikin duniyar nan ba domin suji dadi ba, sai dai domin rayuwakansu su zamto izina ga wadanda sukazo domin zamanta na din din, mai hankali shi kadai yasan duniya ba gurin jin dadi bane, lahira itace matabbata, sannan akwai tarin tanadi da Allah yayi wa bayinshi masu hakuri, tanadin Allah shine tanadi Allah ya sa mu dace,_*


*RABUWA DA MASOYI*


Mikewa tayi ta isa gabanta tace "Goggo, dan Allah karki ce bake kika haifeni ba,

Kukan Munafurci Ma'u ta saki tace "Suwaiba yau kin sani na fada miki abinda ban taba tunanin fadin shi ba,
yau kin kaini makura har na fito miki da *SIRRIN BOYE*
kuka ne ya kufce ma Suwaiba tace "wacece mahaifiyata?
, a ina take?,
nan take shaukin son taga mahaifiyarta yazo cikin zuciyarta,
rungemeta Ma'u tayi sosai tace "Tambayar bata da amfani tunda bata raye,
ni nan ni na raine ki tun kina jarinta da taimakon yayarki,
munsha gwargwarmayar rayuwa gurin baki tarbiyya,
musamman yayar taki da kike yunkurin k'in sadaukar mata da soyayyarki,

cikin kuka suwaiba tace "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, kara kankameta Ma'u tayi tace "duk abin da kika ga na miki a baya bawai dan bana sanki bane, nayi shi ne dan samar miki tarbiyya mai kyau da amfani,
kiyi hakuri,
kiyi hakuri ki bar mata,
"labarin karya ta shirya mata akan mahaifiyarta sannan ta karashe da fadin irin kular da zainab din tayi mata,
kukan bai fasa zubowa a idonta ba tace "Allah ya jikan mahaifiyata Goggo, Ameen Ma'u ta fadi sannan tace "nasan zaki bar ma yar uwarki mijin da zaki aura ko? Nasan zuciyar zinari gareki,
girgiza kai Suwaiba tayi tace a'a Goggo,
yaudara ce wannan,
bazan iya hakuri da shi ba,
domin kuwa Allah sai ya tambayeni,
yasa rai da aurena kuma kawai sai in ce mishi ya auri yayata,
hakan bazai yiwu ba,
tana karashe fadi hade da tashi ta fita zuciyarta na tariyo mata irin ukubar da tasha a hannun Goggo,
ba tun yau take tunanin cewa ba Goggo bace ta haifeta,
gashi yau sanadiyyar Mukhtar an warware mata komai,
hawayen idonta ta share dan tasan in shaa Allahu ta kusa daina zubda su,
tasan Mukhtar zai zame mata komai da ta rasa a rayuwa..

Dakinsu ta shiga jiki a sanyaye,
a zaune ta tarar da zainab da ta gama sauraron duk abinda suke cewa,
tafarfasa zuciyarta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login