Showing 153001 words to 156000 words out of 184071 words

Chapter 52 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt

gama tallan drama's dinsu zasu sako cartoon,

hannu tasa a baki tana sha a boye dan kar Hilal ya kamata,
yadda ta naďe hannun da hula zaka rantse wani abun take sha daban,

Kamar cikin mafarki ta tsinkayi kukan yar budurwa cikin wani tallan arabic drama,
sanye take cikin jallabiya baka kanta yane da ďankwali,

Mikewa zainab tayi ta isa gaban tvn dan kalolin hotunan budurwar ake nunowa,
daga wanda take kuka sai wanda take dariya,

*Adda*

ta furta a hankali tana shafa fuskarta a screen....

" *Hey everyone i'm _MALEEKA SAHEEB SAIF_.... SAHEEBUL QALBEE will be in cinema's on the 3rd may in shaa Allah, don't miss the unconditional love story of NAINAH AND SAMIR, dos in Egypt will see ya on the 5th, nd Istanbul on the dday, love yhu oll my fans.. muahhhh..*




Ya Hilal...
Ya Hilal...

A ruďe ya rufe laptop dinshi ya buďe kofa saboda irin kiran da Zainab take mishi,
duk tunaninshi wani abun ne ya sameta,
haki ya ga tana yi tana nuna mishi tv,

"Adda na gani a cikin tv,
wallahi itace,

ajiyar zuciya Hilal yayi ya kwace naďin da tayi ma hannunta da hula yace

"wannan abun da kikayi shi ya sanya tayi miki gizo,
amma muje in ga ko itace,
bin bayanshi tayi suka zauna a parlon lokacin an wuce tallan har an fara cartoon,
a hankali tace
"an gama, amma ka zauna a sake yin talla zaka ganta,

janyota jikinshi yayi yace
"Bacci kikeji my baby,
kwanta kinji,
anjima in kin tashi sai mu fita yawo,

rufe idonta tayi tana hango fuskar Maleekah wacce tayi ma lakabi da Nadeeyah,
babu abinda ya banbanta su sai tsayi da wayewa,

Maleeka ta ďan dara Nadeeyah tsayi sannan wayewarsu da gogewarsu ma sam ba daya bace,
amma kamannin fuska babu inda suka banbanta,
da tunanin bacci yayi gaba da Zainab,

kwantar da ita yayi a gurin ya mike dan karasa research din da yakeyi akan aikin da gwamnati ke son bayarwa,
yana son Applying aikin amma yasan yafi karfin Papa ma bashi ba...


Cike da confidence yayi Applying haďe da ayyukan da yayi a baya,
tunanin yadda zaiyi ya haďu da mai
*A square TCC*
ya keyi,
yasan zaiyi aikin domin kuwa karuwarsa ce da shi baki daya,
dan in ya yarda sukayi aikin nan ba karamin kuďi zasu samu ba,

Wayarshi ya dauko da niyyar kiran manajan companyn,
tunawa da halinshi da yayi ya sanyashi ajiye wayar ya cigaba da tunanin yadda zaiyi ya hadu da CEO din cikin sauki,,
har ya mike zai  shiga bayi yaji karar waya,
da kamar kar ya dauka dan yaga bakuwar number,
wani sashi na zuciyarshi ya bashi umarnin dagawa yaji ko alheri ne,

Aiko Hilal yayi farin ciki matuka da jin mai kiran nashi dan abun da ya dade yana nema kenan,

nan yayi alwala yayi sallah haďe da yin addu'ar Allah ya bashi karfin gwiwar fada mishi abun da ke ranshi,
ya kuma sanya haduwar tasu ta zamto alkhairi.....





"Shiryawa yayi tsaff cikin kaftan riga da wando ash,
ya dade yana son haduwa da Ceo din companyn da yake wa zane  *SHEIK ATIKU SAHEEB SAIFUDDEEN*
Saboda wadannan  ayyukan zanen gwannati da yake son nuna mishi,
kuma yana son yi mishi gargadi akan macutan dake gudanar da ayyukansu a companyn shi...



Sanyin A.c. hade da kamshi mai dadi ke tashi a cikin office din,


Makeken Hoton jikin bangon idonshi ya sauka a kai gabanshi yayi mugun faduwa,

su hudu ne a jikin Hoton,

Irfan kadai ya gane saboda yayi mishi sanayya marar dadi,


Hoton yar budurwar da mahaifinta su suka fi tayar da hankalinshi,

bai gama shiga dimuwa ba sai da yaji muryar mutumin ya fito yana mishi MARHABAN ya Hilal,

suman tsaye yayi da suka hada ido saboda tsabar firgici,
tabbas yasan mama suwaiba bata da wani dan uwa namiji,

to wannan mutumin me irin fuskarta daga ina ya fito...


Hasbunallahu wa ni'imal wakeel ya fadi jiki na rawa,
a zatonshi gamo yayi da aljani.....


Karasowa kusa da Hilal yayi ya miko mishi hannu dan su gaisa,

kasa daurewa Hilal yayi yayi saurin tsugunawa dan yi mishi irin gaisuwarmu ta hausawa,
nan fa Sheik ya sake jin kaunar Hilal na yawo a cikin jininshi,

dagoshi yayi ya haďe jikinshi da nashi haďe da sumbutar kumatunshi irin dai yadda larabawa ke gaisuwarsu,
hoton dake kan makeken table dinshi kuwa saida ya kusa tsaida numfashin Hilal,

Hotone kato black nd white, fuskar nan bata da maraba da ta su Mama Suwaiba, Sheik, Nadeeyah da yar budurwar dake cikin hoto,
bai kara samun kanshi cikin ruďani ba sai da idonshi yayi tozali da sarkar wuyar tsohon hoton,
wannan karan Hilal ya riga ya gama fita hayyacinshi,
kar dai son da yakewa Nadeeyah ne ke neman kaishi wata duniyar daban,
hannun dattijon da yaji cikin nashi ne yasa shi saurin matsawa baya,
da karfi yake furta kalmar
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel,
cikin rashin fahimta dattijon ya nufoshi yace

"Lafiya?
Menene yake faruwa?

"Dan Allah karka cutar dani, Innalillahi,

"wa inna ilaihir rajiun sheik ya karasa cike da zullumi haďe da cewa "Subhanallah,

jin ya ambaci sunan Allah ne ya sanya Hilal nutsuwa haďe da nemo duk wata jarumtakarshi,
ganin ya samu nutsuwa ya sanyashi cewa
"su shiga cikin parlon office din,
bayanshi Hilal yabi yana ambaton sunan Allah...



Kallon Hilal Sheik yayi yana tambayarshi damuwarshi,

Murmushi kawai Hilal yayi yace

"Babu komai kawai yayi mishi kama da wasu relatives dinshi ne nd they are no more,

hoto ya kuma gani a kan centre table din cikin parlon an haďa pixmix da na Maleekah,
dauka Hilal yayi ya fito da wayarshi yayi scrolling hoton Nadeeyah ya nuna ma sheik,

second goma yayi yana kallon fuskar Nadeeyah,
tabbas wannan tayi kama da yayarshi wacce ya rasa tun da kananun shekaru,
katse mishi tunani Hilal yayi dan a lokacin tsoro ya fita a ranshi, yana da tabbacin wannan dan uwan Mama suwaiba ne bangaren uwa,

"Wannan sarkar ya nuna sarkar wuyar tsohon hoton,
da sauri Sheik yace "Ehem kasan sarkar ne,
gyaďa kai Hilal yayi yace
"Sosai, tana gurin grandfather dina,
gaba ďaya sun manta zaman da suka zo yi,
ko wannensu ya shiga shaukin son jin labarin juna,

"A ina ya samu sarkar,

yadda muryarshi ke rawa ya sanya Hilal dafashi,

"calm down sir,
farin cikin da nake ciki bazai barni in baka amsa ba,
sunanta kaďai zanji ya sanya ni fita gurin nan cikin gaggawa dan bayyanawa yan uwana abun farin cikin da ke tunkaro mu,

a gaggauce Sheik yace
*At---*

*ATIKA*

Hilal ya karashe cike da kaguwa domin ya kasa jiranshi ya karasa,

"Yesss,
she is my sister Atika,
my only sister,
my everything ya karashe cikin matsanancin kuka haďe da rungumar hotonta wanda ya zame mishi kullum...


"Ya Allah...
Hilal ya faďi yana zubar hawaye,

Nadeeyah were are uuu,
Asalinki ya fara bayyana,
ya ilahi,
tsatso mai kyau,
i knew it,
nan gaba abubuwan shahara zasu bayyana gareku,
Ina kika shige Nadeeyah,

kuka sosai sukeyi,
shi Sheik yana yi ne dan duk a tunaninshi zai sake sanya yar uwarshi a ido,

shi kuma Hilal kukan biyu ya haďe mishi,
na farin ciki da kuma na bakin ciki domin duk wanda ya kamata ya ga wannan farin cikin baya tare dasu,

" *Is this a scene or reality?*

Zazzakar muryarta ta karaďe dakin,
a tare suka kalleta tana tsaye sanye da bakin dogon wando wanda kasanshi yake a buďe sosai sai milk riga mai dogon hannu,
kanta yane da da bakin gyale wanda ya bayyana gashinta har gadon bayanta,

karasowa tayi hankali a tashe tana faďin

*ohh Abbu?*

wurgi tayi da jakarta kan doguwar kujera ta zauna kusa dashi,
hawayen ta fara share mishi tana magana da larabci,
tasan Irfan ne kadai kesa mahaifinta hawaye haka,
hoton da ya rike a kirjinshi ta karba ta zuba mishi ido,
ajiyeshi tayi a mazauninshi ta dafa kafaďunshi,

"Bazan hanaka zubar da hawaye ba dan nasan a wannan lokacin babu abinda zaisa su tsaya sai dai domin kansu,
tunda nazo duniya nake ganin hawayen nan,
plss Abbu kayi hakuri,
kayi tawakkali,
in kanada rabon ganinta zaku haďu cikin sauki in shaa Allah,


Fuskarta ya tallabo haďe da sakin murmushi a bayan kukan yace

"Allah ya kawo min lokacin my love,
yanzu na samu labarinta daga gurin Hilal,

kallon inda ya nuna mata tayi,
shigowarta tabbas ta ganshi, amma ganin halin da Abbunta yake ciki ya mantar da ita akwai mutum a gurin,


cikin ido ta kalleshi dan shima ita yake kallo tun shigowarta,
mamaki ya hanashi furta komai dan ya tsorata da hukuncin ubangiji,
irin wannan kamanni har haka, ya salam,
tabbas badan gogewa da wayewarsu ba daya bace da babu abinda zai hanashi kiranta da Nadeeyah,

Takalmin kafarta mai tsini ta cire ta mike rai a haďe ta isa gurin Hilal,
ta riga ta gama hararo abun da ya kawo shi,
tasan sarai yazo da niyyar cutar mahaifinta ne,
shekara sama da hamsin da batar ta sai yau zaizo yayi taking advantage din son da mahaifinta kema yayarshi yace ya san inda take,
in shi yasan inda take meyasa baizo da ita ba,

"Heyyy,
ta faďi haďe da buga hannunta a saitin idonshi,
firgigit Hilal yayi ya dan matsa dan baisan ta karaso inda yake ba,
kusa dashi ta zauna sosai tana fuskantar mahaifinta tana dariya dan kar ya gane manufarta,

"Wa ya aiko ka?
Ta tambaya ba tare da ta kalli inda yake ba,

cikin rashin fahimta ya share hawayen dake makale a idonshi yace

"Ban gane ba?

"Zaka gane,

hannu tasa cikin nashi tace

"Muje ciki akwai tambayoyin da zan maka,
mikewa yayi dan ta fara jan hannun tana tafiya,
da larabci tace mahaifinta tana zuwa...



Sosai ran Hilal ya baci da ta gama jero accusations dinta cike da faďa kamar zata mareshi,
maganarta ta karshe ce ta sashi daka mata wata tsawar da ta daidaita ta,

"Yesss nasan Irfan,
sani sosai,

"Ehen i knew it,
nasan Irfan ne yasaka wannan aikin dan ku samu kudin banza ku je kuyi iskancinku,
ku ko kunya bakwa ji,
at ur age baku san yadda zaku dinga samun daily income ba sai kunyi cuta,
to this deal is cancelled sai ku nemu wani,
nuna shi tayi da ďan yatsa tace

"Wallahi in na sake ganinka gurin Abbu na sai nasa anyi maka daurin rai da rai,
babu inda ba'a sanni ba world wide duk inda na nemi alfarmar a kam-----

Gerraut Hilal ya faďi haďe da buge hannun kasa,
duk sanyin da ya shigeshi na rashin Nadeeyah ya fice gaba daya,

"Count me out,
ban sanki ba, ban taba ganinki ba,
sannan Irfan a companyn nan na sanshi,
u most be stupid in har kikayi tunanin nazo nan ne dan kudin mahaifinki,
he called me himself,
go and ask him,
i'm his company architect,
ban taba ganinshi ba sai yau,
nd wat i saw ya sani faďi saboda ur aunt is my relative,
hannu na rawa ya dauko wayarshi ya nuna mata hoton Nadeeyah,
ganin jikinta ya fara sanyi ta kuma tsumu da mamaki ya sanya shi kwace wayar yace

"I have my own self respect,
nasan i'm nothing like ur father but i'm contented with the little i have,
am not needed here, kuje ku nemi  real yan uwanku tunda ni fake na kawo,
yana kaiwa nan yayi hanyar waje haďe da buga tsaki,

Da gudu tasha gabanshi haďe da rike mishi hannu,

"Sorry sorry sorry,

plssss... ta kara faďi haďe da tsugunawa a kasa,

kwace hannunshi yayi zaiyi magana yaji muryar Sheik a bayanshi,

"Kayi hakuri Hilal,
she is always like that,
akwaita da tambayar da zata kai mutum bango,
zo ka zauna na yarda da kai 100%,

juyawa Hilal yayi ya koma kan kujera ya zauna fuskar nan a murtuke,
wannan babu abun da ta haďa na hali da Nadeeyah,
kalamanta na cin mutunci sun mishi zafi matuka,
dannewa kawai yayi ya zauna dan sauke wannan nauyin badan ita ba sai dan Nadeeyah da su Hafeez,
tambayoyi sheik ya fara mishi,

babu abinda ya iya faďa mishi sai dai kawai ta Haifi twins...

Yadda yaga ya ruďe da murna ya kasa sanar dashi ta mutu,
a ranar maida Hilal ciki ne kadai sheik baiyi ba,
tafiya ya shirya musu da private jet din abokinshi dan baya son wani delay a zuwa ganin yar uwarshi da zuri'ata,


Murna tasashi ya yafe mata rashin nemanshi da batayi ba,
tasan irin ukubar da ta tafi ta barshi a hannun Ummul da 'yayanta,

share hawayenshi yayi bayan ya tuno gararanbar da yayi a baya wanda ya zame mishi tarihi...




Har Hilal ya bar office din bai kalli inda Maleeka take ba,
ita kuwa sai kai kawo takeyi da kayan kwadayi tana dire mishi, tasan bata kyauta mishi ba, idonta ya rufe ya hanata hango kamalar fuskar Hilal,

Sukuku ta yini ranar har ta koma gida,
duk abinda takeyi Hilal kawai take gani,
masifarshi da komai nashi burgeta yakeyi,
samm bai bata fuskar da zata amshi number shi ba,
tayi yawon duniya sosai, ta haďu da maza haďaddu wadanda suke macewa akanta,
bata karo da wanda zuciyarta tayi na'am dashi ba tun bayan Mutuwar Na'em sai Hilal,

*Saheebul qalbee*

ta furta a hankali tana mai hango soyayyarsu ta cikin film din..

"Kwatanta soyayyar da mai zafin zuciya irin Hilal zai fi armashi.. 

murmushin dake kan fuskarta samm yaki daukewa,
tana hango Abbunta da Ummi na sakkowa daga sama cikin jallabiya tayi saurin nutsuwa ta isa gurinsu dan tambayar inda zasu a daren nan...


Amsar da ya bata ya sanyata yin murmushi mai kyau haďe da cewa su jirata dan Allah zata rakasu,

"Jira fa Malee? Ummi ta faďi da harcensu na larabci tana rike haba..


Kwantar da kanta tayi a kafaďun Abbu tace

"Abbu kaga ummi ko?

"Zan jiraki,
komai dake zanyi,
ke zata fara gani tunda sunanta gareki,


rungumeshi tayi ta haye sama da gudu dan shiryawa....



40mins Ya Habeebi,
kasan jiran Maleekah...

bata gama rufe baki suka hangota cikin purple jallabiya mai walkiya,
kan nan ta yaneshi ta fito a balarabiyar asali,
light makeup tayi wanda ya fito da kyawunta na musamman,
kamshinta kuwa dadinshi kansa mai saurare yayi baccin da bai shirya ba,


*ATIKA ATEEK SAHEEB SAIFUDDEN* kenan

ta haďu matuka,
tun tana karama take sha'awar drama,
Shiyasa samm taki maida hankali a karatu,
gata da kokari sosai,
ganin hakan yasa Abbunta yi mata jumping,
tanada 14yrs aka kaita university inda ta karanci theartre art,
da yake field dinta ne sai ta dage sosai dan kullum cikin drama suke,
hakan yasa ta kware sosai,
a yanzu duk kasashen larabawa babu inda ba'a santa ba,
haka tsirarrun yan wasu kasar irin nigeria masu kallon arabic dramas suma duk sun santa,

shekarunta basu wuce 21 ba amma wayewarta ta zarce dan 30...



  "Kinyi kyau my love,

kiss ta mishi a kumatu tace

"Thank u Abbu,

nasan anyi complain?

Dariya yayi yace
"as usual, kin santa,

gaba ummi tayi tana dariya tace "kwaji dashi.....





Basu sha wahala gurin zuwa gidan ba dan estate dinsu sananne ne sosai,


Da fara'a Hilal ya taresu tun daga kasa,
dama ya gama shirya ma zuwansu,
ya faďa ma Anty Reemah zaiyi baki amma bai faďa mata ko su waye ba...




Zainab na zaune tana home work tana zana sunan da yake bace mata a kai,

Maleekah sahy,
Maleekah Sa'eed,
Maleekah sahab

haka ta dinga rubutawa a bayan littafinta,
ko da taji an murda kofar duk su Anty Reemah sunje suna musu maraba bata dago ta kallesu ba,


Na--deeyah...
Hinad ta faďi a hankali tana nuna Maleekah,
dago kai Zainab tayi ta mike da sauri ta isa gurinsu,
kallonsu ta shiga yi daya bayan daya,
tasan ba Nadeeyah bace,
dan in itace abun da zatayi mata ya wuce ta tsaya tana kallonta,


"Maleekah sahab ko?

Dariya Maleekah tayi ta tsuguna kusa da Zainab tace

"Saheeb dai my young fan,

ko dai brothernki ne ya faďa miki sunana, ta karashe tana kallon Hilal,

shuru Zainab tayi dan turancin na Maleeka yafi karfinta,


Anty Reemah ce ta katse shurun ta hanyar nuna musu gurin zama,

bayan sun gaggaisa Anty Reemah ta kalli Sheik cike da al'ajabi zatayi magana Hilal ya rigata dan baya son yasan mutuwar yar uwarshi samm sai yaje ga mijinta,



"Mum wannan kanin maman su mama suwaiba ne,
labarin yadda haďuwarsu ta kaya ya basu wanda ya cikata da mamaki,

"lallai komai da sanadinsa, sanadin aiki ya sa ka samo wannan muhimmin abun,
kaii masha Allah wallahi naji dadi sosai,

introducing dinsu Hilal yayi, yana zuwa kan Zainab da Sheik ya kasa daina kallonta yace

"Ur grand daughter sir,
she is urs!

hawayen farin ciki ne ya fito mishi dan yajita sosai a jininshi,

mikewa yayi ya dauketa sosai a jikinshi,
ya kosa a wayi garin gobe yaje yaga zuri'arshi, shakikanshi, wadanda yake da rashinsu tun kuruciya,
a gidan Papa ya samesu shima yayi farin ciki sosai sukayi hirar kasuwanci da na iyalai,


Sheik jin kanshi yakeyi kamar a yaune aka haifeshi dan ya fara jin kamshin yan uwanshi danginshi na uwa...





Assalamu alaikum.....


maida hankalinsu kan mai sallamar sukayi dukkansu,

Sauka jikin Abbu Zainab tayi ta ruga gurin Meerah,

"Anty Mee zo kiga Maleekah da nake baki labari dazu,

hankalinta sam bai kan zainab tana can kallon yadda Maleeka tasa kafa tana shafo ta Hilal yana matsarwa,
tray din hannunta ta damke dan kiriss ya rage ya faďi kasa,

"Muje zee,


Har kasa ta tsuguna ta gaida su Abbu sannan ta mike ta nufi kujerar da su Hilal suke,
kan hannun kujerar ta zauna,
ganin duk manyan suna can suna hirarsu yasata yi mishi raďa a kunne,


Dariya sosai yayi dan ya gama gane inda ta dosa,
mikewa yayi ya nufi dakinshi..

bin bayanshi tayi rai a bace dan ta gama kulewa,
dangwarar da tray din snacks din da tayo mishi tayi a kan madubi,


"Meerah plss,

kar muyi creating scene a gidan nan kinga munada baki,



"Eh naga baki,
su bakin da suka san inda sukazo ai na samesu suna hira,
kai fa,
ko kunyar idon iyaye bakaji ba ka zauna kusa da mace tana shafa maka kafa kana jin dadi,



Wannan karan dariya yayi mai sauti wanda ya kular da Meerah
ya sata sakin kuka mai karfi,

"La'ila,
ke rufa min asiri plss,
haba meerah,
yarinyar nan kema kinsan tafi karfina daga yanayinta in kika kalla,


"Me zanyi da yanayinta ni,
abun da idona ya gane min shi na lura dashi,
na gama fargabar wata yanzu kuma ga wata zata shi----


Meera..
ya katseta haďe da tsugunowa gabanta,
Na faďa miki soyayya yanzu na rufeta a shafin rayuwata,
bana tunanin zan sake faďawa cikinta so quick,
na faďa miki kiyi hakuri,
wallahi in nace miki zan yarda ki jirani nasan cutarki kawai zanyi,
bazan iya sake yin wata soyayya ba,
u are my best friend tun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login