Showing 78001 words to 81000 words out of 184071 words

Chapter 27 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt

bata bashi ansa ba ya cigaba da cewa
"ina tunanin dawo dashi garin nan Goggo zan kaishi asibitin dutse a duba shi, dan jikin nashi yaki dadi,


tabarya ta dago ta kundumo mishi ashar tace "Allah yasa ya mutu dan ubanka,

shege matsiyaci,


Fita yayi yana kunshe dariyarshi dan shi fushin nata ma dariya ya bashi.....




Mrs Tijjani Shattimah.......
[25/03 11:25 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 4⃣5⃣
By *Aysha Ya'u kurah*





A tare suka iso makarantar da uncle Taheer,

kallon gaban motarshi Hilal yayi ya hango Sabrinah a gaba tana ta zuba iyayi,

Gyara parking dinshi yayi ya kalli Husnah yace "ina sakon da kike ce zaki maida yau,
taba jakarta tayi tace "yana cikin nan,

"okay take care my personal p,
In shaa Allah ta fadi ta murda kofar fita,

Tun da suka tsaya take ta kokarin bude kofar ta kasa,
saida Husnah ta fita sannan ta matso dayan gefen dan ta bude,
A zatonta lalacewa abun yayi..


"Ki kula da abun da ya kawoki makaranta,
in kuma soyayya kika zaba to bismillah babu mai hanaki, its ur life afterall..


Cikin sanyinta tace "ba soyayya nakeyi dashi ba,
yace yana sona kuma har yanzu ban bashi amsa ba *ALLAH*,

sai a lokacin Hilal ya dan samu nutsuwa ya waigo ya kalleta,
narkewa zuciyarshi tayi saboda yanayin da yaga fuskarta,

Cikin muryar da bai san yana da ita ba yace "kin tanadi amsar bashi?

"Um um,

ta fadi tana girgiza kai,
hannu tasa ta kara gyara hular kanta da ta kakarce dalilin girgiza kanta da tayi,

Bakar hular sanyin dake ajiye a gefen motar ya mika yace "wannan nada dan girma ki sata,
ki daina saka ta kanki tunda tayi miki kadan,
sannan in kika dawo gida zan baki amsar da zaki fada mishi,

Dafatan ba saina sake tuna miki dalilin zuwanki makaranta ba,

Yadda yayi maganar cikin dakiya yasata kallonshi,
ido ya daga mata alamar kin gane,

Sanya hular tayi da sauri tace "Eh in shaa Allah,

"Good ya fadi hade da cire lock din ya fito ya bude gefen da take,

yana hango Taheer tsaye a gate da Husnah da wasu yara a gefe,
tana fitowa a motar ya dakatar da ita ta hanyar gyara mata gashin da ya leko,

"wai bakya kitsone?,

ya fadi a saitin kunnenta,

gyada kai tayi tace
"ko yau nayi zai warware,

"okay to sai a yankeshi kawai ya fadi yana kallon yadda zatayi,

Dariya ce ta kubce mata tace
"to in na dawo zan yanke,

"akwai barber karki damu kina dawowa sai muje,

Maza ki shiga school nd becareful,

"In shaa Allah ta fadi tana mamakin yadda ya damu da ita a yan kwanakin nan,
mutumin da ba kowa yake kulawa bare har kaga dariyarshi,
ta ta'allaka abun da tausayinta yake ji da kuma shakuwarsu da zainab,

Harde hannu yayi yana kallonta har ta karasa gate din,

"Good morning sir,
ta fadi hade da rankwafawa,
duk yadda yaso danne abun da ya tokare wuyanshi ya kasa,
bai amsata ba ya juya dan komawa office dinshi,

Husnah da hankalinta ya gama tashi tace "pls sir plss kasa baki ya barmu,
bai waigo ba dan a harzuke yake matuka,

Ko Musaddiq da Hilal yace shine wanda zai aureta bai tsaneshi ba kamar yadda yake jin tsanar Hilal,


Yana shiga office ya jingina jikinshi jikin kofar office din zuciyarshi sai tafasa takeyi,

Allah kadai yasan adadin abubuwan da suka dahu a cikin zuciyarshi,

  Yana tsaye a gurin yaji bugun kofar office din,

dakyar ya iya matsawa hade da bude office din,

Husnah ya gani tsaye tana mishi murmushi,

"ehen what again?

Shigowa tayi ta sauke jakar makarantarta tace

"Sir dakyar uncle Kamal ya barmu muka shigo school kuma yace mu cire black legens din jikin mu,

Ledar da ya kai gidansu ta ciro ta mika mishi tace
"ance in dawo maka dashi,
bai kalli ledar ba yace

"Okay ajiye ki tafi,
ajiyewa tayi tace "sorry sir,
gidan mu ba'a tsayawa da saurayi sai an gama sec school,

Kaga Daddy baisan ka kawo ba Yaya Hilal yace a maido maka,

"nt bad jeki kawai...
ya fadi yana gyara gujerar da zai zauna,


Tana fita ya kifa kanshi a tebur,
tunani kala kala babu wanda baiyi ba,

Da sauri ya fatattaki tunaninshi na karshe na

" *ka rabu da ita*,
dan bama zai iya imagining ba, bare ya aiwatar,

Mikewa yayi dan zuwa ajinsu duk da yau bazai musu darasi ba,

sa'a yaci da ya shiga babu malami dukkansu suna zaune suna hira,

Gaisheshi dukka ajin sukayi ya amsa hade da cewa su zauna,

Rasa abin ce musu yayi dan ba darasi yazo basu ba,
saida ya kusa 5mints sannan yayi tunanin neman wadanda zasu gyara mishi office,

Dadi tunanin yaji a zuciyarshi ya kalli duka yan class din yaga kowa idonshi na kanshi ita kadai ce kai a sunkuye,


"Hey u with black cap,

" *kyari*

sunan dake rubuce a jikin hular, tabo ta *Amal Mus'ab* tayi  tace "Nadeeyah ke yake kira,

Mikewa tayi da sauri tace

"yes sir, keyn office din ya bawa khalifa yace
"mika mata taje ta gyara min,

da sauri Sabrina ta mike tace "zanyi sir,

"noo zauna ki huta,
ya karashe yana fadin hv a nice day class,

thank you sirrrr...



A hanyar shigowa harabar clases din ta ci karo da Badariyya,

Ja baya Nadeeyah tayi dan ta bata hanya,

wani irin kallo Badar ta bita dashi from head to toe,

tana zuwa daidai kanta taga hular wanda take kira da *Rayuwarta*

*iyyye.....*

Badar ta fadi tana kallonta shekeke,

uban waya baki hular nan, 

Taba hular Nadeeyah tayi taga babu amfanin bata amsa tayi saurin bi ta gefenta zata wuce,

Janyota tayi ta zare mata hular tace

"ke har kin isa ki hada jiki da shi, tattara gashinta da zubo har gadon bayanta tayi ba tare da ta amsa ta ba ta juya dan komawa dauko hularta,

Hada ido sukayi yana tsaye duk abin da Badar tayi a idonshi,

"zan dauko hula ta a class sir,

karasowa gurin Badar yayi yace "Hular ki ce,
girgirza kai tayi tace
"ta mijin da zan aura ne,

"ikon Allah ya fadi cike da mamaki,

"ehen ita kuma wacece kenan a gurinshi,

"ba komai bace sir,
kawai dai tana zaune a gidan mu ne,
mamanta da babanta sun mutu,
talauci yasa yayansu bazai iya rikesu ba shine aka dawo dasu gidanmu,

"Nan da nan alamun shi suka sauya yace "abin da na tambayeki kenan?,


"Na baka amsar abin da ka tambayeni a farko na cike da karin bayan ta fadi tana turo baki,

Hannu ya mika mata yace "bani hular nan,
rai a bace kamar zata mutu tace "sir ya za'a yi tasa min hul---

give it here ya katseta cikin tsawa,

Daura mishi a hannu tayi tana kunkuni,


Mikama Nadeeyah Hular yayi ya wuce,

ďan labarin ta da yaji ya sanya mishi kwadayin sanin cikakken labarinta.....





"Alo Hajja Saude,
kiyi  hakuri bazamu samu daman zuwa yau ba,
zamu tafi morocco kai *ummu Ayyu* asibiti,
jikin yaki,


Gyara zaman wayar Anti saude tayi a kunnenta tace

"Allah sarki, jikin har yanzu dai,
to Allah ya bata lafiya,
babu komai, karku damu ni zanje in fara gabatar dashi kafin ku dawo,



Cikin jindadi aminan suka hau hira duk akan sarautarsu da kuma familynsu.....





Hoton da ta gani a kan table din ta dauka tana kallo sosai,
saida tayi mishi guga na musamman sannan ta ajiye,
tana gama gyaran office din ta sake daukar hoton tana kallo,


Hakanan taji mutumin cikin hoton ya shiga ranta,


Sanye yake cikin babbar riga da hula,
yayi kyau sosai,


Tana kokarin ajiye hoton taji yace "my late Father
" *Alhaji Haroun Yallo*,


Ajiye hoton tayi da sauri tace sorry Sir,

na gama yanzu zan wuce class,


Bashi da niyyar matsa mata a makaranta sam,
dan a yadda ya tsara a makaranta nuna mata rashin sani zaiyi kururu.
amma ya zaiyi,
soyayyarta ta hanashi katabus,


Takowa yayi ya karaso inda take tsaye ya dauko hoton,


"Wannan shine Mahaifina,
rayuwar da mukayi dashi ba mai goguwa bace,

kullum in ban tunashi a duk numfashin da nakeyi ba to tabbas zan tunashi a duk takun da zanyi a rayuwata,

He is my best friend,


Mutuwarshi ita ta kashe wasu sassa na farin cikin dake cikin zuciyata,

mutuwa ce wacce yayi ta ba zato babu tsammani,


Ajiye hoton yayi yace

"Mutuwa wata abace wacce zafinta yafi dukkan zafin wutar dake cikin duniyar nan,

zafin wuta na warkewa ya barka da tabo,

amma mikin rashin makusanci kullum sabo yake zama,


Mahaifina ya nuna min kauna har ranar da zaiyi tafiyar din din din,


"A ranar da zai mutu ranar na dawo daga Canada,


saboda kar ya daga hankalinmu shiyasa ya boye mana ciwonshi, ya dinga biye ma duk wata rigima tawa,

Tare muka je aski,
cikin rashin sanin yana ciwo nasa akayi mishi askin dukka kanshi dan ya zame min abin tsokana,
haka nan badan yana so ba ya yarda akayi mishi,

Daga gurin askim muka wuce yawo muna ta zaga gari muna ziyarar gidajen Abokanshi,



Masallacin cikin gidan mu nan ne guri na karshe da muka tsaya,



A daddafe ya idar da sallar magriba,
jin irin numfashin da yake fitarwa ya sani tambayarshi ko baida lafiya ne,
dariya ya kakaro hade da naushin cikina kamar yadda muka saba yace
"in yana da ni ta ina ciwo zai samu muhalli a jikinshi,


Nan take Muryar Taheer ta raunana, hawayen da suka cika idanuwanshi suka dinga tsere a tsakaninsu,

ya cigaba da cewa

"A sujjar karshe ta sallar isha'i karfin Abbana ya soma karewa,

Gaba daya masallacin yayi shuru saboda jam'i da ake bi,

numfarfashin Abbana kadai ake ji a ciki da wajen masallacin,
gaggauta yin sallama liman yayi,

kowa yayi kanshi saboda ganin har lokacin bai dago daga sujudi ba, kuma bai bar fitar da numfarfashi ba, 

Ko da aka dago shi ya gama fita cikin hayyacinshi,


A lokacin wanda ya taba dandanar mutuwa zai fahimci inda Abbana ya dosa,


Dagoshi nayi da karfi ina fadin ya tashi muje asibiti,

Girgiza kai ya shiga yi yana fadamin "ka barni anan Taheer, ka barni anan,
asibiti, ko
gida,
a yau basu da amfani a gareni,


Murmushi yakeyi mai dauke da kuka yana fadin Taheer kayi hakuri,
kayi hakuri abokina,
na boye maka ciwo na saboda nasan ba na tashi bane,

Naso sai ka koma makaranta zanyi tafiyar nan amma inaa lokacina yayi,
ban isa kara kwana daya ba koda kuwa ina son kara shi,



"Kukan da Taheer yakeyi a lokacin mai sautine dan bai taba fitar da wannan labarin da yayi mishi karan tsaye cikin rayuwarsa ba sai yau da a karo na biyu yake shirin rasa wacce yake tunanin dawowar farin ciki cikin rayuwarshi,


Ita din ma Nadeeyah kukan takeyi na tausaya mishi da tausayawa kanta,
domin ita ma tayi rashin dukka iyayenta,



"Ban taba kawo mishi mutuwa ba saboda ban yarda zai tafi ya barni a wannan lokacin ba,

kin saurararshi nayi muka daukeshi dan kaishi asibiti,
ina tuno sanda ya shafa fuskata muna gab da fita daga masallacin yace
"Taheer kaki yarda ko?


Dole ka yard---a d------a wann----
nan ya fara kakari har yafi karfin wadanda suka rikeshi,

ka-- kula  da--- kanka da-- da-- mahaifiyarka,

damke hannuna yayi har lokacin idonshi bai gama rufewa yana tayi min murmushin da ya saba,


"A wannan ranar ne na ga abun da ake kira damuwa karara,

a wannan bakar ranar naga kaddarar rabuwa da abin da kakeso,  a wannan daren mahaifina ya mutu tare da duk wani kuzari nawa..



Tun daga ranar na manta farin ciki da yadda akeyinshi,
babu abin da ke burgeni a duniyar nan bare har yasani farin ciki,


Rabuwa da Abbana....


ya ilahi!!
nan da nan Nadeeyah ta rikice saboda yadda yake kuka kamar ana zare ranshi,

kuka sosai yakeyi wanda bai samu damar yinshi ba ranar da ya rasa mahaifinshi,


Abubuwan da suka cunkushe mishi ya fitar yau yake kokawa a kansu,


shakuwar da yayi da mahaifinshi ta wuce ta ďa da uba,
ta zamo shakuwar jini da hanta,

a ko da yaushe ya rufe idonshi murmushinshi kadai yake gani,

bai taba karo da bacin ranshi ba sai dai farin cikin shi,



Gabanshi ta tsuguna itama kukan yaci karfinta tace

"Uncle kayi hakuri,
sau tari abubuwan da muke so basu cika kasancewa tare damu ba,

jarabawar mu kenan,
gara kai kana da wacce in ka juya zakaji dadi,

ni fa babu uwa babu uba,
babu yan uwan uba da zan kirasu nawa saidai na uwa,


ka godewa Allah domin not all are fortunate,


Duk abinda kaga Allah ya dauke maka to yana da dalilin yin hakan,
ta yiwu in ya bar mana su wata rana saboda azabar ciwo mu gwammaci tafiyarsu akan tsayuwarsu cikin ciwon da mu kanmu bamu isa mu magance musu ba,
nasan yadda kakeji domin nima ina jinshi ko ma ince fiye da naka,


Dan Allah a duk lokacin da ka tunashi ka dinga fadin *innalillahi wa inna ilaihir rajiun*
sannan kayi mishi addu'a domin yafi bukatarta a yanzu....



Wata irin nutsuwa ce ta saukar mishi wanda tun kafin rasuwar Abbanshi rabon da ya shiga irin ta,

share hawayen idonshi yayi ya dago ya kalleta,


Sai a lokacin yake tambayar kanshi dalilin dayasa har ya fada mata damuwar da ya dade yana dakonta,


Tabbas zuciyarshi ta gamsu ita ce wacce zai samu nutsuwa da ita,

kalamanta sunyi matukar sanyaya mishi zuciya,

jin zuciyarshi yake wasai kamar an sauke mishi duk wani nauyin da zuciyarshi ke dauke da shi,


Tsugunawa yayi kamar yadda tayi yace

"is ok, kukan ya isa haka,
ni nasa ki kuka,
ni kuma na daina ke kin ki dainawa, sorry kinji,
tashi ki zauna...


Mikewa tayi tace
"zan tafi class ne,

kujera ya ja mata yace
"kice wa ya saki kuka?


Ajiyar zuciya tayi mai karfi sannan ta zauna,


Ji yakeyi kamar ya rungumeta ya hanata wannan kukan da yasan irin ciwonshi,

"nace ya isa ko nima so kikeyi in cigaba,

kinsan in na fara nawa biyu zan hada,

da na rashin mahaifi da kuma rashin farin cikin rayuwata,
ya karashe fadi a raunane cikin damuwa,


Share hawayenta tayi kamar me shagwaba tace

"na daina,


"Kina sona Umm Nadeeyah?

Yadda ya jefo mata tambayar ta sanyata saurin dauke kanta daga kallonshi,

"ummm bani amsa plss,
nd "who is Musaddiq? Ya karashe yana janyo kujera...



"Yaya Musaddiq? Ta fadi tana kallonshi,

gyada kai yayi yace

"yes waye shi, meye alakarku?


"Babu komai,
he is my cousin, 
"nd husband to be, Taheer ya karashe yana kallon cikin idonta,


A razane tace

"whatt,

ba gaskiya bane,

kaga sister na wacce ta karbi hula dazu?

Gyada kai yayi alamar eh,
"to ko zaiyi aure nasan ita zai aura,

wannan hularshi ce

"ya Hilal ya bani shine ta dauka shi ya bani,

"yaya Musaddiq is very nice, bashi da matsala,
yadda ya dauki su Husnah haka ya daukeni,

cike da gamsuwa ya dan samu nutsuwa yace

"Hilal kuma ya kuke dashi?

Murmushi tayi tace
"dan yayata ne,

He is like an angel to me sir,
he wants the best for me,


Bayan yaya Musaddiq da ya nuna tausayinshi ga iyayena,


Yaya Hilal shi yake bani duk wata kulawa lokacin da na rasa iyayena,
he luks after komai nawa,
movements dina da komai,

he wants me to be an independent lady and----



katseta yayi ta hanyar cewa yayarki ce ta haifeshi,

i mean mamanku daya da mamanshi?

"No Anty Reemah yayar Husnah ce,
she is my cousin,



"Okay
kawai yace ya kauda maganar ta hanyar cewa bani amsar farko da na tambayeki,



Ya zame mata dole ta fada mishi gaskiyar yanzu babu soyayya a gabanta,


Danne tausayinshi tayi a can kasan ranta tace

"Uncle,
shhhh nt uncle,
Taheer...
ya fadi yana mata wani narkaken kallon da ya kashe duk wasu gabbai na jikinta,

Call me TAHEER,
ina son jin sunan daga bakinki plss,

marairaicewa tayi tace "no sir i can't,
sorry plss,
"zaki koya with time,

inajinki!




"Kayi hakuri in abun da fada maka yayi maka ciwo,

bance bana sonka ba,

a yanzu ba soyayya bace a gabana,
nasan in kana sona sosai kamar yadda kace zaka girmama ra'ayi na,


Dan Allah sir mu ajiye maganar soyayya yanzu,

kayi hakuri ka taimakeni in taka matakin nasara a rayuwata,

in Allah ya rubuta kai din mijina ne, babu wanda ya isa ya rabamu saidai mutuwa,

Dan Allah uncle kayi hakuri,
mu yarda duk abin da Allah ya rubuta akan mu shine alkhairi,


"Murmushi ya sakar mata mai kyau zuciyarshi ta samu nutsuwa da kalamanta,

dole ya girmama ra'ayinta yayi nesa da ita ya tayata cika burinta,


yasani kamar yadda ta fadi in har kasantuwarsu tare rubutacce ne a lauhil mahfuz, babu makawa duk inda taje dole ta dawo gareshi,


A yanzu jin kanshi yakeyi kamar sabon mutum wanda ya yarda da duk abin da ya faru dashi kaddararshi ce tazo da haka,


"Na amince da bukatarki,
zan kuma girmama ra'ayinki saboda karatu nada matukar muhimmaci a rayuwar mace,
musamman marainiya irinki, naci burin aurenki a cikin kwanakin nan,
nasan inada karfin kaiki bangon duniya kiyi karatu in har anayi,

to nima inaso ki samu abin da kike so,

lokacin da kika mallaki hankalin kanki you decide who u want to settle with,
i pray to Allah nine wanda zuciyarki zata amince dashi a lokacin,


Zan kauracewa ganinki har kiyi achieving goals dinki,
saboda ganinki zai dinga hanani sukuni har in kasa tayaki cika burinki,



Wani zobe ya fito dashi a jakarshi ya mika mata yace
"Aure nufi ne na Allah,
in Allah yayi ni mijinki ne kamar yadda zanyi addu'a ba dare ba rana to babu makawa sai na aureki,


ki rike wannan zoben a matsayin kariya daga gareni,

"Take care of yourself please,
u will always be my omri..



Hawayen da ke makale a idonta ne ya sauko ta kasa dauke idonta akanshi,
hannu yasa a lallausan kuncinta ya share mata hawayen yace

"bana son kuka Omri na,
karki dinga kuka kinji,
duk abin da zai dameki ki tuno *Taheer Haroun Yallo* yana tare dake kuma baya san ganin damuwarki,


Mikewa tayi da sauri ta fita daga office din,

bayan office din ta zauna ta dinga zubar da hawayen tausayin Taheer,

shine mutumin da ya fara furta so a gareta,

badan santa da karatu ba da babu abinda zai hanata amince mishi,


zoben ta kalla ta kankameshi a kirjinta kamar zata maidashi cikinta....



A bangaren Taheer kuma daurewa yayi sosai ya iya yi mata wadannan alkawuran,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login