Showing 183001 words to 184071 words out of 184071 words

Chapter 62 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt

kinka dashi,
dafe kanshi yayi da hannayenshi biyu saboda hawayen dake zubo mishi babu kakkautawa,

Mikewa Taheer yayi dukkan lakar jikinshi a sake ya kama hannun Junior suka sauka kasa,
a hanyar da zai sadasu da kofar fita ya haďu da Hilal da ya dawo daga rakiyar abokansu,
shima duk ya fukace ya fita hayyacinshi kamar shine mai ciwon,
"A'a yallabai har kun fito,
ya faďi yana mika mishi hannu,

"Eh dare nayi,
Allah ya bashi lafiya,
"Ameen Hilal ya amsa haďe cewa sai da safe mun gode,

"Allah ya tashemu lafiya Taheer yace yana mai saka kafarshi a waje,


A gurin motarshi suka tsaya ya kira number Nadeeyah wacce ke kan dadduma tana zubda kwallar da ta zame mata jiki,
a hankali ta ďauka cikin nuna bata cikin damuwa tace
"Uncle kun wuce ne?

"No muna waje,
muna san ganinki ne ya faďi wani ďaci na tokare makogaronshi,

Kara sassauta murya tayi tace "Gobe ne fa, daga gobe bazan sake barin gefenka ba, har sai ka gaji da ganina,
kayi hakuri plss,


Lumshe idanuwanshi yayi haďe da kallon sama a zuciyarshi yana rokon ubangiji sassauci akan wannan jarabawar,
*Tayi min tsauri da yawa* ya faďi ba tare da yasan ta fito ba, yana mai kwantar da kanshi kan murfin motar,


"Gani nan zuwa Uncle, in dai rashin ganina yayi maka tsauri, bakayi deserving shan wahala akaina ba,
bata jira amsarshi ba ta kashe wayar ta mike haďe da ninke dardumar tayi waje....
Duk abin nan da sukeyi a kunnen Raudha wacce ta fashe da kukan Nadama,
gashi dukkaninsu na suffering daga mugun halinsu,
babu wanda ya tsira,
shiyasa akace Sharri dan aike ne, in ka aikashi dawowa yakeyi ya shafi wanda bai nan sanda kayi aiken,
tayi nadama matuka a yanzu da itama bata ga tsuntsu,
domin ko ďuriyar 'yayanta bata ji, har gara Radiya ta roki Shamsu ta waya yayi mata alkawarin yana dawowa italy zaizo su sasanta,
ita fa, babu waya daga Abbati bare har tasan ko har yanzu yana nan da ragowar soyayyarta a cikin ranshi,

Addu'a ta shiga yi ba kakkautawa tana faďawa Allah damuwarta haďe da neman afuwarshi.....




Cike da kulawa ya kalleta yace "Kuka ko?
Wa ya sa kanwata kuka har ya koďar min da idanuwanta?

Rufe fuskarta tayi da hijab kukan da ke tokare a wuyanta ya fito da karfinshi,
barinta yayi tayi ma'ishi sannan yace

"Me kike so?
Tell me ko me kike so zanyi miki in dai zai saki daina zubar hawaye kullum,
Junior ya faďa min bakya cin abinci,
bakya kula dashi,
har ihu kike mishi,
tell me ur problem,
i promise to solve it for u komin wahalarshi...



Hannunshi ta riko a hankali tace "With u my problems are always solved,
bani da wata matsala Uncle, thanks for always being dere for me....



Sanya hannun yayi ya share mata hawayenta shima duk gabban jikinshi a karye suke a zuciyarshi yace

"I will also solve this for u, sadaukarwa a soyayya wani abu ne,
i will make sure u get wat u want,
a fili kuma cewa yayi ta kwantar da hankalinta zai cigaba da solving ko wace irin matsala tata har ranar da kasa zata rufe idonshi..



kwantar da fuskarta tayi kan tafukan hannunshi wasu sabbin hawayen na zuba a kansu..


"Bari in tashi Junior yazo yaga shagwabar da baya yi Mamma nayi,
abin kunya ya faďi cike da zolaya yana girgiza kai,


Dariya tayi sosai tace
"Kai ka koya min, leka cikin motar tayi ta hangoshi kwance ya mike yana bacci,
"ya kamata ku tafi gida,
plss uncle kuyi bacci gobe kasan zakasha wahala sosai,

"Ai bakinki ne wahala,
ke zanma wannan faďan,
kuma ki tabbatar kinci abinci yanzu kafin ki kwanta,
inason gobe in ganki kinyi kiba kamar Husnah kina jina ko,


Buďe baki tayi tana dariya tace "sai dai in kamoka,
ko kuma------

Ihun da suka jiyo a cikin gidan ne yasata katse maganar da tayi niyya,
tabbas wannan muryar Hilal ce sai kuma ta Husna da ta biyo baya,
da sauri ya rufe kofar suka ruga ciki da gudu..





Ganin daukacin yan gidan sun nufi dakin da Musaddiq yake yasasu nufar ďakin suma,
a tare suka iso ciki da Daddy,
abin da suka tarar ne tada hankalinsu,

Hilal ne ke kokawar kwace kwalbar hannun Musaddiq ya kasa saboda wani irin karfi da ya karu wa Musaddiq,
sannan kuma girman ba ďaya ba, duk sauran yan uwanshi dake gurin sunyi yunkurin karba ya hanasu,

Tsaye Daddy yayi ya kasa tabuka komai saboda bashi da karfin yin wani abu domin yayi iya kokarinshi ya fahimtar da ďàn nashi ba komai kake so kake samu ba,
bazai iya tunkararsa ba a yanzu ya riga ya sare da rayuwar danshi,
yasan zaiyi matukar wahala ya rayu..
ganin Daddy ya kasa cewa komai yasa su Anty Reemah sake sakin wani kukan,
ita kuwa Husnah kiran wayar Hafeez da Papy takeyi tana ihu tana kiran sunan Musaddiq,


Da sauri Taheer yayi gurin suka haďu da Hilal suna kokawar tare,

wani hauri ya kaiwa Hilal a ciki wanda sam baisan yayi ba ma,
ya riga yaci alwashin aikatawa shiyasa yasa ďaya daga cikin abokansu siyo mishi ba tare da yasan abun da zaiyi dashi ba,

sannan abun da idonshi ya gane mishi daga sama shi ya sake tunzura zuciyarshi ya tabbatarwa kanshi babu fashi sai ya aikata abun da yayi niyya...


Rike ciki Hilal yayi ya kasa tashi aka bar shi da Taheer da ya matse hannunshi koda kuwa kwalbar zata tsaga dukkan hannunsu,
ba tare da ankara ba Taheer yaji nashi ta bayan hannun,
a gigice ya saki hannun wanda hakan ya bawa Musaddiq damar ďaga kwalbar da sauri,
ihuu dakin ya dauka suna rokarshi da Allah da annabi,


Juyawa Daddy yayi ya bar ďakin yana mai kuka cikin zuciyarsa na irin tarbiyar da kowanne cikin 'ya'yansa suka samu,
ya sadakar ďan da yafi kowa kauna cikin yayanshi yau zai kauracewa ganinshi,
ya barshi ya aikata abun da yake so domin kuwa ko ya hanashi sai ya aikata tunda tun tasowarshi bai nemi abu ya rasa ba sai wannan..



A hanzarce Nadeeyah ta haye gadon da zai sadata da daidai hannunshi ta sanya iya karfinta ta kabe hannun haďe da daukeshi da lafiyayyun mari har biyu sannan tayi mishi wata iriyar runguma wacce bin umurni ne daga zuciyarta,


Tsittt dakin yayi kamar babu wani mahaluki da yake rayuwa a cikinsa,
daddadar muryar Nadeeyah kaďai ake ji wacce take fitar da ita cikin raunannen kuka.......





Mrs Tijjani Shattimah........

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login