Showing 12001 words to 15000 words out of 126208 words
Chapter 5 - ALKAWARIN ALLAH BOOK BY HUGUMA.pdf
yaqi fita daga ranki kamar sauran abubuwa?" Kasa bata amsa tayi sai tafukan
hannayenta data saka guda biyun ta rufe fuskarta dasu,ita kanta tana son ta koma normal,tana
son ta zama kamar kowa,tanason ta manta da komai amma ta gagara yin hakan?,me yasa
abun yafi tsaya mata fiye da komai?.
A jigace ta dawo gida bawai don tayi wata gajiya ta azo a gani ba,illa dai zuciyarta data
dahu lugub ta kuma saare tun sanda yaran suka jefa mata tambaya a kanshi,batayi dogon
zama a falon ba ta yiwa anty zubaida sallama kan cewa gobe da wuri zata tashi tana son isa
makaranta da wuri don gobene ranar hutunsu.
*1:26 pm*
Tsaye yake cikin wani makeken fili wanda ya qawatu da fareren furanni tas da jefi jefin
koraye,waje ne daya ni'imtu,ya kuma qawatu da wata irin iska mai dadi da taush take kai kawo
iya fadi da girman filin,cakude iskar take da qamshi mai sanyi wanda ke ratsa zuciya,fararen
kayane qal a jikinsa,yana tsaye gaban wata qaramar qorama mai garai garai,kana iya hangen
kifayen dake linqaya da kai kawo daga can qasanta.
Ingarman bayanshi take iya hangowa,ta zuba mishi idanu tana jin wani bugu da zuciyarta
keyi,tana jin tsoro da zumudin tunkararsa lokaci guda na mamayarta,a hankali ta dinga takawa
gareshi,iska na diban gashinta tana watsashi gaban fuskarta hagu da damanta,lokaci lokaci
tana sanya hannu tana d'aukewa.
Dab da bayanshi ta tsaya taci gaba da kallonshi gabanta na faduwa,tanajin kamar zata kira
sunanshi sai bakinta ya kasa furta komai,ta dan jima a haka sannan ta miqa hannu da niyyar
kama kafadarsa sai ya waiwayo,fuskarshi cike fal da annuri kamar yadda ta saba ganinsa,yayi
kyau ya canza kamar bashi ba,cikin sakan kad'an dukkan wani annurin fuskarsa ya gushe,ya
hade girar sama da qasa,bacin rai ya bayyana qarara a fuskarsa
"Me kike yi a nan?!" Ya fada cikin tsawa da fusata
"Ban sani ba!" Itama ta maida masa cikin tsawa da fushi,sai kuma ta juya cikin gaggawa ta
bashi baya ba tare data bar wajen ba,ta d'an jima ahaka sannan ta waiwaya,saidai wayam baya
wajen,babu shi babu alamarsa,wani tashin hankali da batasan na meye ba ya rufto
mata,musamman sanda taga duhu ya soma mamaye wajen,kiran sunanshi ta soma yi a jere
babu qaqqautawa,saidai babu alamun yana jinta bare ta saka ran zai amsa.
A firgice ta miqe daga kwanciyar da take bakinta d'auke da sunanshi kamar yadda take
kiranshi cikin mafarkin,a hankali hankalinta ya dawo jikinta ta fuskanci mafarki ne,saita sauya
sunan nashi da ambaton sunan Allah,yayin da hawaye ya soma sauka daga idanunta masu
zafin gaske,wanne wacce irin jarrabawa ce?,har a mafarkin ma bazai haqura ya barta ba,tayi
shiri hakanan ta tattara dukkan qarfinta tana yaqi dashi haiqan,saidai ta fuskanci kaman fad'an
gwaggo a kofa take.
Sai data gama kukanta son ranta sannan ta sauka a hankali don karta tashi huda da yau
take tayata kwana,ta shiga bandaki ta daura alwala,saidai yau ta kasa sallar kamar tadda ta
saba,saboda wata irin kasala da mutuwar jiki data sakar mata,abinda ya gudana a mafarkin ya
soma dawo mata tar a kwanyarta,duhun da taga ya soma mamayarta shine abu na farko daya
daga mata hankali,me hakan yake nufi kenan?,saita tuna ranar da suka ga fuskokin juna na
qarshe,komai ya soma dawo mata d'aya bayan d'aya cikin rayuwarta kamar wadda aka
kunnawa magijin film.
*_ZAN RAYU DAKE_*
Ranta a matuqar bace take kallon botikanta guda biyu dake shaqe da shinkafa da waken
sadaka wanda tuni suka hadu da qasa suka saje,botikam kuma sukayi fata fata dasu,sannan ta
sake d'aga kai ta dubi ahmadi dake tsaye gabanta shida abokanshi biyu yana kallonta cikin
gadara "Anzubar kiyi duk abinda zaki,yarinya ba kowan kowa ba sai shegen isa da izza,don kina raba
mana sadaka saikin gindaya mana sharadi,bamu da hannun diba mu zuba da kanmu?"
"Ni kuka yiwa haka?" Ta fada tana hadiye wani qullutun bacin rai da baqinciki
"Ke aka yiwan,ki dauki duk matakin da zaki dauka"
"Xaku ga gatana" ta fada a sanyaye bayan ta duqa tana tsince abinda xai iya daukuwa a
wajen,ta fadi maganarne kawai ba don tana da gatan ko me tsaya mata ba,ta fada ne kawai
saboda bata da abun cewar
"Waye gantanki?" Ya fada bayan sun sheqe da dariya duka su ukun
"Nine gatanta!" Wata kakkausar murya ta ratsa dariyar tasu,cak suka tsaya da dariyar,basu
kadai ba har itama dagowa tayi daga tsintar da take tana laluben ina mai maganar yake da
idanunta,matashin saurayi ne wanda duka duka a qalla bazai haura shekara ashirin da biyar
ba,wankan tarwada ne dogo wanda da alama yana yin qiba zata boye tsahonsa,yana da kyan
fuska mai qayatarwa irin kyan da kama kallonshi kasan cikin yaren hausa fulani yake,kuma
tabbas sahun farko da kyawawansu,ma'abocin kwarjini da kallom farko kawai zaka yi masa
kwarjininsa ya tabaka,fuskarshi a tsuke take babu alamun annuri a tare dashi yake takowa
gabansu ahmadi,kwarjininsa ya sanyasu tsayawa cak,fargaba ta kamasu,saida yayi gab da
ahmadi kamar zai fada jikinsa don har yana dan take masa qafa yace
"Me tayi muku?" Cikin tsoro tsoro da son nuna jarumta yace
"Raina mana hankali take,kullum ta kawo abincin sadaka sai ta rainama mutane wayo" a
hankali ya waiwaya ya dubi gefanshi inda take tsaye,karon farko idanunsu suka sarqe dana
juna,wani irin nauyi taji da batabtaba jinsa ba sanadiyyar kallon idanun wani a duniya,kamar
yadda shima yaji wani yanayi da baisan na meye ba ya saukar masa harsai daya lumshe
idonsa ya kuma bude cikin sakan biyu,hakan ya sake qara kwarjininsa da kashe jikin shahida
"A'ah,wallahi ahmadi baku da mutunci" muryar wani dattijo dake xama a wajen lokaci zuwa
lokaci ta katsesu,duk suka maida hankalinsu kanshi sanda ya gama tattare buzunsa da yake
zama yana dinkin takalma,ya qaraso wajen yana nuna su ahmadi da yatsa
"Yarinyar nan tunda ta soma zuwa wajen nan kuka kafa mata qahon xuqa,da kuka fuskanci a
kintse take shine kuka tsiri takurata,kowa ya shaidi yarinyar nan tunda take zuwa wajen nan
bata da abokin fada,hasalima taimakonmu take,bamu da abin ce mata sai godiya,kullum daga
kwanonta muke ci mu qoshi,bata taba bude baki ta kula wani ba bare rashin kunya ta biyo
baya,dama yau tun dazu na kula da take takenku shi yasa naqi tafiya gida da wuri har sai ta
tashi,ashe kuwa tsiya kuka shirya" a hankali ya dauke kyawawan idanunsa daga kan dattijon ya
maidasu kansu ahmadi da duka gama tsurewa saboda bayanin da baba isuhu ya kwararo,sosai
ya kafesu da ido wanda har sai da sukaji kallon har cikin lakarsu
"Kubar nan,daga rana irinta yau kada na sake ganinku a nan arean,koda kuna da abunyi har sai
ta gama raba abincinta ta tafi"
"Barema basu da abinyi sai zaman kashe wando" baba isuhu ya dora sharhinsa,da hanzari
suka juya suka soma tafiya,saida suka bada 'yar tazara a tsakaninsu sannan suka fara gunguni
"Ba wani shege Allah,ke kuma zamu gamu,mu dake ne wallahi......ba wani waye waye" da kallo
ya bisu hannayensa xube a aljuhun wandonshi,idan ka tsirawa fuskarshi ido sosai qaramin
murmushi yake can qasan ranshi,saboda yadda suka nuna raki muraran da basu tsaya sunyi
zage zagen daura dashi ba,ya tabbata da sai sun gane kurensu.
"Allah ya saka maka da alkhairi kaji yaro....kubura maza hada kayanki ki wuce gida" baba
isuhu ya fada yana juyawa wajensa shima yana ci gaba da hada nashi kayan.
Cikin wani irin nauyi da taji jikinta yayi mata ta duqa tana ci gaba da tsince abinda zata
iya,saiya duqa shima a hankali yana tayata laluben farantai da cokulanta da suka nutse cikin
qasa.
Kusan ma ya fita lalubowa da yawa,hannunshi yayi futu futu da qasa fiye da nata,baice
komai ba ya taka wajen wata roba tata ya zuba cokulan ya ciro d'an tsumma daga aljihunsa
dayafi kama da handkherchief ya goge hannunshi sannan ya dauki botikin daya rage a wajen
ya saka robar a ciki ya rufe ya dauki botikin yayi gaba,bata gane me yake nufi ba amma saita
gaza tambayarsa saboda kwarjinin da yayi mata,binsa tqci gaba dayi wanda suna kaiwa
qarshen titin yadan ja ya tsaya,saita wuceshi tayi gaba,takunshi ta dinga ji alamun yana biye da
ita ne,saidai idan ba kaga sanda suka taho taren ba ba zaka ce tare suke ba.
Suna karyowa layinsu taji gabanta ya fadi sanda ta kalli gidansu
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" ta furta cikin zuciyarta,saboda tuna kalaman da ummanta ta
dinga fada kam mahaifinsu kafin fitarta da abincin sadaka,fatanta d'aya,Allah yasa zuciyar
umman ta sanyaya kafin dawowar mahaifinsu,matuqar bata sanyaya din ba Allah ne kawai
yasan iyakacin abinda zai faru yau a gidan nasu.
Wannan tunanin da kuma tunanin wanda ke biye da ita baquwar fuska ne a unguwar yasa
saura gida biyu ta qarasa qofar gidan nasu taja tunga ta tsaya ba tare data juya ba,tana jin
sanda ya qaraso gefanta ya aje mata botikin
"Duk sanda zaki taho ki dinga samun d'an rakiya namiji babba yana rakoki ya dawo dake" ya
furta cikin wata kwantacciyar murya data tafi da tunaninta cikin lokaci guda,ta lumshe ido tana
jin zuciyarta na qara yawan bugunta,bata motsa ba har sai data tabbatar ya bace daga layin
gana daya sannan ta sanya hannu ta dauki botikin nata,sai kuma taji haushin kanta ya
kamata,ko banza ya cancanci ta bude baki tayi masa godiya saboda taimakon da yayi mata ba
tare daya santa ko yasan daga ina ta fito ba,yanzun haka babu lallai ta sake ganinsa bare tayi
masa godiya,da wannan tunanin ta qarasa qofar gidansu,sai kuma fargabarta ta dawo sabuwa
sanda ta soma jiyo tashin murya daga cikin gidan nasu,dai dai sanda qanwarta mubina ta fito
hannunta dauke da 'yar tsana da kayan wasa na qasa wanda suka sha fentin pink da green,har
zata wuce abinta da gudu shahida ta cafko rigarta,saita tsaya tana duban shahidan
"Baba ya dawo?" Ta tambayeta tana fatan tace mata a'a,amma saita amsa mata da
"Eh ya dawo,yana qofar dakinsa ma suna fada da umma" ta bata amsa tana zame rigarta ta
sake sheqawa da gudu ta shige cikin yara 'yan uwanta ko a jikinta.
Jingina bayanta tayi a soron gidan nasu tana jin munanan lafuzan dake fitowa daga bakin
mahaifinta da mahaifiyarta suna jifan junansu dashi,wani qataton tashin hankali da take tsintar
kanta a ciki duk sanda ta riskesu a wannan halin ya rufto mata,saita sulale ta duqa a soron
tanajin ruwan bala'in dake tashi cikin gidan,wanda ta tabbatar zuwa yanzu dukka maqota kowa
ya kasa kunne ya diban rahoto,ta rasa wannan wacce irin masifa ce?,ta rasa meke haifar da irin
wannan gagarumin yaqi kulli yaumin tsakamin mahaifanta,basa kwana uku cur cikin jituwa da
juna,basa sati cikin salama da walwala,tunda ta taso tayi hankali haka ta rsiki rayuwarsu,babu
ragayya ko kad'an ga junansu,ba wanda ke ganin wani da gashi a tsakaninsu.
A qalla sun kusa awa guda suna wannan dauki ba dadin a tsakaninsu,wanda har zuwa
sannan hawaye baibar zuba a idanun shahida ba,tilas ta miqe da niyyar shiga ciki ko Allah
zaisa tayi nasarar dakatar dasu,duk da tasan cewa da wuya wai gurguwa da auren nesa,don
idan irin hakan ta faru dukkansu idanunsu rufewa yake basa ji basa gani.
Ilai kuwa yana zaune bakin rijiya yayin da da umman tata ke cikin kitchen,har ta qaraci
sallamarta babu wanda ya jita a cikinsu,hakan ya sanya ta dirr botikin ta durfafi dakinta ta bude
ta shige sannannta rufe qofar ruf waiko zata daina jin tashin munanan furucinsu,saidai bata
sauya zani ba,haka tq zame ta zquna gefan katifarta ta hade gwiwarta ta qanqame tana ci gaba
da kukanta.
Basu saurara ba har sai da khadija qanwar shahida ta biyu ta dawo daga gidan kitson da
umman ta turata da yunwa,tace umma yunwa amma bata bi ta kanta ba,hakam yasa ta watsar
da takalmanta ta zube dirshan wajen tahau ihun kuka,katsam sai farouq mai binta ya farka daga
baccin da yake shima ya hau tsala nashi kukan jin ba'a daukeshi ba akan kari,tilas baban nasu
ya suri takalminsa ya fice fuu badon sun gama ba,ita kuma tahau hidimar yaran tana yi tana
mita da alamun itama bata huce ba.
"Au,ita kuma wannan yaushe ta shigo tazo ta yasarwa da mutane botiki kan hanya salon
wani yaci karo dashi ya fadi,inama sauran botikan?" Jin hakan ya sanya shahida komawa
saman katifa ta kwanta luf tamkar mai bacci tana sauke ajiyar zuciya,hakan ya sanya koda
khadija da umman ta aikota tazo ta dubo shahidan tazo saita koma tace mata umma bacci take "Bacci?,bacci kuma da wannan yammacin?,k'nnnnn,to Allah yasa ba zazzabinne kuma ya dawo
ba" ta fada tana ci gaba da baiwa faruqu nono.
Takunta ne kawai ke kai kawo a idanunsa sanda yake komawa daga inda ya
rakota,idanunsa ya dinga lumshewa hakanan yanayinta da yanayin tafiyarta yaji ya
burgeshi,sanyinta,yanayin maganarta,da haka har ya qarasa wajen da suka baro dazun,yanzun
babu kowa,har malam isuhu ma ya wuce,kai tsaye ya wuce shagon balarabe mai saida kayan
provision,wanda dama tun asali wajensa yazo.
Hannu ya bawa bala sukayi musabaha,sannan ya zauna kan bencin dake aje daga cikin
shagon saboda custumers daya tarar yana sallama
"Ai na hangoka kaida wadan can yaran marasa kunya,yarinyar da babu sawa ba fitarwa,ina
Allah Allah naje na musu magana naga kaje,ai yarinyar kirkir ce,ba qaramin taimakon masu
sana'a a nan wajen take ba,kowa na yabonta"balarabe mai kanti yaci gaba da baiwa anwar
labarin zamanta a wajen duk da ba tambayarsa yayi ba,hakanan shima ya samu kansa da
saurarensa,duk da cewa bai tofa komai ba cikin zancan,har sai da balarabe ya gama
b'ab'atunsa yayi shuru
"Kana nufin kullum sai tazo nan kenan?" Anwar ya tambaya yana miqawa balarabe naira dari
biyu,yasa hannu yana amsa
"Qwarai kuwa,kullum tana zuwa daga qarfe uku na rana zuwa hudu,hudu tanayi ta gana
rabarwa ta hada kayanta sai tayi gida" baice uffan ba saiya maida akalar tunaninsa kan me xai
saya da d'ari biyun wanda zai riqeshi zuwa sanda zai sake samun wani kudin
"Me dame za'a baka malam anwaru" d'an tsaki yaja kad'an na alamun dawowa daga tunani
yana murza goshinsa
"Bani kwaki da suger"
"Kuma dai?" Kafadarsa ya dage yadan mari cinyarsa da tafin hannunsa
"To yq za'ayi,rayuwar kenan ai,wataran sai labari in sha Allah"
"Baka yarda ne anwaru....ni na yarda da amincinka,na yarda ka zabi abinda kakeso cikin
shagon na baka bashi kaje idan ka samu ka kawomin amma ka qiya" balarabe ya fada sanda
yake auna masa kwakin a baqar leda,dan miskilin murmushi anwar ya saki
"Idan ka bani naje na samo na kawo maka naji dadi gobe sake karba zanyi,idan kuma yauna
samu abun biyanka gobe fa ina dashi?"
"Ni a wajena ba wata matsala" kai ya kad'a
"A'ah,Allah ne kad'ai baya gajiyawa,amma yau da gobe dole dan adam ya gajiya" kai malam
balarabe yake kadawa,ya jima rabon da yaga matashi mai kishin kai kamar anwar din,matashin
daya dogara da kanshi bai rabu da kowa ba,ya yarda shi din ba kowa bane,ya kuma yarda da
talaucinsa ya kame kansa,yana gama auna masan ya miqa masa ya karba yayi masa sallama
ya wuce.
Muqulli ya ciro cikin aljihunsa ya saka ya bude qofar gidan,ya tura ya shiga,babu kowa cikin
gidan dama bai tsammaci ganin kowa din ba tunda yasan shi d'aya yake rayuwa a cikin
gidan,saidai ga mamakinsa gaba daya dakinsa daya fita ya barshi a akillace an bibbincike
masa,ya saba ganin hakan,yasan kuma bazai wuce samarin unguwa bane da suka kafa masa
qahon zuqa haka kawai ba,yasan baibar wani abu mai amfani da za'a dauka ba cikin
kayan,bama cikin kayan ba cikin gidanma gaba daya,aje ledar garinsa yayi ya duba agogon
dake maqale a bango,saura minti ashirin asha ruwa,yasan zai isheshi ya gyara wajen,mutum ne
da bayason qazanta ko kadan,a nutse ya gyara komai ya maida muhallinsa,sannan ya wuce
kitchen ya bude robar da yake aje plate da kofi ya dauko ya jiqa garin sannan ya sake fita ya
siyo pure water guda d'aya da naira goman data rage masa,yana shigowa soro aka sha ruwa,a
nan ya balle ya shanye,ya qarasa bakin fanfo ya daura alwala ya wuce masallaci.
*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI
SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*KO KUMA*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da
sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARINGν ½νΉν ΌνΏ½*
ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos[6/30, 10:46 AM] +234
814 691 0795: *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI
SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*KO KUMA*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da
sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARINGν ½νΉν ΌνΏ½*
ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½ν ½ν±ν ΌνΏ½
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos
*AA*
0οΈβ£5οΈβ£
Qarfe sha biyu na rana ta duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta,siririn tsaki taha
qasa qasa,tun daxun ake maimaita magana d'aya taqi ta qare,da d'ai da d'ai d'ai take qarewa
malaman dake zaune a office din shugaban makarantar ana tattauna taron da gobe ne za'a
gabatar a kuma rufe makarantar don tafiya hutun azumi,don tsarin makarantar ne basa karatu
cikin azumi,suna rufe makaranta ne azumi saura sati daya ,su dawo karatu bayan sallah da sati
biyu,caraf idanunsu suka hadu,saita janye tata qwayar idanun taja tsakin a sanda yake jifanta
da murmushi,malam