Showing 3001 words to 6000 words out of 64084 words
Chapter 2 - QURUCIYAR JUMMAI Hausa Novels By Halimatu Sadiya Muhammad.txt
talla..
Da yamma aka dafa mata kyada aka kasa a tirey..
Umma tace fito ki tafi..
Tace tau""domin tasan abunda ta shirya"
Tana fita, ta samu babban Leda ta juye gyadar duka a ciki..
Bata tsaya bin taka allawiya ba,domin tasan halin ta da bakar gulma""
Islamiyya ta nufa cikin sanyn jiki,mal.babba na ganin ta ya kama kunenta,ta kunne ya daga ta sama.
Yace sai yau kikaga daman zuwa makaranta?
Tace walahi sati na biu banda lfy, yanzu ma sadaka na kawo amin adu'a.
Saketa yayi,ya amshi ledar gyadan,yace shiga aji ayi adu'ar dake.
An tashi islamiyya ne, tana tafe tana waqa""as usual""
Amma wanan na islamiyya ne,kamar haka; al karimu mai girma Allah shi kadai,shi yakan bamu rai,shi yakan dauki rai
Zana Baku labari yan uwana kuji gidan wuta da aljannah zabi zakuyi,wanda yabi aljannah shine mumini,Wanda yaqi aljannah shine kafuri.
Daren wuya daren nadama, daren da bawa yakan yi kuka,in na tuna kwanciyar qiyama,zuciyata takan yi sanyi,ba uwa can, ba uba can,ba abokin gudu da tsira,in kayi hairan, ka iske hairan, in kayi sharan ka iske sharan..
Tataro muje fatimatu,tataro muje matabata,ba gidan mune ba duniya,ba gidan mune ba gidan aro,anyi duniya domin wa, anyi duniya domin annabi muhammadu(S A W)gashi ya bada baya yabar wasu, wasu su bada baya subar wasu, muma mu bada baya mubar wasu...
In babu tsarki babu alwala,in babu alwala babu sallah,in babu sallah babu addini mutum dashi da dabba babu bambanci.......
Har ta isa gida, umma tace gidan uban wa kika kai min gyada?
Tace sadaka nayi dashi a islamiyya...
Tace yau sai na maki bulalan naira Dari na,duk wanda yamaki tsaya...
Haka ta rinka rabe rabe har Baban su ya dawo sallar isha'i
Yace auta lfy?
Ta fada mashi yadda sukayi da umma.
Yace ke saratu(umma)ya akayi kamar Yar yarinyar nan ki daura mata talla?
Tace na gaji da ganinta haka kullum sai gantali cikin unguwa, sanan yau sai na mata dukar kudina
Yace nawa ne kudin?
Tace duk kwanun gyada naira talatin, kwanu uku, leda naira goma,itace naira ashirin.
Yace ga naira Dari shike nan ko?
Tace bai hana gobe in daura maki wan..
Zama tayi a dakin Baban su,sukaci abinci""faten dankalin hausa da wake ne""
Umma gidansu allawiya ta shiga, taba maman allawiya lbr abunda jummai ta mata.
Tace ga shawara mai zai hana ki dafa mata doya da yajin kuli,yanka naira goma, tunda doyar nada saukin kudi,kuma bata cin doya.
Ni kuma zan rinka dafama allawiya shinkafa da wake da mai da yaji, su zauna nan bakin titi, yan cirani zasu saya tunda babu masu abinci....
UMMA TACE HAKA ZA AYI.
*TAU YA KUKE GANIN ZATA KASAN CE JUMMAI DA ALLAWIYA WURI GUDA DA SUNAN TALLA*?
*ku biyo ni muje zuwa*
*L££MA*π
[08/01, 21:41] βͺ+234 812 140 7930β¬: πΈπΈπΈπΈπΈπΈ
π·π·π·π·π·π·
*QURUCIYAR JUMMAI*
π·π·π·π·π·π·
πΈπΈπΈπΈπΈπΈ
*HALIMATU SADIYA MUHAMMAD*
*L££MA*π
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION*πβπ»
*7-8*
Ranar Monday ko wanka jummai bata tsaya yi ba,ta kama hanyar makaranta,bata biya ma allawiya ba yau.
Front sit ta zauna, ta aza Jakarta saman desk,yadda duk wanda ya shigo zai gani..
Class din ya fara cika,duk wanda ya shigo bai bita kan jakar""kasancewar government schl ne kuma primary most of the children basu iya karatu ba,sanan diyar babban mutum CE,ba kowa yasan ta ba,domin ko su jumman basu taba ganinta ba sai a hoton jakar""'
English teacher ya shigo, duk suka mike..
Gud morning sir.
Yace morng,get sitted.
Wari ne yaji ya cika class din.
Yace what is smelling?
Kowa yayi tsuru tsuru
Koda ya matso kusa da jakar jummai,ya taushe hanci,
Yace ma jummai; why did u pollut the class.
Tace bani bace
Yace speak English
Ta rasa yadda rata yi,domin tana jin abunda yafe gadi,amma bata Iya mayar wa.
Ko da yayi checking bag din, ya fita da take away habba wari kamar mushe..
Tace ka bani abinci na,dama shi kake son ci tunda kaga daga gidan masu kudi ya fito.
Ko kallon ta bai yi ba ya fita dashi wake.
Allawiya na can daga baya sai dariya ta ke yi
Tun daga ranar duk inda taga English master sai tace ma yara ai Barawo ne,daga gidan masu kudi aka bata abinci tazo dashi makaranta ya dauke.
Sai da rana guda ya zanne mata jiki, sanan ta Shafa masa lfy.
Yau koda suka dawo daga schl an dafa ma jummai doya, allawiya kuma shinkafa.
Bayan ta tube uniform, taci abinci..
Umma tace yi sallah ki dauki doyar ki tafi.
Fita tayi kofar gida tace walahi umma ban zuwa tallan doya haka kawai ana zaune lfy...
Umma tace kada ki bari a kama min ke.
Tace sai dai ki kashe ni walahi banyi.
Kama hanya tayi zuwa gidansu allawiya,can ma ta iske Maman allawiya na fama da ita ta dauki tallan.
Magana tayi ma allawiya a kunne,suka taba, ai nan da nan suka sheka a guje..
Mama na ina zaku,ko kallo bata ishe su ba.
Basu tsaya ko ina ba sai bakin gate na siyona church,bukin engagement akeyi na yan church din.
Ga abinci iri, iri sai police band dake tashi.
Serving Kansu suka yi,sai da suka koshi,jummai ta fara dikar rawa,sai daf da magrib aka tashi..
Suna tafia ta ga wata tsohuwa zaune kofar gida, jummai tace hajia mai dawa mayya
Matar tace shegen yaro ,Allah tsine uwaka.
Jummai tace sai dai uwarki tsohuwar mayya.
Ta sheka,allawiya na biye da ita.
A gida kuwa, bayan sun gudu ne Aysha ta dawo daga tallan dafafan masara,umma ke fada mata yadda sukayi.
Tace kema umma da nacii kike,jummai har guda nawa take da zaki na daura mata talla,wadda babu komi cikin kwakwalwarta sai zallar quruciya.
Umma tace idan ba haka na mata ba,bara tabar yawace yawacen banzar nan ba.
Tace dan Allah umma kibar biyewa zugar mutane akan jummai,ni dinan na isa in maki duk tallan da kike so.
Yanzu bara nayi sallah na dauki doyar zuwa tasha baa rasa masu saya ba.
Umma tace Allah maki albarka,ita kuma ya shiryata.
Amin umma
Oh Aysha yanzu shike nan bakya da hutu; da asuba kije islammiya,ki dawo kije boko, idan kin daw kije talla,da dare ma talla,ko yaushe Zaki samu lkacin kan ki?
Muryan baba sukaji yana fadin sai ranar da kika dena daura mata talla.
Yace Saratu ban San me kike so ki zama ba,Iya gwargwado ina quqari a kan Ku,amma bakya gani sai kin bata min tarbiyar yara,su kenan Allah ya raya mana, haba Saratu.
Ba inda Zata talla walahi.
Ya juya fuuuu.
Tace Aysha aje maci gobe, je kiyi sallah isha'i ki tafi islamiyyar dare, tunda ja'irar yarinyar nan taqi dawo wa.
Da su jummai suka dawo gida, baba ya hana umma dukan jummai dole ta kyale ta
Allawiya kam tasha duka wurin yaya nafi'u.
Washe gari su jummai na zaune a class suna hira
""Da yake sun kusa fara common entrance exams na shiga secondary schl.
Jummai tace ko yaushe zamu gama makaranta har muyi aure gashi ance tashin alqiyama ya kusa.
Wata daga cikinsu,wadda duk ta fisu girma, tace nikam aure zanyi da mun gama exams.
Allawiya tace lalai lauratu ZAKI zama Yar iska kenan.
Tace dallah Ku yarane Baku San komi ba.
Bayan sun koma gida,umma tace anshi sayo kuka gidan Maman bello saura ki tsaya wasa..
Tana tafe tana rera waqa bata Masan takai kofar gidan sale ba,Ji tayi an turata cikin gida an rufe gate.
Tace lfy mallam?
Yace yau zan rama iskancin da kika min ranar, mazza tube rigarki ki cire wando, bani kike kira kwarto ba?
*L££MA*π
[13/01, 19:59] βͺ+234 812 140 7930β¬: πΈπΈπΈπΈπΈπΈ
π·π·π·π·π·π·
*QURUCIYAR JUMMAI*
π·π·π·π·π·π·
πΈπΈπΈπΈπΈπΈ
*HALIMATU SADIYA MUHAMMAD*
*L££MA*π
*@AM££NCI WRITERS ASSOCIATION*πβπ»
*INA masoyyan jummai wanan shafin naku ne,kuyi duk yadda kuke so dashi*
*gaskia nayi farin cikin sosai yadda littafin nan ya samu karbuwa*
*nagode da adu'ar Ku masoya Allah yabar kauna*
*9-10*
Shekewa da wani mahaukcin daria tayi.
Tace Ji yadda kake tadda jijiyoyin kai,kana wani zazare idanu kamar tsohun maye.
Yanzu baka Ji kunya ba?
Kamata Yar kankanuwar yarinya kake cema tube riga tube wandu,kamar wadda ya samu wata uwar mata.
Idan na tube me zaka min?
A haihuwar kaji dai ka haifi iri na.
Kuma ance maka kwarto ko karya nayi?
Almaqashi ta dauka,na rantse da Allah idan baka bude min gate na wuce ba,sai na yanke gindin nan,sanan in Tara maka jama'a,in qala maka sharrin da har ka mutu bara ka mance da Jummai ba.
Sum sum ya dauki key ya bude mata gate.
Tace zaka San kayi da mai yi,MU zuba shege ka fasa dan halak sai yanka,TTA wuce abinta hankali kwance.
Tana fita ta sheqa @360,tace Allah na gode maka da kayi in mai baki, nasan da shegiyar can ne mai shegen tsoro kamar farar kura da yanzu ya gama da ita(Aysha).
Data dawo gida umma ke fada masu ai fati na nan zuwa idan sun samu hutu.
"Fati diyar kaunan umma ce daga kauyen mahuta dake kebbi state zata zo,warin jummai CE.
Murna jummai tayi""domin akwai ta da son baki ko din ta basu labarin yan anguwarsu.
Yanzu Aysha bata zuwa talla,sai gashin masara from 8:00pm to 10:00pm.
Idan ta daw schl tayi aikin gida,da yamma taje islammiya.
Jummai kam sai abunda ya qaru na rashin jin ta,islammiya bata zuwa,idan an turata ta wuce wurin wasa,schl din ma sai taga dama.
"Da yake irin gifted child din nan ne,da an koya mata ABU ko sau guda ne ya shiga kanta kenan, ko bata class akayi data amsa BUK din yan class diny ta duba ya zauna kenan,Dan tun tana primary 3 ta iya reading both English a and Hausa, ga hand writing mai kyau sai dai bata copying note, tana jin turanci amma bata iya Mayar wa, duk da haka ita ke daukan 1st KO 2nd position a class din.
Su allawiya kam in banda tsabar satar amsa babu abinda ta iya, sai karatun Hausa,idan kaga taci exams sit guda suka zauna a jummai.
Shi yasa da fada ya hada ka da jummai sai tace duk baka kyaleta ba bara ta baka amsa ba,ko tana son abinka sai tace ka bata, ta baka amsa.
Anyi lokacin da jummai ke sayar da amsa, idan maths and English exams ne, 50 naira each raka biya ta amsa ta rubuta maka, sauran subject din 20 naira each.idan ta taraa kudinta,ta sayo;awara,taliyar fulawa,dawake,gulisuwa,tuwon madara da sauran su.........
Sun fara common entrance exams a sa'a,da yace oral exams ne.
Bayan sun qare ne,suka rabu cikin kewar juna.
Yanzu kam jummai an samu freedom, ba boko,ba islammiya,sai bakar yawo.
Da dare tace su rabe Ku zo muje wurin
Ubale mai kanti dibar madara sukace whhhh muje.
Shago ne babba NA kayan masarufi,mutane ne makil sunata sayan kaya, kasan cewa kayanshi Nada saukin kudi..
Su jummai na isa suka qusa cikin mutane da babban ledar su, su dumbuji madara su zuba, su dunbuji milo su zuba su dumbuji sugar su zuba..
Wani inyamuri ne yazo sayan maganin sauro ya hankalta dash.
Yace hey Hausa pikin na wa for u
U don get promotion be dat
Frm beggin to thieving people property.
Sha una all desame,all of una na hausa ube,how it take worry me?
Jummai tace na me be thief?
I will put zakafi for u now now.
Yace idiot,shege banza,dan iska..
Ta fara waqa;
LA la la lala
La lala
Kwadon ubanka ya tsinke
Saura qashi da dan tsoka.
Yara Ku zo Ku sai nama.
La'anane dan wuta
Suka amsa:
Kafuri
Mai futsari a tsaye
Kafuri...
Hasarare
Kafuri....
Abishi da go ra har wuta...
Ya dauki kata ko ya bisu da gudu
Suka sheka..
Jummai tace kuje gida kuyi bacci,mamar wasa ma yau bacci take Ji.
Audu yace jummai a raba madarar mana
Tace wanan kayan ba namu bane
Allawiya tace na wage?
Jummai tace baquwar mu
Gobe rata zo daga kauye, kunga bai yuwuwa ta baro kunnu can, tazo birni taci gaba da shan kunnu,sai ta rai na ma gidan mu da wayyau.
Suka ce ba matsala.
Tun da safe jummai ta share dan madai dai cin gidan su tayi goge goge""duk da ba wani abuna azo a gani ke gare suba.
Wanka tayi,taci kwaliya
Tea tahada mai kauri, ta rufe a cikin jug.
Tace ina ki ka samu kayan tea?
Tace wurin ubale,kuma babu mai sha domin na baquwa ne.
Umma tace abincin sata raki ba baquwar?
Aysha tace wada zata Taso tun daga kebbi state zuwa niger state(minna) aka hadawa tea tun yanzu?
Babu ruwan ki,kuma yau ban zuwa ko ina sai tata iso tasha tea nan.
Aysha tace umma na wuce islamiyya.
Tace a daw lfy.
Yan wasa sunyita sallama ma jummai, amma ta fau taqi fita.
Sai da la'asar fati ta iso, da yake tasan gida kuma babu nisa da tasha, ta karaso da Yar Ghana most go nta kodade.
Jummai najin sallaman ta, ai a guje tayi hanyar zaure, amsar jakar hanunta tayi sannu fati, shigo ciki.
Umma sai murmushi take yi
Zama tayi saman yagagen Leda carpet dake palour su jummai.
Jug din tea ta kaw mata da cup.
Umma dai kwanu mai marfi ta bata""faten tsakin masara ne na manja, yaji sure da kyada""
Jummai ta jaye kwanun gefe, tace bashi ZAKI Ciba dan shi kika bari kauye, ga dai shayi nan.
Ai ko ta kafa kai sai data shanye shayi tas, ta kuma shanye fate.
Jummai tace taf wayaga na kauye a birni.
Aysha ta daw isllamiyya,tace ah su fatin dai, yasu gwaggo?
Tace lfy lau.
Ina tsaraba?
Jummai tayi caraf, yan kauye kika San suna kaw tsaraba ko son banza sun fiki,umma ce dama idan zata ta daukar ma kanta qalulan wahala,ayi tsaraba niqi niqi.
Fati dai na sauraran cin mutunci da ake masu..
Da safe masa umma ta aika aka saya ma fati, jummai tace alambaran sai dai fati tasha tea,dan akwai masa kauye.
Fati kam a dadin ta duka biu ta hada.
Da yan maa jummai taja fati, wai zata zaga da ita taga gari.
Daga gidan su allawiya aka fara
Tace kin gidan babban aminiyata wadda tazo jiya, duk da gidan haya suke, amma dadi suke ci.
Tace uhm.
Tace nan gidan mai bredi ne,kin san yarbawa qazamai ne, katti kee kwabin flour zindir ba riga duk zufan hammatan su na zuba cikin bredi shi yasa kullum yake kwantai yadda masarar umma ke kwantai..
Tace muje layin baya, in banda kwasar daria babu abinda fati keyi.
Gidajen nan uku na masifafun unguwar nan ne,tsofai tsofai dasu; Hajia ibra, hajia mai dawa da Hajia taya haka suke kamar mayyu.
Fati tace tab.
Nan kuma gidan zuriar duwayu kenan,.manyan su a yara duk babban duwayu ke gare su.
Suka sheqe da daria.
Nan kuma gidan yan'aljannah duk unguwar nan babu Wanda ya kai su kirki,basu fada da kowa zattausayi, bayin Allah.
Ga gidan mamar murtala, tsuyaya ce, sai mugun son kudi.
Wai kamar ruwan rijiya mtar nan sayar wa take lokacin rani duk bokiti naira goma,tsinaniyar har da kirari akai mata
Money ya dey
Money ya kam.lol
Fati tace ban jin turanci ai, tace duk kanwar ja ce inji jummai.
Tace nan kuma gidan shehu lalura kenan, duk unguwar nan yafi kowa kiran babu, ga cin bashin tsiya,matan shi kuma badai qazanta ba"kin san halin matan hausa wa musamman sakwatawa"
Yauwa ga islamyyan MU
Azaluman biu ne,mal.Babba da malama hadiza.
Ita mallama hadiza ina mata uzuri sabida bata San zafin haihuwa ba, tunda bata taba haihuwar ba.
Shi kuma Mallam babba ma gemun bunsuru, basamude ne daga Yemen ya gudo nigeria,shine aka danka mai makaranta.
Jifa sukaji na duwatsu ta ko ina...
*L££MA*π
πΈπΈπΈπΈπΈπΈ
π·π·π·π·π·π·
*QURUCIYAR JUMMAI*
π·π·π·π·π·π·
πΈπΈπΈπΈπΈπΈ
*HALIMATU SADIYA MUHAMMAD*
*L££MA*π
*@AM££NCI WRITERS ASSOCIATION*πβπ»
*domin samun littafan mu a Facebook @AM££NCI NOVEL GROUP*
*INA NEMAN AFUWAN KU AKAN JINA DA KUKA YI SHIRU KWANA BIU,I WAS VERY OCCUPIED NE SAI KUN YITA HAKURI DANI YANZU*
*11-12*
Wa zata gani?
Dan lami gwangwanin alala...
Tace MU gudu fati mahukaci ne,zai halaka mu, ai kuwa sheka wa su kai sai gida...
Baba dake zaune bisa tabarma a kofar dakin shi,yace ya ya,lfy kun shigo a guje?
Tace baba dan lami ya biyo MU da jifa.
Umma tace me ya kai Ku har bagadaza.
Tace naje nuna mata gari ne AI.
Tace da ya fashe maku kai taga garin da kyau AI,fati wuce ki huta dama ita bata gajia yawo.
Haka fati tayi hutun ta cikin fari ciki da anashu wa.
Data tashi koma wa sha tara na arziki su umma su kai mata.
Common entrance ya fito.
Jummai ta samu admission a""government technical schl minna""makarantar su Aysha,domin yanzu jss3 take.
School din bai da nisa da gidan su.
Alawiyya ma nan ta samu.
Ranar monday suka fara zuwa,jummai baayi Mata uniform ba,tsohon na Aysha tayi amfani dashi,dan basu da hali.
Alawiyya komi sabo aka yi mata,kuma Baban ta ya kai ta.
Jummai kam ita takai kanta,tana isa an gama Assembly har an fara tsaran latti""prefect""
Fuske wa tayi zata wuce, wani dan ss3 yace ''hey where did think u are going.
Kneel down my Friend.
Murguda baki tayi, tai tafiyar ta.
Class din da aka rubuta jss1A ta shiga, makil yake da students, Layin baya ta zauna sit din da allawiya ke zaune.
Maths teacher ya shigo.
Aka mike
Good morning sir,banda jummai,tace iskan cin banza,primary gud mrng sir, secondary gud mrng sir,aikin wahala.
Yace get sitted..
Let me introduce myself.
Am Muhammad Raji by name""popularly known as M.Raji"", I will be teaching u mathematics.
Ya rubuta topic;-Roman figures
Yace bring out yr writing materials.
Kowa ya fitar da book,calculator and mathematical set,amma banda jummai domin ko book bata dashi.
Baba yace tayi hakuri har second term ta fara zuwa, dan bai da kudi yanzu,tace atafau sai ta fara zuwa.
Ya rubuta example:-Roman figure 1 to 100 ya rubuta, yayi baya sanan yace suyi copying.
Ya fara going round, yana observing student din,jummai ya han go zaune tana faman gyangyadi.
Desk din ta ya buga,firgita tayi,ta mike tsaye.
Yace what's wrong with u?
Tayi shiru zata zauna.
Yace keep standing.
Why are u not writting?
Tace, takadata na wurin yaya ta.
Yace speak English, u are no more in primary schl.
Where is yr sister?
Tace jss3A
Yace call her for me.
Ya fita sai ajin su Aisha, tace M.Raji na kiran ki.
Sai da gaban ta ya fadi domin duk schl din babu Wanda vai sai halin shi ba.
Suna zuwa, ya tamvayi Aysha ya suke da jummai?
Tace sister tace.
Yace ya sunan ta.
Tace MARYAM SALIS.
JUMMAI tace nima popularly known as JUMMAI.
Yace shut up,who ask u.
Yace Aysha salis she told me that her writting materials are with u?
Tace she did not give me anything sir.
Yace ma jummai why did u lie to me?
Tayi tsuru tsuru dan kuwa karyan ta shirga.
Yace Aysha salis go back to yr class.
Yace Maryam salis start frog jump from here to the staff room 10x.
Zama tayi a qasa tace walahi banyi, mugun banza daga zuwa na yau yau, Ashe haka secondary yake?
Ai gara ma a mai dani primary.
Bayan makaranta ta zaga ta haye itacen mango, ta cika riga da danyun mango.
Security ya hango ta saman itace, yayi yayi ta saura taqi, principal ya fada ma
Tace yaje ya samu social master ya fadi mashi, bata Iya harkan kana nan yaran nan.
Yana class baba mai gadi ya sallama Mai.
Yace ina kwana baba
Yace lfy lau M.Raji,ya fada mashi abunda ya faru, yace muje in gani.
Suna zuwa ya sake baki da mamaki.
Yace shin ba yarin Yar nan naba punishment yanzu ba?
Yayi juyin duniya ta sauko.
Tace sai ya rantse bazai mata komi ba.
Yace walahi, walahi walahi sai kinyi punishment, sanan kibar makarantar nan.
Ya aika aka kira Aysha, yace dama sister nan taki nada tabin hankali
Tace sir