Showing 90001 words to 93000 words out of 126557 words

Chapter 31 - MIJIN MALAMA Book 2 Complete by Nimcey Sarauta .txt

lissafi yake ko yana ƙarami idan yaci yaji ya dinga hawaye yana zaro tongue yana "Mami pepper, Mami my tongue zai cire" Har wasu ƙananun guraje ke fito masa, ya zubawa abincin idanu ganin rice ɗin ta ɗan yi wani colour gwanin sha'awa ya sanya ya ɗauki spoon, tare da yin bismillah ya sanya a baki, da wani kalar sauri ya cillar da spoon ɗin, wani zufa na yanko masa jikinsa ya ɗauki rawa da ɓari, idanunsa sukai jajur suka fito waje saboda azaba, babu wanda ya fahimta, gashi ya kasa magana sai fito da harshe yake yana dunƙule hannu wata kalar gigitacciyar azaba yake ji tun daga kan yatsar ƙafarsa har zuwa tsakiyar kansa, yana jin har wani tiririn azaba yake ji na fita daga kansa, idanunsa suna ƙanƙancewa tunda yake bai taɓa jin abu makamancin haka ba, shi yasa ba abincin kowa yake ci ba, a hankali ya kifa kansa a dinning ɗin jikinsa duka ya jiƙe sharkaf da wata kyakkyawar zufa wacce tsananin azaba da gigicewa ya fiddo da ita, numfashinsa ya fara sarƙewa tsakiyar ƙirjinsa na masa zafi zafi da zugi, Mai martaba Ajlaal Sultaan da Zaytoon magana suke a hankali hakan ya sanya gabaɗaya basu farga ba, Roohan waya yake dannawa Ƙhulud kuma abincinta kawai take ci, zaton su kuma Gimbiya na sashin ta, Daidai nan majeederh ta fito ƙamshinta a kullum dake alamtawa zuciyarsa zuwanta shi ɗin ne a yanzu ya sanar da shi, ya miƙe da ƙyar jiki na ƙyarma Jee ta ce "Granny ga fresh milk ɗin...," Bata ƙarasa ba ta ji an damƙota hanka ya jawo hankalin jama'ar wajan. "Khalil lafiya?" Cewar Zaytoon amma ina babu bakin magana Jee dake ƙoƙarin yi masa magana taga ya yi sauri a gaggauce cike da neman ɗaukin jin harshen shi zai tsinke da wani fitinannan wahalallan yanayi ya haɗe bakinsu waje guda...
[14/09, 7:43 am] Sdy Auwal Gstc: *_Nimcyluv sarauta 86_*
Da sauri Zaytoon ta sunkuyar da kanta ƙasa, Mai martaba Ajlaal ya yi kamar bai san meke faruwa a wajan ba, Ƙhulud dai murmushi tayi tana cigaba da cin abicinta a nutse. Roohan da yake shirye da makancewar Idanu ya zuba musu idanu,domin a duniya yana son labaran Soyayya da duk abinda ya shafi “Love”Shi kuwa Khalil wata kyakkyawar ajjiyar zuciya ya sauke ta cikin bakin jee lokacin da harshen shi ya samu gurbi cikin bakin nata, sanyin daya ratsa tongue ɗin ya sassauta rawar da naman jikinsa ke yi har yanzu zufa ce ke yankowa a jikinsa, fuskarsa tana sauka a fuskar Jee, yadda ya riƙe fuskarta da kyau yana sake shigar da ita jikinsa tana jin yadda fatar jikinsa ta ɗauki wani zafi, sanyi yana ratsa jikinsa, kai tsaye ta fahimci abinda ya haddasa masa kiɗima da gigicewar daya sanya ya manta su waye a wajan, ta kansa kawai yake da neman inda zai samu sassauci da sauƙin azabar dake ratsa harshen nasa, wata fitinanniyyar sahirtacciyar sumbata yake sauke mata a gaggauce ce, cikin yanayi na samun nutsuwa yana ƙara riƙe zagayayyiyar fuskarta a hannunsa, tare da shigar da ita jikinsa. Fahimtar halin da yake ciki da zafin yaji ya sanya Majeederh ita kanta mantawa da abinda ya kawota da kuma wadanda suke wajan, a nutse ta shiga rage masa zafin yajin ta hanyar sucking ɗin tongue ɗin a sanyaye in a romantic style, tana zuba yatsun hannunta cikin kansa tare da nutsa su slowly slowly take hargitsa sumar kansa, while still kissing his tongue, ajjiyar zuciya ya shiga saukewa feeling relieved na pain ɗin da yake ji, Zaytoon ce ta fara miƙewa ta bar wajan sukuku, Mai martaba Ajlaal tuni ya kama hannun matarsa sun yi turakar shi domin ya jima da barin cikin fada, Roohan ne zaune kawai yana son yaga inda al'amarin sai tsaya, daga taimako al'amarin ya rikiɗe jee ta zame fuskarta tana ƙasa da murya ta ce "Ya harshen?" Ya kwaɓe mata fuska a ɗan marairaice yana kwantar da kansa a wuyanta daidai kunnenta sai da tayi da gaske kafin ta ji ya ce "Ba sauƙi, i need more" Ta hararesa ya kashe mata idanu, ya rungumeta sosai a tsakiyar ƙirjinsa a hankali ya furta "I love you Madam" Ya faɗa a tausashe har yanzu idanunsa jajur amma a wannan karan ba wai na zafin bane, itama ta ɗaga masa gira ta ce "Abincin fa?" Ya girgiza kai yana taɓe baki alamar baya so, a hankali ta ce "I can cook you a non-spicy meal now" Ya zuba mata narkakkun idanunsa wanda suke da zallar buƙatar ta a fili, sarai ta gane ta share ta fahimci Khalil tunda ya yi aure ya rage cin abinci, ta saka hannu ta mintsine shi ta ce "What?" Ya rungume ƙugunta ya ce "I was just thinking" Ta ce "of? Ya cire hannunsa ya nuna mata saitin ƙirjinsa, kana ya nuna mata alamar love da hannu, ta girgiza kai irin bata gane ba.
Ya saketa ya ɗan yi baya da ɗan ƙarfi kuma ya ce "I don't know why I love you, I just know that I'll love you forever" Roohan ya yi saurin ɗakko iphone ɗinsa ya danna play na vedio, yana lumshe idanunsa wlh ji yake ina ma shi ne Khalil, Majeederh ta rufe bakinta tare da juyawa ta nufi Khalil da nufin rufe masa baki, ya zille ya yi wajan yana mata murmushi idanunsa a jirkice kamar mai nuna mata wani saƙwanni a cikin su. A hankali ya furta "I love you, i love u so much Hawwa'u means a lot and everything to me wife" Tashin hankalin Majeederh ganin wani ruwa ƙwance a idanun Khalil, a hankali kuma ruwan ya ziraro kafin ya sauka tayi saurin tara tafin hannunta ruwan ya sauka, a tsorace a firgice kuma ta kalli Khalil ganin da gaske hawaye ne ke sauka, wahala bata taba saka Khalil kuka balle farin ciki Ya Allah! What is happening to him? What's bothering him?.
“I don’t want to live without you for even a single day. You’re the best thing that ever happened to me, and I’ll cherish you in my heart forever!” Ya furta a hankali tears running down his cheeks, da wani kyakkyawan tashin hankalin daya rikito mata tare da lulluɓe ta, ya sanya mata wani shakku da wani gajiyayyen tsoro a ƙofofin zuciyarta take kallon Khalil, bata gama zullumin abun ba sai da taga sabuwar reza a hannunsa kafin ta ƙarasa tuni ya ɓalle rigarsa daidai tsakiyar ƙirjinsa da rezor ɗin ya rubuta harafin _M_ jini ya fara zuba abinka da lafiyayyen mutum, da wani irin gudu ta ƙarasa wajansa ta rungume shi tana kuka ta ce "And what is this pls my poor darling husband?" Ya yi mata murmushi yana ɗaga girar shi ya ce "Madam" Ya furta underneath his breathe. Ganin yadda jinin ke zuba ya sanya Majeederh ɗora lip's ɗinsa a wajan ta goge tas da shi a hankali ta furta "why are u doubting? Baka yarda ni taka bace?" Ya yi mata shiru ya kama hannunta ya damƙe da nasa hannun yana riƙe da fuskarta ya ce “Take my heart, my love, and my soul. You are my other half, and I can’t imagine life without you. I love you with all that I am!" A hankali muryarsa na ɗan rawa kamar zai fashe mata da kuka ya ce "Don Allah, don Allah don Allah don't ever leave me" Ta girgiza masa kai, jikinta na ƙyarma ɓari da wani kalar makyarkyata ya ce
“Each time I’m with you, nothing else matters because you’re all that matters to me. I love you with all my heart, baby.”


Ƙoƙarin kawo ƙarshen maganar take ta hanyar ɗaga masa hannu ta ce "Ok, Ohk i understood! Ka bar wannan maganar if you have something to do, je ka yi, Khalil stop ban so ban son jin anything" Roohan dake gefe idanunsa ya yi caɓa-caɓa da hawaye hadda Majina a hankali ya ce "Ohh my future wife kina ina? Nazo na sameki"
Khalil ya yi mata dariya yana mata gwalo while hawaye bai bar fuskarsa ba, ya furta "Sometimes the worries overwhelm me. I fall into a pit of darkness and confusion. You are the only one that can pull me out of it. I need you to be there through my rough patches, because without you I am lost. Please don’t forget me Ƴar Madara" Majeederh ta fashe da kuka ta faɗa kansa suka haɗu suka faɗa saman lafiyayyen saman turkey grass carpet ɗin wajansa, ta shiga dukan ƙirjinsa tana kuka sosai yana mata dariya yana kuka shi ma ya matseta a jikinsa da wani mahaukacin ƙarfi ya ce "Don’t forget me, I have not forgotten you. Remember our life, our romance, our love…I could never forget you, and I could never stop thinking about you. You have invaded my mind and captured my heart. Your absence from my life is the only thing that will ever keep me from thinking about you every single day. No matter where in the world we are, as long as we are breathing, I will always love you.....," Bata bashi damar ƙarasa maganar ba tayi saurin haɗe bakinsu waje guda ta shiga yi masa wata ƙyakƙyawar sumbata wacce bata taɓa yi ba, Khalil ya matseta yana sauke ajjiyar zuciya da sauri kuma ya miƙe da ita yana tangaɗi ya nufi wani lafiyayyen sashe da aka basu a cikin Palace ɗin. Cikin dare Khalil ya ɗauki wata farar Luggage Bag ya saka komai nasa, a hankali yake komai baya son making any mistake da zai sanya ta farka daga bacci, musamman da yaga baccin ya mata daɗi duk da ta wahala sosai har sai da mararta ta amsa, ya ɗauki jotter da pen ya ɗan yi short note ya ajjiye a gefen pillow, a hankali kuma ya sunkuya ya shafa cikinta daya fara girma, yana jin motsin unborn ɗinsa, ya yi kissing jikinsa a hankali ya ce "Take care of your mom, i love u child" Ya yi pecking lip's ɗinta ji yake kamar shekara shi fa zai yi, tunda suka samu fahimta bai taɓa kwana ɗaya ba tare da ita ba, ya miƙe a hankali tare da ficewa da sauri ya yi baya ganin Mai martaba Ajlaal hakimce a main parlour hannunsa riƙe da black tea yana sha, daman ɗabi'ar shi ce fitowar dare. Khalil ya rasa yadda zai yi sai kawai ya juya ya haura window tare da dirk'a cike da kulawa ba tare da fahimtar, fadawa da sauran maids na Palace ɗin ba ya fice kai tsaye kuma airport ya nufa daga nan sai Pakistan.


Pakistan,Peshawar.
Ddmaster bom na zaune hakimce wata kyakkyawar budurwa mai kimanin shekaru 20 a kusa dashi, fara ce tas mai sanyin kyau idanunta blue ne kamar na mage, ba imani akan fuskarta ko kaɗan, amma abun mamaki bata fiya damuwa da ƙananun kaya ba. A hankali ta ce "Na fahimta Oga" Ddmaster bom ya ce "Za mu yi baƙo, ba baƙon alheri bane, daga hukumar NAPTIP aka turo shi da niyyar siyan kaya, idan yazo zai kasheni tare dake ya kuma tafi Nigeria da gawarwakinmu do you want that to happen?" Ta ɗan ya mutsa fuska ya ce "Good, zaki je matsayin ke ce wacce zaki bashi kayan ni kuma ina mota ina kallo, ki yaudare shi" Ta watsa Idanu ta ce "How? Tayaya?" Ya ce "Mu raunata masa zuciya, rauni na har abada Clara, na faɗa miki daman na daɗe ina tagging nasa remember?" Clara ta ɗan yi shiru sai ta watsa hannu ya ce "Yaron nada fikira idan muka same shi matsayin ɗan tawagar mu i am sure it will be our success" A hankali ya ce "Debaka died" Ta ce "Na sani, amma har lokacin bata yi masa allurar ba?" Ddmaster bom ya ce "Ta ci amana ne, ai babu soyayya a tsarinmu son da take masa yasa ta kasa masa allurar duk lokacin data ɓata, zata tona mini asiri kawai na danna ƙaramin bom ɗin jikinta, itama bata san da shi ba, yanzu mahaifiyar yaron tana hannunmu, zaki tafi da ita yana yin wani kuskure ki yanka mata wuya, shi kuma idan ya yarda ta rayu kiyi masa allurar guba a jikinsa, mu kaɗai muka san maganinta adadin lokacin data ke ɗauka awa biyar ne daga nan mutum zai mutu, idan kuma mun yi masa magani to zai manta komai sai mu abinda muka gindaya masa kawai zai bi understood?" Clara ta ce "Sure" Ta ce "Taya zan gane shi?" Ddmaster bom ya nuna mata photon Khalil ta jima tana kallon Idanun Khalil kana ta ɗauke kai ya ce "Already yana cikin ƙasar nan, zuwa yamma zaku haɗu haka appointment ɗin ya kama" Duk wannan bayanin fuskar Mr President kuma Ddmaster bom a rufe take ruf, ya yi using wata na'ura mai sauya masa magana.. Majeederh na tsaye hannunta riƙe da Glass cup mai ɗauke da fresh milk a ciki zata miƙawa Zaytoon kenan cup ɗin ya suɓuce ƙasa ya faɗi, gabanta ya yi wani irin mummunan faɗuwa ta dafe ƙirji ta ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!" Zaytoon ta ce "Lafiya?" Ta ɗan girgiza kai ta ce "Babu" Roohan ya ce "Granny wai Gimbiya da Khalil ina sukai ne? Basa gidan nan fa" Ta ɗan yi shiru ta ce "Kasan Gimbiya bata da sakewa Maybe wani wajan ta ja shi" Majeederh tayi shiru sai kuma ta juya number Khalil take kira ana ce mata a kashe, ta kasa samun nutsuwa ta yi alwala ta zauna tana jan casbawa....
Khalil zaune cike da gadara yake kallon Clara kafin ya ce "Ina Ddmaster bom yake?" Ta ɗan kalle shi ta ce "Ddmaster kake son gani ko kaya?" Ya ce "Both" a gajarce ta miƙe tsaye ta ce "Ba zaka samu ganin shi ba, kuma ba zaka samu ganin kayan ba" Ta zaro wuƙa a ƙugunta ta ce "Mijin Malama Ko private Investigators daga hukumar NAPTIP ta ƙasar Nigeria?" Khalil ya yi wani shu'umin murmushi ya ce "U got it well Clara, Dr Ibrahim-Khalil Daniel David, ur father's son" Clara ta kalle shi sai kuma ta saki wata dariya ta ce "Waya faɗa maka ina da uba? Who are you?" Calmly ya ce "Your twin brother Abraham" ta ce "Mahaukaci! Dog!" Bata tsaya jiran komai ba ta buɗe bayan mota ta fito da Gimbiya dake ɗaure da sarƙoƙi ta ce "Ka amince na saki mahaukaciyar uwarka, kaƙi kuma na yankata akan idanunka" Khalil ya dinga kallon Ummie irin why? Sai kuma ya ce "U can kill her if you want, zaki iya kasheta idan kina so, bani da haɗi da ita matar Ddmaster bom ce" Clara ta dafe kai ta ce "Kada ka manna mini hauka, ƙungiyarmu ba a soyayya balle aure" Khalil ya zaro picture ya nuna mata, Ummie da Mr President ne a zaune, ta ce "Wannan innocent man ne Mr President Denial David, Ddmaster bom zuciyarsa a ƙone take" Khalil ya ce "Kin taɓa ganin fuskar Ddmaster? Kin taɓa tunanin meyasa ya fifitaki? Sbd ke jininsa ce kuma ƴarsa...." Daga bayansu aka ce "Ƙarya yake miki Clara kill her yanka matar" Clara kanta ya fara juyawa bata saba ɗaukan tension ba, kawai rashin imani ta sani ta ce "bazan kasheta Until you open your face" Ddmaster zufa ya fara saukar masa, daga can gefe hukumar Pakistan na kallon komai, haka hukumar Nigeria data Germany. Ddmaster bom ya ce "Kiyi mini al'ƙawari ina buɗe fuskata zaki kasheta" Clara ta ce "Ban san kowa ba sai kai, bana saɓa al'ƙawari harshe na a tsarkake kasan ban taɓa ƙarya ba, ba kuma zan yi ba" Ddmaster ya cire mayafin fuskarsa, jikin Clara ya ɗauki rawa da ɓari a firgice ta ce "Mr President? You! Kai ne Ddmaster? Kai ne mugu kai kake mulkar jama'a kuma?" Khalil ya miƙe ya yi baya kamar zai duba sai ya tsaya a bayan Mr President, Clara ta juya ta kalli Gimbiya taga ita take kallo ga wani hawaye masu zafi kwance a Idanunta, sai kuma tayi cilli da Gimbiya tana dafe kai, Mr President ya ce "Wannan dalilin yasa na sanya mata bom ina dannawa zai tashi da ita wlh ba zan barta ba, dole rayuwar wani ta sanwalta a cikinku, Clara waccan ɗin babarki ce ni kuma Mahaifinki ne shi kuma biyuninki ke, akan kuɗi babu abinda ba zan iya aikatawa ba, na zaɓi mayar dake karuwa saboda samun cikar burina, na rabaki da uwarki wacce na saka a kasheta amma bata mutu ba, a yau ko ni ko ku dole rai ya sanwalta" Remote yake ƙoƙarin ɗakkowa da wani irin gudu Clara da Khalil sukai kan Dad ɗin nasu, a lokaci ɗaya cikin sa'a guda hawaye na fitowa daga cikin idanuwansu suka caka masa wuƙa ɗaya a ƙirji ɗaya gadon baya, remote ɗin ya faɗi ƙasa, Khalil ya rungume Dad ɗinsa ya ce "I love you Daddy, bani da zaɓi kai ka zaɓawa kan ka...," Bai rufe baki ba Dad da yake numfashi da ƙyar ya zaro wuƙa da sauri ya daɓawa Khalil a ƙahon zuciyarsa, the same time ya caka masa sirinjin allurar a wuyansa.....
[18/09, 8:13 pm] Sdy Auwal Gstc: _*Nimcyluv sarauta 90*_


*Follow my Facebook account🤓 muna taɓa muhawara a can kar ayi baku👇🏼*
https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL


Wani irin deep hot kisses ya yi mata mai sanyi wanda ya sanya ya ji numfashinta ya sauka a neck ɗinsa, wani irin ƙamshin mai haɗe da sanyin Spraymint mouth freshener ya ratsa hancin Khalil, wanda yake jinsa har ƙasan zuciyarsa, ta ɗan hasken daya rage ya tallafo fuskarta yana mata wani irin zallar kallo mai cike da sahihin so da ƙauna, kallonta yake kamar zai cinyeta ɗanya, ya jima da fahimtar ba a reality take ɗaukan dukkan wani abu da yake mata ba.


Jikinsa ne ya ɗauki rawa da ɓari, kamar yadda nata yake, jikinta ya gama farkawa ita ɗince dai har yanzu idanunta yake rufe, amma ilahirin gab'ɓanta karkarwa suke, jikinta ya mimmiƙe wani irin hargitsatsen fitinannan saƙo Khalil yake aika mata, a hankali ta fashe da siririn kuka tana riƙe kansa tare da danna shi a ƙirjinta da kyau, yadda zai samu full access na yin abinda yake, cikin raɗa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login