Showing 15001 words to 18000 words out of 117648 words
Chapter 6 - YA ABIN YAKE Book Complete By Nazeefa Sabo Nashe .txt
Sajjad.
Lauratu tana da hud’u: Sa’ad,Sa’adatu sai Sadik da Saddik’a.
Nan kuwa gidan Umaru Usman Dan Borno da aka fi sani da UU D’an Borno kamar yarda kuka sani Sadiya Na da yara biyar Hammad Humaid Sai Hamidan da Abdul Hameed da Humaid.
Ita kuma Sakina (Ammi Na da Biyar) Najwa ce babba sai Nasma da Ahlam sai Muneerat da Hamda. Wad’anna sune jikokin Didi tsohuwa mai ran k’arfe, mai tsage gaskiya duk d’acinta. Manyan duk an aurar dasu idan ka cire d’akin Ammi da mace d’aya jal ta aurar. Inda ta auri wani hamshak’in d’an kasuwa suke zaune a can k’asar ibadan yanki yarbawa duk da bahaushe ne ya zab’i zaman ibadan a can ya ke duk wasu kamfaninnikansa saboda rashin kishin arewa.
_____________________________
Da k’arfe hud’u na yammacin ranar ta juma’a suka Sanka a airport d’in Malam Aminu Kano international airport da ke birnin kano.
Kaf k’annensa maza da cousins brothers d’insa ne suka zo tararsa.
Suka fara saukowa daga jirgin, ransa ya b’aci lokacin da ya fara shak’ar iskar Nigeria.
Sanye yake cikin black jeans na companyn Gucci, Sai casual T.shirt Na companyn Tommy Hilfiger dake U.S da rigar sanyin Tomford Bumber a jikinsa sai zabga k’amshin turarensa na kullum yake Emporio armani oud. K’afafunsa sanye da takalman Dolce and Gabbana logo embossed leather slippers, bak’ake Wanda suka haskaka kyakkyawar tausashshiyar fatar k’afarsa. Idanunsa kuwa cikin black glass suke Na companyn Gucci. Hannunsa da yake d’aure da agogo k’irar Gucci bracelet watch ya kalla. Yana sauka daga matattakalar jirgin fuskarsa a d’an d’aure yana sakin tsaki akai-akai musamman ganin arnen zafin da ake kwararawa a k’asar Nigeria mai barazanar dafa fatar mutum, musamman Su da suka dad’e basa k’asar. Ya ilahil Alameeen’ ya fad’a murya a cunkushe.
Daga kallon farko idan kayi masa zata zaka yi saurayi ne da ba zai haure matakin shekaru takatin ba ba zaka Ta’ba bashi shekaru har talatin da takwas ba.
Da gudu k’annesa suka rungume y’an cutest yaransa. Idanun Hamood cikin na Kamla da sauri ya bud’e baki yace “Masha Allah Hamda’s carbon copy.” Da sauri sauran ma suka kai dubansu kanta suna ta’ajjabi da mamaki a zahirance suka ce “Wannan dai Hamda ka haifo y’a.” Gabansa ne yake fad’uwa a duk sa’ilin da suka had’a Hamda da y’arsa, duk da zahiran shima ya san suna kama irin kamar nan da dole idan Na gansu ka san JININ SU D’AYA.
[1/12, 7:43 AM] Nazeefah Nashe: Alk’alamin JIKAR NASHE
Ya Abin Yake?
Page 9.
08033748387
Ina macen datake fama da ciwon mara in mijin yana saduwa dake kirinka jin xafi to kixo kimallaki female care
Ina masu fama da basir constfree tea yana magnin basir yana gyara fata tayi kyau
Royal jelly ya gyara mace yafito mata da shafe dinta kama daga breast hips duwawo
Fat bunner yana rage kitse ina wanda kitse ya mata yawa a jiki kigarxayo kimallaki naki 09131164861
Gamai bukatan yin register xai iyayi yasaya afarashin company
Company ght zakiyi registered akan 4500 kikawo mutun biyu suyi siyaya company zatabaki 36000 inbaki shiryaba karkimin mgn ngd
_________________
Haka suka d’unguma zuwa ainahin main House d’in su da ke unguwar Hotoro G.R.A.
Mutanen gidan suna jin shigowar motocinsu suka fita a guje domin tararsa.
Sakina ce kawai bata fito ba, da yaranta masu bak’in hali Najma da Nasma. Amma hatta da Muneerat sai da ta fito a guje duk da kiran da Ammin take zabga mata.
Tunda ya fito ya zubawa k’annensa ido yana mamakin yarda suka girma lokaci guda. Har zai shiga sashen mahaifiyarsa Hamood ya kama hannunsa had’e da fad’in “Big Bro rufa mana asiri idan ba so kake Didi tasa ayi yak’in duniya na biyu ba.”
Ya d’an bud’e ido yana kallon k’aninnasa, saboda sam ya manta a irin wannan lokacin Didin tana kasancewa ne a gidansu.
Ya juya direct ya nufa sashenta, yaransa da matarsa suna bin sa da sauri. Mahmah da take tsaye a window Ta saki Hamdala don farin cikin ganin yaronta, duk da kawaici da Alkunya ya hanata fita ta ganshi.
Didi da azama ta mik’e tana janye k’afarta da Hamda take shafawa Man zafi. Cikin fara’a kamar bakinta zai yage take fad’in Maraba lale, Oyoyo da mutanen Birmingham Masha Allah tubarakallah. Ta rungumeshi cikin tsananin farin ciki.
Hamda kuwa idanunta cikin na Kamla tana mamakin tsananin kamarsu. Su kansu su Khairi kallonta suke musamman Nanna da ta kasa janye idanunta daga kallon yarinyar mai kama da tata d’iyar Kwabo da Kwabo. Saboda duk zuwan da take Hamda lokacin tana makaranta shi yasa basu tab’a had’uwa da ita ba.
Hamda cikin ladabi ta durk’usa ta gaida Nanna, ita kuwa ta jata a jiki tana kallon Didi da Hammad da ya rintse idanunsa yana mamakin yarda yarinyar ta sake girma, da gaske kuma tsananin kamanninsu ya sake bayyana da Kamla musamman yanzu da suke zaune waje d’aya.
Cikin Masifa Didi ta dinga korar mutanen da suka yi dandazo a falonta. “Haba yau naji masifa, a bar mutum ma ya huta da jikokinsa ba za’a bari an zo an zuba musu ido kamar me? Ni jaraba ta yaran gidannan ta fara isata, mutane ga ido k’wala-k’wala, duk sun bi sun gado manyan idona na masifa.”
Ta dinga mita bayan sun tafi sun barta da jikokinnata sai kace su ba jikokinta bane, ko da yake su kansu sun san soyayyar da takewa Hammad daban ce, ko kuma don kasancewarsa shine Jikanta Babba a maza tunda Najwa da suke kira Yana ta girme masa.
Sai da suka tafin sannan ta zuba idonta akan Hamda ta saki baki tana kallon kamanninsu da Kamla.
Gaza shiru tayi har sai da ta magantu “Ikon Allah, ikon gaske kai kuma Hammadu sai ka haifo mai kama da Hamda kwabo da kwabo, ko wa suka yo a dangi don mu dai kaf danginmu ba masu kama da mutanen itofiya (Ethiopian).
Idanunsa ya zuba yana kallonsu, a duk sanda kuma ya kallesu sai gabansa ya buga fad’uwar gaba ta sameshi, baya son ana yawan ambaton kamanninsu haka ne yake sawa yaji k’irjinsa kamar ya tarwatse.
Nanna ta ce “Ai haka lamarin ubangiji yake, ba abin mamaki bane musamman kasancewarsu Jini d’aya, ai k’arfin jini ya zarce haka.” Hammad ya sake jin dukan da k’irjinsa yake ya tsananta musamman da ake ta nanata kalmar Jini d’aya. Anya kuwa wannan sirrin da suke k’ok’arin k’udindunewa nan gaba kad’an kuwa ba zai fallasu ba.
A sama ya jiyo muryar Didi tana tsaki “Ayi mace lusara, kina girma kina cin kashi abincin ma jira kike nace ki d’ebo ki kawo musu? Bayan tun safe muke tsaye akan digadiginmu muna aikinnan amma ba zaki tashi ki kwaso su ba.”
Ita dai Hamda bata bari ta k’arasa mitar ba, sai tsintar ta suka yi a k’ofar kitchen, Nanna Ta sake binta da kallo tana yaba kyau da tsarin halittar zubin jikin yarinyar, farin ciki ya cikata da ta tuna itama Kamlanta haka zata dawo mai kyau idan ta girma.
Shi kuwa Hammad tunaninsa daban yake ta yarda yake mamakin girmanta, duk da ba wata k’iba bace da ita amma duk wasu halittu na y’an matancinta a cike taf da albarkatun ubangiji. Yayi ta’awwizu da tunanin hakan da yayi don ya San sarai ba shi da hurumi anan.
K’ememe Didi ta hanasu tafiya wajen Mahmah da ta kasa zuwa ta gansu, anan suka zube akan daddumar Didi mai taushin gaske suka ci abincin mai dad’I don Didi gwana ce wajen girki shi yasa Hamda ita ma ta koya. Ta iya girkuna kala-kala.
Shigowa U U D’an Borno ya yi yana fara’a, da farin cikin ganin yaronsa da familynsa.
Da sauri Hammad da Nanna suka durk’usa don gaisheshi haka nan su Khairi da Abul khair ma suka gaisheshi.
Idanunsa akan Kamla yana dafe da kan Abul khair ya ce “Didi kin ga ikon Allah ko? Tunda naje barkar yarinyar nan na ce miki kamar su d’aya da Hamda, don har hotonta Na d’auko a waya Na had’a da Na Hamda wallahi ba banbanci ko kad’an banbancin d’aya ne wannan lotsawar da Hamda take da shi a k’asan hab’a ita Kamla a gefen Hanci take da shi. Tabbas kun haifawa Hamda y’a don nan gaba ko guduwa tayi da ita ba wanda Zai ce ba y’arta bace.”
Gani suka yi kawai Hammad ya rik’e kansa ya mik’e, had’e da cewa “Godiya nake Didi, bari naje na gaida iyalan Abbu” daga haka yasa kai ya fice da sauri bai saurari surutun Didi ba.
Su Nanna ma suka bi shi suna dariya.
B’angaren Ammi ya fara shiga direct, yana fatan ya iya danne b’acin ransa idan yayi arba da fuskarta da kai tsaye yake kira bak’ar Fuska. Addu’oi ya fara yi a zuciyarsa kafin ya saka kai cikin sashen nata.
A zaune ya sameta saman kujera, gaba d’aya yanayinta zaka kalla ka tabbatarwa kanka da gaske yau bata cikin nutsuwar zuciya, don dai ko kallabin kanta bata d’aura ba balle akai tajallin gyaran gashi.
Idanunta k’ozai-k’ozai babu kwalli. Guri d’aya ta zubawa ido, da alama tayi nisa cikin zuzzurfan tunanin da ya ke mata kaikawo a zuciya.
Bata ji sallamarsu ba sam, sai k’amshin turarensa da ya riga ya zauna rad’am a hancinta ba tun yau ba tun yana saurayi shine dai ainahin turaren da yake amfani da shi.
K’amshin ne ya farkar da ita cikin razani, idanunsa kuwa suka gauraya cikin nata.
Y’ar fara’ar da take fuskarsa ya d’inke tsaf, tare da amsa gaisuwar su Najma da suke gaisheshi cikin mutuntawa, kasancewar sun san shi mutum ne da baya wasa da su tun suna yara balle yanzu da ya mallaki hankalin kansa.
Shigowar Kamla ne yasa Ammi wani irin mik’ewa da sauri cikin razana tana dubanta. Ganin yarda idanu suka yi yawa a kanta sai kuma ta sunkuyar da kai ta waske tana jan hannun Abulkhairi.
Abin mamaki madadin shi da yake matsayin d’a wajenta ya gaisheta, itace take gaisheshi cikin basarwa da sunkuyar da kai tamkar dai surikinta.
Mintuna uku cikakku bai k’ara a d’akin ba, ya mik’e da sauri ya fice, yana jin zcuciyarsa kamar ana hura masa wuta. Suma su Nanna suka d’unguma suka bishi.
Hakanne ya bawa Ammi damar shigewa d’aki a sukwane tana sake lalubar numberr wayar babbar aminiyarta da tun safe take nema bata shiga. Wannan karan ma dai still wayar a rufe take kamar yarda ake ta sake jaddada mata a waya.
A kujerar parlourn Mahmah ya zube idanunsa a runtse kafin ya bud’e ya zube su cikin na mahaifiyrsa da take ta kallonsa cike da murmushi. Rabin hankalinta kuma yana kan Nanna da y’an jikokinta da sam babu shakuwa a tsakaninsu. Taja hannun Abul khairi tare da fad’in “Maigidan da ba awo ba cefane.”
Sai da ya sauke ajiyar zuciya kafin ya samu damar gaishe da Mahmahn cikin k’arfin hali da dauriyar zuciya. Mahmah ta amsa masa zuciyarta cike da farin cikin zuwansa Nigeria.
Sun dad’e suna hira duk da shi rabin hankalinsa ba akan hirar yake ba, sau tari sai Nanna ta sako shi a zancen sannan yake ankarewa da nisan tunanin da ya lula.
Ganin da ya yi ya rasa samun nutsuwa ya mik’e ya nufi sashensa, don ya sake nazari sosai akan lamarin da kansa tsaye zai iya cewa ALMARA.
_____________________________
Cikin sa’a k’arfe sha biyun dare ta samu numberr aminiyarta ta ta shiga ta saki wata nauyayyiyar ajiyar zuciya, duk wani abu da ya tokare mata na b’acin rai ya sauka daga k’irjinta. Gani take tamkar ta samu mafita ta gama.
Murya a cunkushe ta ce “Ke kuwa Kady ina kika shiga tun safe nake nemanki?”
Kady daga can taja ajiyar zuciya “Ke dai bari, ya aka yi? Akwai matsala ne?”
Tsaki Nanna taja ta ce “Idan kin ji matsala d’aya kenan matsaloli dai yaronnan Hammad fa ya dawo k’asar nan.”
“Innalillahi!” Daga can Kady ta zabga kafin ta ce “Yanzu meye abin yi?” Ammi taja tsaki “Ke zan tambaya kady, wallahi kaina ya k’ulle kin jefa ni a matsala da na sani tun farko ban karb’i shawararki ba, takaicina d’aya ranar fallasuwar sirrina, ranar da za’a tono b’aragurbin k’wan da na burne, ranar da jama’a da dama za su......” kuka ne ya kufce mata. Kady tayi tsaki “Yanzu na barki kiyi kukan kenan? Idan kin gama kukan sai na kiraki, tunda kuka ne zai mana maganin matsalarmu.”
Had’iye kukan tayi da kyar ta ce “To yanzu ya kike so ayi?”
“Ki bud’e kunne da kyau ki jini, idan zai yiwu a salwantar da ran Hammad kawai idan ba haka ba komai na iya faruwa.”
Ammi ta saki ajiyar zuciya a karo na biyu kafin Ta ce “Kina ganin haka ne mafita?” Tsaki kawai Kady ta ja tare da latse madannin wayar ta mutu ta san sarai Ammin yanzu zata waske zancen kisan, duk da ita dai bata hango wata mafita bayan wannanba.
___________
Sai da ya yi wanka sannan ya samu nutsuwa, duk da har a lokacin yana jin yanayin yarda k’irjinsa yake duka, Kansa yana matuk’ar sarawa, a zahirin gaskiya ji yake ya
Kamata ya sanar da mahaifiyarsa zancen nan, duk da muninsa ya kai muni amma bai kamata ya b’oye mata ba ba yanzu ake ji ba gaba ake ji, tunda ya tabbatar Hamda bata da gadon mahaifinsa, Bai kamata kuma ta cigaba da amsa sunan Mahaifin nasa alhali shi yasa ba ubanta bane.......
To fa! Wannan shine Ya Abin Yake?
[1/12, 7:43 AM] Nazeefah Nashe: Alk’alamin Jikar Nashe.
Ya Abin Yake?
08033748387
Follow me on Wattpad
@Nazeefah381
ArewaBooks
@Nazeefah
https://arewabooks.com/book?id=635c58dc8a75f51b283a378e
Da safiyar ranar ta shirya tsaf, da azama ta ja motarta sai gidan Kady don sam kasa barci tayi jiya tambayar duniya kuma Abbu yayi mata sai ta ce Bata jin dad’i ne, shi yasa yau tana cewa zata Asibiti bai yi nawar hanata ba, don yanayin da ta kwana shi kansa abin ya yi matuk’ar rikitashi, sai ya ce tun bayan haihuwar Hamda bai tab’a riskarta a yanayi kwatankwacin na jiya ba.
Daga jin yanayin horn d’in motar Kady Ta tabbatar mutuniyartace ita kanta sam bata cikin nutsuwa don haka yau da wuri ta sallami mai gidan, tana shirin kiranta a waya sai gata ta bayyana. Da sauri ta bud’e k’ofar hasashenta kuwa ya yi dai-dai don Sakina ce cikin wani irin yanayi ta shigo parlourn, wullar da jakarta kawai tayi ta ce “Kina ganin kashe Hammad shi zai rufe b’aragurbin sirrina?
“K’warai kuwa.” Kady ta masa mata cike da k’warin gwiwa “Rashin salwantar da rayuwar Hammad shi yake nuni da fallasuwar b’aragurbin k’wan da zai girgiza ahalin D’an Borno.”
Sakina tayi tsai da ranta, kafin ta saki gwauran ajiyar zuciya, ta ce “Bana son salwantar rai, zan saka dai a sake masa gargad’i had’e da tabbatar masa da k’udirina na k’arshe idan har ya sake ya bayyanawa mutane gaskiyar lamari.”
Kady tsaki ta ja, kafin ta ce “Ni ban ga dalilinki na rashin son kashe shi ba, mutumin da rayuwarsa kamar wata bala’i ce ga taki rayuwar, ke da kanki kince baya miki kallon mutunci balle ya girmamaki, kina tunanin idan ya cigaba da yi miki haka uwarsa ba zata so sanin dalili ba? Kina tunanin idan ya b’oyewa kowa zai iya b’oyewa mahaifiyarsa?”
Sakina ta share zufar da ta game goshinta. Hankalinta a tashe ta ce “Tabbas zancenki na kan hanya, saboda yarinyarsa Kamla yarda kika san kaki yarinyar nan Hamda tayi saboda tsananin kamarsu, ni kaina har mamakin bayyanuwar kamar nayi, wallahi abin ya bani tsoro kamar dai wata ishara ce Allah yake so ya nuna....”
“Shi nake so ki gane, ki cire duk wani shakku a kawar dashi daga doron k’asa, ina dalili? Tun ranar da abin ya afku na sanar da ke a kawar da shi kika wani ce a gargad’eshi, alhali kwalliya bata biya kud’in sabulu ba namijin dai da kike so baki haifeshi ba, kika tsaya cewa wai yaro ne zai ji tsoron tona hakan ga kowa, to ga dai yaro nan ya girma kuma yana shirin bankad’a duk wani sirri idan ba kiyi wasa ba, haba idan da nice ai da tuni an wuce wajen.”
Sakina ta ja ajiyar zuciya “Shikkenan, ki bari zan shigo yanke shawara anjima insha Allah.” Daga haka suka yi sallama, Sakina kam ta samu salama a zuciyarta ta kuma amince da shawarar Kady tana ganin hakan kawai shine mafita a gareta, da ahalin D’an Borno family gaba d’aya.
_____________________________
Tun asuba da ta farka bata koma ba gyara sashen Didi tayi kafin ta tafi sashen Amminta nan ma ta gyara. Wanka kawai tayi ta dawo parlourn Didin ta zauna had’e da d’aukar Alk’ur’ani tana karatu, Didi kuwa lazimi take, da radio a gefenta tana saurarar labaran BBC Hausa.
Sai da Takwas ta cika sannan ta shiga kitchen don d’ora abin karyawa kasancewar juma’a ce Didin bata azimin tsofaffi don idan watan azimin tsoffin ya shiga sau hud’u take yinsa duk sati litinin,talata,laraba da Alhamis.
Kunun tsamiya da ta saka wadataccen lemon tsami tayi musu, sannan ta soya musu k’osai da dankali da k’wai.
Kafin kace me? Har ta gama, ta kawo Daddumar Didin ta jeresu. Didin shi mata albarka kawai take tana fad’in Uwarki tayi farar haihuwa sai dai ita bata san haka ba shashasha, a zamanin nan samun yarinya mai hali irin naki ai sai an tona.” Murmushi kawai Hamda tayi. Dai-dai lokacin da aka yi knocking k’ofar sashen Didin.
Tsaki Didi tayi kafin ta ce “Jaraba, ko waye kuma da safiyar nan? Allah yasa dai lafiya.”
Hamda ta kalli agogon parlourn ta ce “Didi k’arfe 9:30, yanzu ai ba sassafe bane.” “Gurinki ne ba sassafe ba wajen mutanen gidan nan kam ai ba mamaki yanzu suka yi juyin farko.” Hamda dariya ta guntse kafin ta k’arasa bakin k’ofar. Cikin sanyin muryarta ta ce “Wanene?” “Bud’e” kawai ya ce cikin dakewar tasa muryar.
Gabanta ne ya fad’i sanin cewa shine tun jiya ta haddaci muryar tasa, da zarar taji take riskar kanta cikin wata irin razananniyar fad’uwar gaba.
Hannunta na rawa ta murd’a handle d’in k’ofar bayan ta murza mukullin da yake jikin k’ofar.
K’amshin turarensa ne ya fara dokar hancinta kafin ya shigo idanunsa a kanta, yarda ta mak’ale jikin bangon ya tabbatar masa da yanayinta na rashin sabo da jama’a. Kamar a tsorace take da mutane bata sakewa da su, kullum yanayinta na nuna kamar ace kyat ta zura da gudu.
Idanunta a k’asa cikin rawar murya ta ce “Ina kwana?”
D’auke idanunsa ya yi daga kanta kafin ya amsa da “Lafiya” ya shige ya barta a tsaye ta bi bayansa da kallo sanye yake da jallabiya