Showing 30001 words to 33000 words out of 107121 words
Chapter 11 - MA'AIKACIYAR GOMNATI BOOK COMPLETE BY Asma Baffa .pdf
Tana shiga ta sanarwa sauran sis nata,shegiya Allah ya kawota zata ci ubanta yau wlh,sadiya
kuwa wata sandar karfe ta dakko.tana Ashe yau za ayi daukan rai,kwanan wata zai kare,naja
jeki waje ki jira tana fitowa ki mana flashing.
Ita kuwa iklas part din maman omar ta wuce,hannu bibiyu suka tarbeta,yau iklas an sami
waje har kitchen ita ta taya mama girki,wajen 5:30 tayiwa mama sallama ta fito domin tafiya
gida,
Tazo tsakiyar gidan su sadiya suka zagayeta kafin kace me sun rufe ta da duka,sai da suka
farfasawa iklas jiki,da kyar mama da masu gadi suka kwaceta,
Hhhh Allah sarki iklas da kyar take motsi ko ina jini,fuskarta ce kawai take normal,hospital
mama tasa driver ya kaisu ita da iklas,dressing akayi mata,mama tayi tayi iklas ta bari su kaita
gida amma taki yarda,dole suka kyaleta ta shiga taxi ta tafi gida,omar da ummi hankalinsu ya
tashi ganin ba iklas ba labarinta,har dare shuru,Omar sai tsaki yakeyi ya kasa zaune ya kasa
tsaye,sai duba agogo yakeyi,
Shaddar iklas ta baci da jinin dukan su sadiya,sannan gashi period din da takeyi shima garin
fadan pad ta goce,duk ya bata mata jiki,tana dingishi hade da nishi ta rarrafa ta shiga gidan,su
ummi ta gani tsaye a tsakar gida hankalinsu tashe,da gani ita suke jira,tana shiga da sauri suka
tareta,
Rushewa da kuka iklas tayi,tana ta kuka me ban tausayi,jikinta suka gani duk rauni,omar ne
ya riko hannunta,accident kikayi? cewar omar ,cikin sheshekar kuka iklas tace
wash...was...wasu suka dakeni,sai ta kara sakin kuka,
Su waye?wanne yan iskanne suka Dakar min jikata marainiyar Allah ummi ke fadi,wasu ne
ummi,idan kin sansu ki fada min cewar omar,ni ban sansu ba kawai sunce na zagesu wai,omar
kuwa Sam bai yarda da zancen iklas ba.ummi kuwa yarda tayi tace Allah zai saka miki,muje kiyi
wanka ki gasa jikin.
Ruwan zafi ummi ta hada mata kana tayi wanka,tana daga cikin toilet ta kwalawa ummi
kira,ummi kuwa bata kusa sai omar dake zaune a kujera,me kike so a miki ummi sallah
takeyi,pls sir wata Leda zaka dauko min a room kan bed dina,dakin su iklas ya shiga ya dauko
ledar wacce ba komai bane ciki face pant da pad,tsaki ya ja karbi kayan kazantarki
malama,hannu ta miko ta window ta karba,omar kam hannun nata ya bi da kallo,yanda suke
masu matukar kyau ga ruwa jiki sunyi fresh fari tas, shirya kanta tayi, tea omar ya hada mata ta
sha,duk abinda sukeyi ummi tana sallah tana kallonsu tare da jin dadi, suhaila harda kukan
tausayin iklas.
Gomnati sai kuka takeyi tana yarfe hannu abin nata harda shagwaba ya koma,omar kuwa
tausayi ta bashi har wani lallabata yakeyi duk zatonta zafin ciwo ne,kukan nata jinsa yake har
ransa.
Haka sukayi fama da iklas har ta warke,kamar kullum iklas ta fito daga schl a gefen titi wata
mota dalleliya ta parker a saitin iklas,sauke glass kasa akaayi,ba kowa bane face sultan,yazo
wucewa ya hango wata kamar ummi da taje wajen maman omar,wacce ya gani da omar yana
kokwanto,
Gaisawa sukayi ummi kike ko?yea ya gida ya aiki?cewar iklas dan ta San
sultan,ahmmmm...kamar ke na gani da omar rannan a garden kingdom ko?da mamaki iklas ta
nuna Sam bata San waye Omar ba,ta manta ma da wani omar,wanne omarfa?frnd dina mana
Wanda ya baki envelop ki kaiwa mamansa.ohhhhh na tuna dama sunansa omar?ai na manta
ma,pls ya koma gida kuwa,
Au dama bake na gani tare dashi ba,gaskia ba ni bace,maybe wata ce,ok pls kin taba yin
sana'ar talla?cewar sultan.mene kuma talla ban gane ba.it's OK bari naje na gode fa,sultan yaja
motarsa yayi gaba abinsa.
Da sauri iklas ta sha kwana,ko nisa batayi ba wasu Igbo suka parker sukayi mata lift,har taki
shiga motar saboda yan iska ne a unguwar,sabo da kar sultan ya ganota ta shige motar ba tare
da tunanin komai ba,
Joseph ne ya dawo baya kusa da iklas India shi kuma nmandi ya ci gaba da tukinsa,ga
hanya kusa amma sai suka canja suka dauki ta nesa wacce za a Dade ba a zo layin su iklas ba,
Sai shawagi sukeyi da ita a mota,Joseph ne ya matsa jikin iklas,ta kara matsawa,har suka kai
karshen bangon murfin motar,
Iklas sai hakuri take basu tana rokon su sauketa amma ina,tuni Joseph ya fara shafa
cinyoyinta,kuka ta saka musu,amma sai daria sukeyi mata tare da kara kwakwumeta,manne
jikinta tayi waje daya yayinda shi kuma ya sutale hijab dinta,wow this girl fine woooo,omoh see
her hair like arabs girl,
Kirjinta ya fara kokarin shafawa ta tsala ihu, make bakinta yayi,a take ya fashe yana jini har
hancinta,tafiya sukeyi har sukazo gidan su iklas basu gane cewar gidansu bane,omar ya leko
kofar gida yana jiran suhaila ta kawo masa recharge card daya aiketa ta siyo masa,
Iklas ya hango a bayan motar wasu kuma mutumin taba jikinta yakeyi,iklas kuwa tana ganin
gidansu ta kwala ihu tana Neman agaji, su Joseph tabbas sun ga alama zata tona musu
asiri,gashi ta makale jikinta ko kirjinta ya kasa latsowa,haushi yaji ya fesa mata mari ya taka
birki kuuuuu,ta fito kuwa da gudu suka ja motarsu da gudun tsiya.
Suka bar unguwar,Omar kam ya gama tsorata da lamarin iklas, ya rasa ma tantancewa me
yakeji a zuciarsa, wanne kalar bakin ciki ne yake ji ya kasa ganewa.
Hannun suhaila ya ja sukayi cikin gida, kallo daya yayiwa iklas ya dauke kai,baki duk jini da
hanci,a waje ta tsaya ta goge jinin sabo da ummi,
Wanka tayi da sallah taci abinci,sai istigifari iklas keyi a ranta, duk da tasan bata da laifi
amma ai ganganci tayi tasan yan iskane amma ta shiga motarsu,
Ba abinda ya dameta irin kallon da Omar ya mata,haka kawai taji ta shiga damua,gashi ko
magana yaki yi bare ta samu damar wanke kanta,yanzu zai mata kallon yar iska.kunyarsa take
ji sosai,duk tayi wani sukuku da ita,ummi har tambayarta tayi ko lfy?amma tace normal take
gajia ce.
9:30pm washe gari kowa ya tashi banda Omar, yau ba schl Saturday, ummi ce ta umarci
iklas da taje ta Kira Omar suyi break,kwance ta sameshi sai marfakansa yakeyi, tashinsa ta fara
yi.a tsorace ya tashi zaune daga shi sai boxers, tsoro ne ya kamashi sosai kan mafarkin da
yayi,bai San sanda a rungume iklas ba,yana shakar kamshin wuyanta tare da sakin ajiyar zucia
Asmabaffa
[27/03, 17:48] Hassan Atk: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ
45-50
By
Asmabaffa
Na gode masoyana Allah karo karfin ido.
Kiciniyar kwace kanta takeyi amma ya mata rungumar karfi,da kyar ta fara zamewa cikin
magagin bacci omar yace 2nmt pls.....tsayawa tayi cak tare da lafewa ita dama iklas ta Dade da
son ta jita a kirjin omar,bata San me yasa ba kuma ta rasa dalilin da yasa jikin omar ke
birgeta.sun dauki minti biyar haka omar ya dawo normal,jinsa yayi manne jikin mace ai bai San
sanda fancakalar da iklas daga jikinsa ba,sai da ta fado kasa daga bed din.
Masifa ya fara IKLAS karo na farko da Omar ya kira sunan iklas,wani zirrrrrrrr taji lokacin da
omar ya furta iklas,kallonsa tayi tare da tsilli tsilli da ido tana Sosa gashi,me ya kawoki dakin
nan,mikewa yayi idonsa jajir ya damki kunnenta,kara ta saki kadan,ba kyajin magana ko
iklas,am I ur mate? Ke bakya banbance tsakanin maza da mata,bayan yan iskan da suka
saukeki dazu kinga bance miki komai ba shine zaki sauke iskancinki kaina ko?
Ina ina ta fara ....to wai...wai ba kaine ka janyoni jikinka ba kuma ka rokeni kan na tsaya,har
hawaye kayi fa wai kar na tafi,kuma kace kai dadinka kake ji,kukan karya ta fara yi,kuma ni
taimaka maka nayi,daga taimak....shut up tashi ki fita mayyata kar ki kuma zuwa min room kije
kiyi raping dina,ki samin kazamin jikinki duk dazu wasu gardawa sun gama goga jikinsu a naki.
Kuka ta saka masa harda rufe ido da hannu,dama nasan yar iska zaka na kallona,na rantse
da Allah billahillazi la'ila ha illahuwa Allah daya ragemin hanya sukayi shine suke kokarin tabani
sir.
Kaga Allah kallo wurin da suka dinga marina akan naki yarda ai kaga jinin ma ko,ni ban wani
gani ba ke dai kawai kin lalace jikin maza kike so,in auren kike so ayi miki mana,har kayan daki
zan miki, cewar omar
Iklas tsalle tayi ta make kafada Allah kiyaye na haihu na ragwaje,ai nasan ma yanda kake ji
dani baza ka bari amin auren wuri ba,tunda kai kaka tana jin maganarka.
Igbo za a aura miki tunda su kike biyewa suna lagudaki.hawaye ta fara, wlh sir na fada ma ni
ba yar iska bace,Omar yasan gaskia kawai maganinta yake son yi sabo da ta daina ganganci.
rike haba iklas tayi kamar gaske tace ohh sir wai kai wanne mai kake shafawa ne?mene
kuma?hmmm jikinka Allah ya Omar kamar flour baka ji ba.daria ce ta kwacewa omar,ga iklas
tayi wani zaman cin tuwo a kasa, banza omar ya mata.
Minti 1 iklas tace yaya?kinga get out,kofa ya bude mata tare da kamo hannunta ya tankada
keyarta waje ya rufe kofar,sai da ta kusa faduwa kasa,tunawa tayi bata fadi kiran da ummi tace
tawa Omar ba,jikin kofar ta Dora kanta ya Omar kazo inji ummi muyi break,tsaki yaja ke kinfa
isheni kije zanzo wanka zanyi...ok.
Kamshin omar da suka ji shi ya basu tabbacin fitowarsa wani danyen yadi ne sanye jikinsa
light blue,har kasa ya gaida ummi,umaru wannan kwalliya haka kamar me zuwa zance?amshe
zancen iklas tayi haba ummi ke ba dama mutum yayi kwalliya sai kice zance zai je to shi ya
omar wa yake da ita,ina yake fita Da har zaiyi wata budurwa, to uwar shishigi ki bari umaru ya
bani amsata mana,
Murmushi omar ya saki ummi bikon matata zanje,tayi yaji sabo da rashin ganina da
batayi.sallallami ummi ta fara yanzu umaru kana da mata amma baka fada min ba,ayi hakuri
ummi,yanzu ma so nake iklas ta rakani can.dole kaje ai baka kyauta ba umaru.
Da karfi iklas tace bazanje ba kaje kai kadai ina ruwana da wata matarka,ni nasa ka
aureta,zamana takeyi,kai ta shafa can kaje da wata badai ni ba.cike da masifa ta mike zata
shige daki,omar kuwa daria kawai yakeyi kadan kadan wannan masifa ta iklas da takeyi,riko
hannunta yayi tunda bazaki ba suhaila jeki shirya ki rakani,
Tana zaune suhaila ta fito sanye cikin English wears Riga da wando masu kyau,ummi ta
gyara mata gashinta,wuce iklas tazo yi iklas kuwa kafa tasa wa suhaila ta shatile kafarta ta fadi
kasa,kuka ta fashe dashi me karfin gaske,rufe iklas da masifa ummi tayi.
Omar da ummi ne suka lallasheta da kyar,gani tayi da gaske tafiya zasuyi,fuuuu tazo ta wuce
su tare da bangaje omar,mota ta gani rantsatsiya a waje, omar na danna remote ya bude iklas
ta balle murfin gaban motar ta shige,
Shi kuwa omar murna yayi a ransa dama haka yakeso,a baya ya zaunar da suhaila shima ya
shiga.yasan idan ba iklas tafiyar baza ta yiwu ba saboda definitely ciwonsa zai tashi,amma idan
iklas na kusa ya riketa sai ya warke
Tafiya sukeyi sun fara shiga abuja city iklas kawai kumburi takeyi kamar zata ce wayyo na
shiga uku na lalace
Tunda suka fara tafiya omar ciwonsa ya fara tashi kawai zufa yakeyi ya rasa inda zai sa
kansa, ba shiri ya sadada hannunsa ya riko hannun iklas,da karfi cike da masifa ta fisge
hannunta,naga Wanda zaka rike ai yau.
Omar ta kansa yakeyi kawai shi yasan me yake ji,suhaila ce dake bayan mota ta mikowa
omar hannu gashi ya omar ni ka rike nawa hannun ka kyale na anty.iklas juyawa tayi a fusace ta
zubawa suhaila rankwashi ta make hannun wai ni sa'arki ce,ina ruwanki da shi,ba a son hannun
naki to.
Omar na nishi da kyar yake tukin motar kallon iklas yayi idonsa yayi jajir,ki daina dukanta ke
iskancin da kikeyi a garin nan wa ke dukanki,kunya iklas taji tace to a kyale maganar kana fama
da kanka,hannunta ta miko masa ungo gashi ka rike na taimakamaka.yatsunsu ya sarkafe wuri
daya yaci gaba da driving,5mnt omar ya dawo garau dashi,yayinda iklas da shi suka shiga wani
hali na shauki kowannensu ji yake jininsa na masa wani yammmm.....yammmm.
Wani katafaren barbing saloon Wanda yake hade maza da mata omar ya parker,mata maza
birjik ciki ana gyaran gashi,matan manya da yaran manya,da manyan masu kudi sune a
cikinsa,turawa ne masu aiki a ciki.gurin ya hadu kamar a turai,
Fitowa yayi sakale da hannun iklas kamar chewgum,tafiya sukeyi cike da izza,iklas ta raina
kanta kyaune kadai ya ceceta,dan duk tafi matan ciki kyau nesa ba kusa ba,sai kallonsu
akeyi,suhaila na kusa da ya omar.bangaren mata ya fara kaisu yana zaune,iklas ta karbe daya
hannun ta mika masa daya hannun gashi rike wannan dayan ya samu ya huta.
Kujera aka ba omar yana zaune gaban iklas hannunsa rike da nata haka akayi mata gyaran
gashi aka gama,suhaila ma an mata,sunyi matukar yin kyau,su Kansu masu saloon din sunyi
jinjina.
Wurin maza suka koma wannan karan iklas aka bawa kujera ta zauna gaban omar rike da
hannunsa,masifu kawai take ji a jikinta na kamar sha'awa amma ta rasa gane mene take ji.
Omar kuwa a cikin jininsa yake jin bala'in sha'awar iklas wacce bai taba ji ba,amma haka ya
daure ya cije.tunda aka fara gyarawa Omar suma iklas ta fara turbine fuska,idan ta kalli Omar
sai ta tabe baki,wlh ka cuci kanka ko kyau bakayi ba,minti daya ko biyu zata kalleshi tace ko
kyau,wai dole za a je bikon mata.
Gajia Omar yayi yace tunda sahar na son kalarsa ai alhmdlh dama dan ita nayi.mutumin da
ba a sonsa anyi yaji an barshi wooooooo....cewar iklas,duk rashin fara'ar Omar iklas daria take
sashi.
Haj rahina ce gaban baffan su omar,pls baffan yara 1million nake rokonka ka bani zan canja
motata.hajia rigimarki ta isheni duk motocin gidan nan,omar fa baya bari motoci su shekara
yake kawo sabbi,jin baffa ya ambaci omar yasa ummansu sadiya daure fuska,kaga alhaji ni ba
zancen tambadadde nazo kamin ba,dan iskan yaro Wanda tsabar bin matane yasa ya bar
gida.wa ya sani ma ko a waje tayo cikinsa....bata rufe baki ba taji saukar lafiyayyun mari har
uku...kunci ta dafe tare da tsagewa da kuka tana kururuwa ta cukume baffa da kokawa tare da
danna masa ashar,ai kuwa baffa ya sa kafa ya harbata gefensa,ta bigi center table,
Takadda ya dauko ya rubuta mata saki daya,tare da dafe kansa da kyar ya karasa
dakinsa.faduwa yayi kasa yayi sharab...mama wacce abin ya faru kan idonta da kuka ta dago
baffa,sannan ta kira maza masu aiki da driver suka kwashi baffa zuwa hospital.
Gaskia kowa ya ga yanda omar ya hadu sai ya kyasa,mata sai kallonsa sukeyi,da yawa
suna so su kawo kokon bararsu na love amma yanda suka ganshi kankame da hannun iklas
yasa suka ja baya, sai kallo daga nesa,
Take away ya musu na abinci kala kala sannan ya kamo hanyar gida,dadi ne ya kama iklas
sosai ganin baza a je bikon sahar ba.
Sabo da murna sai labari takewa Omar,suna isa gida iklas ta hango saleem, da Sauri ta
bude mota zata fita,Omar yaga saleem sarai,rigar iklas ya rike gam, kallonsa tayi yace muje
gida waccen dan iskan zaki je wajensa ko?
Naji ai na fasa zuwa,to sakeni muje gida mana,kayan suka shigar gida,a cikin motar omar ya
bar key din iklas na kusa dashi ta kwace hannunta taje wajen saleem da gudu ta karasa, har
sun fara hira akan business da aikin gomnati yanda ake cuwa cuwa kudi na shigowa, wajensu
Omar ya taka yaje cike da takama ya zubawa iklas rankwashi muje gida,cike da shagwaba tace
ya omar da zafi fa,gani yayi zata bata masa lokaci kawai ya sunkuceta ya sabata a kafada.
mutanen layin sai daria sukeyi GOMNATI ta hadu da dai dai ita.
Asmabaffa
[27/03, 17:48] Hassan Atk: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ
50-55
By
AsmaBaffa