Showing 24001 words to 27000 words out of 107121 words
Chapter 9 - MA'AIKACIYAR GOMNATI BOOK COMPLETE BY Asma Baffa .pdf
da addua,kira min yarinyar na
ganta,
Tare da mama suka Shiga dakin baffa,a kunyace iklas ta durkusa har kasa ta gaida shi,da
fara'a ya amsa tare da yaba tarbiyarta,mama hakan take,daga bisani mama tace ki saki jikinki
duk lokacin da kiga kina da lokaci ki dinga bullowa muna gaisawa,baffa ya kalli hajia baki fada
min sunanta ba,oh kaga murna tasa na kasa tambayarta,yar albarka ya sunanki? UMMI kawai
tace,bata San wanne suna zata ce ba.
Palo suka dawo iklas ta mike rashe rashe kwance kan 3seater tana ta yiwa kanta selfie,taga
gida me kyau,
Suleim ta jawo da uniform tayi musu pic kala kala,abdallah ma haka,mama na gefe amma
saida iklas ta dauka da ita,sultan ma kiransa tayi ya manne gefenta ta musu kala 3.duk tayi ne
sabo da ta nunawa oga omar.
Sai daria take basu iklas ba boye boye waje ya burgeta ta yaba.sai 5pm tawa su mama
sallama,an cika iklas da sha tara ta arziki,mama turaruka,atamfa kala biyu,baffa 20k ya
bata,sultan ma 10k ya bata,ta fito tsakar gidan kenan iyayin iklas ya kaita ta dinga zagaya
compound tana ta daukan selfie,har jikin motoci,tana haka ta kai garden,yaran haj rahina ta
hango birjik a garden.
Lallabawa tayi taji Suna ta gulmar su Omar suna zancen asiri,bata karasa ji ba sukayi karo
da Aisha,kallonta Aisha tayi take taji ta tsani iklas,ga bakin cikin kyau da taga iklas ta fisu
kaf,tayi imani wannan tafi omar ma kyau,
Kwalar iklas Aisha taci ke gidan ubanwa zaki,?gidan ubanki cewar iklas,ai tuni su sadiya ma
suka karaso wajen,iklas taga tabbas zaneta zasuyi,da sauri tace kuyi hakuri Ku saurareni,
wajen sadiya aka aiko ni,sadiya cike da bala'i tace gani lfy,karewa sadiya kallo tayi tana tuno
maganganun suleim yanda sadiya ta tsanesu ta tsani yaya Omar.a kan me za a zagi oga wlh ba
a isa ba kunji iklas da karfin Halifax.
Gajiya sadiya tayi ta dakawa iklas tsawa ke karki raina mana hankali fa,duka iklas ta
makawa sadiya a kirji,ba tare da sadiya tayi tsammani ba,,tana juyowa ta dullukawa Aisha
dundu ji kake dummmmm ta arce da uban gudu, gateman sunga komai,su kansu dadi suka
ji,domin su aisha sun gallabesu,tana zuwa gate cike da murna suka wangale mata kofa tace na
gode da karfi ta ci gaba da gudu,saida tayi nisa da gidan sannan ta Shiga taxi sai gida.
Su sadia kuwa sunyi suman tsaye,Aisha tace billahillazi duk ranar Dana hadu da yarinyar
nan....wlh.....hmm...sai na kusa zare mata numfashi. Sadiya kasa magana tayi tsabar bacin
rai,yarinya karama ta kwada mata duka haka.
Taxi na tsayawa ta wuce gida sai daria takeyi hade da haki kamar tayi gasar tsere.oga
Omar yana kwance a Palo bacci ya fara daukansa dan ya gaji da jiran dawowar iklas,dariarta ya
jiyo ya fito waje sanye da wata dakakkiyar gezna milk color,yasha kyau,
Fuska tamke kamar kullum ya kalli iklas ke lfy,kusa dashi tazo tana tuntsira daria hannunsa
ta kamo,yarrrr omar yaji bai San sanda ya fisge hannunsa ba,kara sakalo hannunsa tayi ta
jawoshi tsakar gidan tana murmushi ta shimfida musu tabarma,kaka ummi tana kallonsu domin
fitowarta kenan zata je makwafta,murmushin manya tayi tasan iklas bata fiye tsoron maza ba ta
saba da gogayya dasu,tayi talla a kwalta,ga unguwarsu hausawa kadan ne,dole mutum ya tashi
haka,danma iklas kwai tarbiya, sallama ta yi musu ta tafi gidan suna makwafta zasuyi aikin
abinci sai dare zata dawo,
Suhaila ce itama tayi sallama ta dawo daga islaamiyya,oyoyo beauty cewar omar dadi
suhaila taji tace sannu da gida yaya omar,ta wucewarta dakinsu,
Iklas kuwa kalonta ta mayar gefen omar,sir dole kasha lbr yau,nan iklas ta kwashe komai ta
fada masa,sannan ta nuna masa video da ta musu,omar harda kwalla ganin mama da yan
uwansa abin sha'awa, yayinda iklas ta bashi daria sabo da shirmen da ta dinga yi a
gidansu,kamar irin yar gida,omarma ji yayi hankalinsa ya kwanta ya kara samun nutsuwa.
Kinyi kokari yan mata cewar omar,iklas kuwa cinyar omar ta dafa kasan me nake wa
daria,zame cinyarsa omar yayi,ita kuwa iklas kallon omar takeyi kaamar jininta,kamar dan
uwanta,kuma ita bada wata manufa take taba jikinsa ba,ga kuma unguwarsu sun saba da
hakan sabo da yaren da suke unguwarsu,wannan ba komai bane wajensu.
Wai pls oga sir su waye sadiya ne?kar ki kara ce min wani oga ko sir,sunana omar..sorry to
ya omar,ina jinki suna ta zaginka da su mama har zance asiri sukeyi,ban gama ji ba mukayi
fada.fada kuma?cewar omar,sisters dinane fa,shekewa da daria iklas tayi ta manta ta sake riko
hannun omar daya,kash wannan zata kasheni wlh batasan yanayin Dana ke shiga ba a zuci
yayi maganar,daya hannnun yasa ya cire hannun iklas a jikinsa,ji yayi hannunta kamar Auduga
dan laushi.
Video ta kunna masa fadansu da su sadiya omar kanshi yasha dariar abin,sau 2 yana
kalla,drama queen dama sun zaneki,tab ai wlh basu isa ba,wannan sadiyan me siri siri kafa
kamar ta sauro,wasu zagada zagada dasu,tab Allah gidanku ya omar rida ridan tsofaffine ciki
hhhh kaga wata me kwalliyar aljanu kuwa,baki ya bige mata sannan tayi shuru,kayan da ta
samo ta nuna masa.
Yana gani yace kinji dadinki,wayarta ya karba ya dinga kallon pics din iklas a
cikingidansu,sai daria yakeyi,mikewa tayi zata kwace wayarta ta fara jin haushin dariar da yake
mata,hanata yayi tana kokarin kwacewa ta kasa,sai haki takeyi,
Zuwa tayi da iya karfinta zata makalkaleshi da sauri ya mike tsaye ya matsa kamar irin yaga
wuta zata konashi,bai son ta haddasa masa masifar da take jawo masa da zarar ta rabi jikinsa,
Pics yaci gaba da kalla har yazo kan nata da sultan,gani yayi kafadan sultan tana gogan ta
iklas,wani takaicin iklas yakeji,zuciyansa ce yaji ta baci,ga wani kishi daya taso masa,wato ma
yanda take taba shi haka takewa kowa,ai kuwa sai yayi maganinta,sai ta daina shashancin taba
jikin ko wanne namiji.
Kara kalla yayi yaga wato pics dinsu da sultan har kala 3.bai San sanda ya kwarankwatsa
wayar da kasa ba,sai da tayi warka warka,tayi raga raga.tsaki yaja cike da bacin rai ya
ficewarsa daga gidan baki daya.
Abinda Omar bai taba yi ba kenan,tunda ya dawo gidan su iklas bai taba gigin fita ba sabo da
tsoron yanayin lafiyarsa.
Iklas tayi matukar firgita kamar me aljanu,daga yi masa abin arziki ya zama tsiya
Tsoro taji kar ummi ta dawo ta tadda Omar ya bar gidan,tasan yanda ummi ke kaunar
omar,gashi bata San me yasa ya dawo gidansu da zama ba,,duk irin arziki da Allah ya
musu,yanke shawara tayi gwara fa tabi bayansa ta dawo dashi.da gudu ta bi bayansa kamar
zata tashi sama.
Titin layinsu ta mike a 80 tunda uwarta ta kawota duniya bata taba yin gudu irin wannan ba,sai
tareta matasa keyi suna gomanti gomnati,iklas amma ina Sam bata ji bata gani,
Wani uban lungu ta shawo kwana,wata majalasa ce guda ta maza,sun hango gomanti na
sheka gudu,wani cikinsu tace hey weyting?iklas tana gudu tace ba lfy ta wucesu fuuuuu...suna
gani haka suma suka kwasa da gudu suka rufa mata baya.
Tazo dai dai jikin wani shago taji an riketa caraf da mugun karfi,ido 4 sukayi da omar,da karfi
tazo zata rungumeshi tana murmushi hade da Jan numfashi,gocewa yayi da sauri ya matsa ta
rungumi iska,
Kunya taji ganin namiji yafita kamewa da taka tsantsan.
Ayi min afwa idan an samu matsala readers dan Adam ajizine.
Ina ji dake MAMAN SULTAN.
Asmabaffa
[27/03, 17:48] Hassan Atk: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ
30-35
By
Asmahbaffa
Masoyana masu karanta wannan novel duk inda kuke a kasar nan ga gaisuwata na sauke
muku mota mota,kwando kwando.ina jinjina Allah kara nisan kwana me amfani da karfin ido.ayi
min afwa kwana biyu banyi posting ba.
Me hali baya fasawa fuskar nan kamar Wanda akace mama ta rasu! haka take a
daure,tunda omar yabar gidan su iklas gabansa ya kara faduwa,gaba daya tsoro da fargarba ne
ya shigeshi Wanda bai San dalili ba,tuni yaji ciwonsa ya fara dawo masa,yayi niyyar kiran driver
sa domin ya gwada zuwa gida wajen mama,amma me yana fitowa daga gidan hankalinsa ya
tashi,ji yake kamar ana hura masa wuta a jikinsa,gaba daya ya fita a tunaninsa,ji yayi yana
neman sumewa shine ya tsaya dai dai jikin shagon da ya hango iklas na famfara gudu,cikin
zafin nama ya riketa dan tabbas ya San nemansa ta fito yi,gashi magriba ma tayi,
Iklas kuwa tunda taji kunyar gocewa da omar yayi dan kar ta rungumeshi, ido ta kafa
masa,nan ta hango jikin omar na rawa kaf kaf kamar mazari,ga gumi na keto masa duk da
cewar ba a Dade da dauke ruwan sama ba,kara kura masa ido tayi nan fa ya fara dafe kirji yana
cije lips kamar zai fadi,idonsa sai wani lumshewa sukeyi,tsoro ne ya kamata,sir....ya omar wai
lafiyarka kuwa?
Hannu ta kai zata kama hannunsa ya boye hannun,fuska ta daure itama ta fisgo hannun
nasa tare da cewa! muje gida ya omar baka da lfy,rike take dashi gam,shi kuwa ba musu ya
bita,suka jera abin sha'awa kowannensu na ji da kansa wajen baiwa.
Duk inda suka ratsa sai an kallesu an kara kalla,duk sun haske unguwar,kowa nuna gomnati
yakeyi suna ai bro dinta ne yazo,me kudi ne,gashi nan gomnati ta daina talla,ta zama yer
gayu,maganganu kala kala.
Gida suka karaso lokacin Omar ya fara nishi ma zai fadi kasa,da sallama suka shiga,yana
zura kafarsa daya cikin gidan yaji wani azababbiyar niima da kwanciyar hankali,take yaji gaba
daya ciwonsa ya yaye lokaci daya...a ransa ya furta lallai wannan gidan ni'ima ne,
Bayan sallar isha kaka ummi ta dawo daga unguwa,yanzu most of d time omar ke wa
suhaila assignment, yau ma hakane shi yayi mata homework,
misalin karfe 1 na dare iklas ta farka,hanklinta ya kasa kwanciya tana tunanin ya omar karfa ko
bashi da lfy,
Mika da hamma tayi ta kama shagwaba tana ummi fitsari ki rakani,farkawar ummi keda
wuya ta fara masifa ba inda zani da tsohon Daren nan,ke kenan fitsari da zawo,dama haka iklas
ke so,ficewa tayi sadaf sadaf da sanda ta murda dakin omar,a zaune ta ganshi yayi tagumi a
gefen bed,dago kansa yayi yasan dama sai ita,
A tsorace ta karasa kusa dashi sir omar bacci ka kasa yi ne?harara ya watsa mata,ki daina
zuwa wajena da dare ko ba komai sabo da gudun zargi,ba kya jin magana,ki daina sani
magana fa tam,baki ta turo kai ya omar Allah baka San a ma gwaninta ba,me zanyi ma ina
tunanin ko baka da lfy ne that's y na leko ka,OK tnx as u can see am fine sai ki tafi.
A shagwabe tana buga kafa to kayi bacci mana,dan ta tafi kawai sai omar ya kwanta a bed
din,kafin ya mike kafarsa ta karasa ta hada leg nasa wuri daya ta mikar masa dasu,blanket taja
ta rufa masa,a.c ta kara karfinta kana ta kashe masa light,ta fice zuwa dakinsu,da rarrafe ta
shiga dan kar kaka taji tafiyarta, kwantawa tayi ta bar omar da tunaninta, yanda ta iya kula da
mutum , wai bata ma auri mutum ba kenan ina ga ta aureshi.lallai mijinta ya more,sahar dinsa
ya tuno wacce ko kallon arziki bata yi masa bare ta gyara masa kwanciya,wai a haka ta waye
kuma yar boko,ga me talla nayin abinda ta gagara yi.
3days later omar yasa an kawowa suhaila sweet da snacks,wayoyinsa duka a flymode suke
yana buga game a Palo,yayin da suhaila da ummi suka tafi kasuwa,iklas ta tafi kai kayan
siyarwarsu makwafta,Omar bacci ne ya daukeshi a Palo,nan ya shiga mugayen mafarkansa
kamar kullum,ya hada zufa,sai nishi yakeyi,iklas ce ta dawo da Sauri ta fada palon,tsugunawa
tayi kasan kujerar da omar ke kwance,addua ta shiga tofa masa,falaq da
nas,fatiha,ayatulkursiyyu,amanarrasulu,can taga ya daina mafarkin,dadi taji tace kai Ashe zan
iya rukiyya ma in na dage,
Omar ne ya bude idonsa cike da bacci,tashi yayi zaune, a hankali ya bude idonsa tare da
aza su kan kyakyawar fuskar iklas jinjina kai yayi,a ransa yana fadin wannan yarinya tana da
nacin tsiya,ruwa ta dauko masa da sauri,a ransa yace ikon Allah kaga shishigi.
A gabansa ta tsugunaa tare da kallonsa cike da tausayawa, Jim kadan tace pls sir ka fada
mana abinda ke damunka,inma baza ka fada min ba ka sanarwa ummi,in kuma baka son ummi
ta sani ka fada min zan boye ma sirrinka,
Maybe zamu iya baka shawara,bai dace ka zauna haka ba,in kuma kaki to zan fadawa ummi
mafarkan danaga kanayi da kuma time din Dana ganka a bakin shago,
Ido kawai ya zubamata yana kallonta har ta gama.Hannun iklas ya riko da hannu biyu ya
zaunar da ita a kujera,kinyi alkawari in na fada miki baza ki fadawa kowa ba?da sauri iklas tace
ae wlh sai in kai kace na fada,I mean sai da yardarka.Good muje tsakar gida to sai na fada
miki,cike da zumudi tayi waje.
Farar kujera ta mika masa ya zauna itama haka,har sun dauki kusan 20mnt amma omar ya
kasa bude baki yace komai,a zuciyarsa har ga Allah yana so ya fadawa wani matsalarsa ko zai
bashi shawara amma ya kasa,daga lokacin da yayi niyyar sanarwa wani sai ya kasa furtawa.
Gajia iklas tayi da zama ta kirashi cike da sanyin murya,ya omar kayi shuru,kallonta ya kara
yi ba tare da yace komai ba,sunyi wurin 30mnt amma yaki magana
Da kyar da sidin goshi ya cije ya furta bani da lfy a jikina,kamar ya?cewar iklas shuru yayi
mata,haka ta hakura ta kyaleshi tunda ya kasa cewa komai,ita kuma bata gane me yake nufi
ba.
Har ta mike zata wuce sai ta fasa ta dawo ta zauna inda ta tashi,tana zama ya zuba mata
ido daga bisani yace zan fada miki next time not know,
Zuciyar omar kuwa ko ya yi niyyar fadi sai yaji a cikin ransa ana gargadinsa,zuciyarsa na
tafarfasa,bakinsa yayi nauyi sai ya kasa fada.
Ya schl yanzu aji nawa kike?cewar omar dan kawai ya canja zance.suna hira su ummi suka
dawo,ummi sai Murna takeyi ganin iklas tare da yaron kirki umaru.
Bangaren sahar kuwa duniya take tsikara da tsinke,babu ta inda bata cokalar duniya,ta
manta ma da aure a kanta.
Mama da baffa sun yanke hukuncin zuwa gidan su sahar domin yin bikonta.
IKLAS na gidansu yau Sunday haka kawai taji yau ta tashi da masifa,ji tayi duniyar ta mata
zafi,kamar ta kunnawa kanta wuta,kowa ta tsaneshi,magana kadan sai ta balbale mutum da
masifa,
Ita kanta ta rasa dalili, mamakin kanta takeyi,omar na kallonta yanda takewa ummi da
suhaila,da safe ma sai da ta Zane suhaila akan kallon film.iklas tana kwance ta baje a tabarma
tsakar gida,omar na gyarawa suhaila farce yayinda ummi ke kitchen,haka kawai sukaji iklas a ta
fashe da kuka wiwi. Kuka take sharba sosai tsakaninta da Allah,Har shidewa takeyi.
Kallonta omar yayi da sauri ke kumafa?lfy kikewa mutane kuka,da ganinta yasan akwai
matsala,ummi kuwa fada ta kamayi me yasa zaka saurareta umaru tunda ta zama shashasha
ba sai tayi ba,yarinyar nan tun safe take bala'i! haka kawai ki dauki halayyar banza da wofi,wlh
bazan laminci iskanci ba.
Omar bai so fadan kaka ummi ba sai yaji haushi danme zatayiwa iklas fada,ai ruwa baya tsami
banza tunda iklas tana da juria haka kawai baza tayi kuka ba
A fili yace ummi ki kyaleta maybe tana da damua ne,pls ya fada da kalar tausayi,hmm ai dama
nasan kai umaru baka ganin laifinta biye mata kakeyi shi yasa take kara shagwaba.murmushi
yayi ba tare da yace komai ba,sai gomnati da ya kafe da ido wacce take ta sheshekar kuka
harma da jingina kanta ki?? Jikin bango tana ta yi.
Ranar haka ta kwana tana kunci da bakin ciki,washe gari Monday haka ma taje schl kowa
cin ubansa takeyi ba mutunci...
11:30am dai dai suna class taji kamar danshi a kasanta ita kanta ji takeyi kamar acikin ruwa
ta zauna,mikewa tayi tsaye ,Ai firgita tayi sosai,tabbas shine! jini ne,wato abinda takejin lbr
period, ta fara itama,abin yazo kanta.
Kunya taji yau kam ba zaman schl dole ta tafi gida,hijab din wata Christian