Showing 39001 words to 42000 words out of 191310 words

Chapter 14 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

wa yanan ki kwasa ina ganin ai zasuyi maki wanda naje dasu school ne wanan time wani ma sau daya nayi amfani dashi.
Ikon Allah ashe shi yasa ubangiji yace idan zakayi kayi don Allah idan zaka bari kabari don sa.
Nagodewa Allah da ban nuna komai ba duk da raina ya baci amma na tsaya nayi mata abinda take so a dakin.
Don kayana na yayan wani da wance masu tsada da kyau sun fi kalla goma wai duk ni kadai keda su tace min.
Na juya kaina a sunkuye ina fadin nagodd tace kai haba dai da baki nan ma ai duk a nan zan barsu saida hjy ta bayar dasu ga wanda take so.
Jin dadin kyautan yasa na ranan harda dakin ta na gyara mata da zuciya daya sai dai ta dawo ta samu dakin a gyara na gyara mata ko ina.
Nayiwa kawar mami kitso haka yaja hankalin sauran matan suke ta kwadayin in masu suma sai naji mami tace su bari a dawo Abuja don tare dani zata tafi.
Wani dadi naji sosai a raina jin mami tace dani za a tafi abuja din garin da nake jin labarin shi yau gani zan tafi cikin sa duk da nasan ba fita zanyi ko ina ba amma dai zan karasa ince ai na taba zuwa.
Tun da naji na fara shiri nima duk da naji Nuriya ta fadi ba dadewa za ayi a can ba nima kaya kala biyar na zaba daga cikin wa yanda ta bani ranan.
Naso sai na nunawa mami kafin inyi amfani dasu hakan bai samu ba don busy da mami take a ranan .
Bata da lokacin kowa har kanta ma da tashigo zata fice daga gidan ko ace ana mata sallama.
Sai ya kasance ina daki ko ina wurin su mama kande sai idan zanwa mami din wani abinda ya shafi rayuwan ta za a kirani.
Dan taron da akayi a dan kwana biyun dana dawo kauyen mu a gidan mami yasa na koyi wasu abubuwa da dama a furin jama,an da suka cika gidan.
Su kansu yan mata gidan mami suna ta kansu ne yanzu kowa na shirin tafiya saidai na kula cewa kamar ba wani shiri tsakanin su da yar mami din Nuriya don ban faye ganin su a tare ba.
Ko banza duk tafisu aji da kyau sosai ga wayewa da tsari don ko maganan ta abin koyone.
Washe garine za ai tafiyan inda wasu zasubi jirgi wasu kuma a mota zasu tafi inda ina cikin wa yanda zasubi mota da farko.
Amma mami tana duba list din lokacin ina dakin take fadin ban yarda abar zeey nan ba idan mun isa can waye zai kula damu kafin su iso sai dai a cire sunan wani a sakata cikin tawagan da zamu tafi.
Wayyo Allah na ashe in Allah yasoka tsuntuwa yake maga ko a dakin ka yau nice wai zan shiga jirgi tunda mami ta furta ai kamar na shiga ne in Allah ya nufa.
Karfe shidda yai muna a filin jirgi ranan nasha zagi gun yan matan mami don tafiyan nan da mami tayi dani a jirgi tare da kawayen ta da yaranta dama wasu daga cikin dangin su.
Koda muka isa can motoci muka samu sunzo daukan mu nidai basai na fada ba don bakauya na koma a cikin duk da dai kowa yana harkan gaban shine.
Amma hakan bai hana tsaraguwa ba a cikin su da rakubewa a guri daya tunda ba wanda ya sanni ko nasan shi sai mami da yaran ta sukuma bata kaina sukeyi ba.
Duk da akwai yan aiki irina kalian da wasu sukazo dasu daga wasu wurare sai dai hakan baisa na mamesu ba ina falo ko da yaushe don kada mami ta nemeni ban kusa kamar yadda naji ta fada kafin muzo.
Haka komai ke tafiya a tsare kamar yadda suka tsara abinsu gwanin ban sha,awa sai kallon mamaki nakeyi maza da mata ana ta cudanya a guri daya ba wanda ya damu da hakan .
Da kauyen mune ai da hakan ya zama abin magana a gurin mutana amma nan ba wanda ya damu da hakan .
Wai washe garine za ayi rantsuwar su mami din tunda muka iso wasu maza sukazo gidan suka fita tare da mami da yaranta manyan mazan biyu.
Haka yasa kadaicin rashin gabnin su mami a gidan ya dameni na dawo katon falon na zauna tare da wasu mata suna ta hiran su nidai sai sani lokaci nake dan jin hiran da sukeyi din.
Ina kallon duk mai shiga da fita don na jawo kofan da muka sauka a cikin hikima na zare key din kofan ina ji daga inda naje zaune ana tambaya na kyalesu.
Don ba wanda zai daukacewa nice na kulle kofan sai dai da mutum yazo ya murda yaji a rufe kofan yake ya juya inda ya fito.
Har masu tafiya a mota suka iso gidan ya kara rikicewa da hayaniyar jamma, a haka yasa na fito daga cikin falon na dawo waje na zauna.
Balle tun isowar ya matan suke aika min harara da warning ya karasa na gudo daka ciki na dawo wajen gidan.
Nan ma motocine ke faman shige da fice tun ina aunawa a raina ince wanan yafi kyau a, a ta dazun tafi har na gaji na zubawa sarautan Allah ido.
Can naga dawowan su mami hakan yasani mikewa tsaye daga inda nake zaune ina kallo na nufo wurin motar nasu.
Sannu da zuwa mami na fada daga bayan ta hankalin ta naga daddy su siyama jikokin ta suna magana.
Hakan bai hana mami dan juyowa tana amsa min gaisuwan ba ta juya taci gaba da maganan da sukeyi na juya zan bar wurin .
Sai kuma ta juyo tana fadin zeey karbi jakkan nan nawa ki rike min nazo da sauri na karba na ja dan nisa dasu na tsaya.
Sun dan gama magana ta fara tafiya yana biye da ita yana fadin amma mami sai naga kamar dai bayanin farkon nan shine shawaran bi koda yake barin gashi Jafar din duk da ban san inda ya shiga ba.
Kuje kuyi shawara dai zan dan shiga inyi sallah kafin wani abu ya dauke min hankali kuma ta fada ta fara tafiya makarrabanta suka biyo bayan ta ruuuu dasu.
Nima binsu nayi da kallo ina mamaki duk wanan taron haka don mami akayi shi haka ?
Naji tace on Allah ku bari inyi sallah yanzu zan fito ta nufi kofan dakin da nake zaton shine nata wanda na riga dana rufe tunda na fahinci hakan.
Mami ai kofan a rufe yake wata ke fadi daga gefenta lokacin da hjy ta murda kofan dakin da zuman shiga dakin..
Tun dazun ai dakin yana rufe an rasa inda key din yake da dan mamaki ta tsaya tana juyowa kafin na karso ina fadin ga key din mami a hannu nice na rufo kofan dazun.
Ok zeey key din yana hannun ki ashe thank god wallahi yarinyar kirki shaf na manta da zan fita in rufo dakin.
Da sauri na ciro a cikin aljihun dogon rigan dake jikina tunda ta dan jaye wurin na gane nufin ta na isa da sauri ina bude kofan.
Juyawa mami tayi tana fadin don Allah a dan jirani in fito tasa kai tsshiga tana fadin zeey shigo ki hada min wanan maganin nabi bayan ta muna shiga tace don Allah rufo kofan nan in huta hakana.
Ki duba akwai magani a cikin jakka ban samu shaba da safe na fita take fadi tana shiga bandakin.
Maganin na dauko daga cikin jakkata don nasan shi na saba hada mata na balla daidai yadda take sha na dauko goran ruwa mara sanyi dake dakin na a je akusa.
Daidai tana fitowa ne ake buga kofan taja tsuki tare da fadin mutanen nan idan nabita nasu bana samun sallah ko azahar ban samu yiba yau balle la,asar ga lokaci na shigewa.
Dukan kofan da aka karayi da karfi take fadin wai waye zeey bude kofan idan maishi ya shigo yaga ina sallah dole yajira idan zai iya.
Kofan na nufa na bude daga ciki aka turo ana fadin haba mami kin fita tun safe kin dawo kuma kin shige kin rufe kofa.
Aisha yar mami ke magana tana shigowa dakin a cikin shagwaba idon ta ya sauka kan mami dake kabara sallah kafin ta juyo tana kallona tana fadin.
Tare kuka fita ke nan da mami din kai na girgiza bakina kuma na fadin ina nan gida ina falo zaune na bata amsa.
Wuri ta samu ta zauna tana maida hankalin ta furin wayan ta yayin da na shiga gyara dakin don wanan daman na samu a yanzu tun zuwan mu garin..
Har mami ta idar da sallolin dake kanta ta juyo tana fadi Esha ya akayi ne wai ma kunci abinci kuwa ?
Zeey kinci abinci ita dai wanan din nasan halin ta balle yau taga wanan taron haka a gidan nan ?
Kaina girgiza daga inda nake tsaye ba tare da nayi magana ba kina jiran me wanan yarinyar da gidanci kike wallahi ga abinci nan ki tambayi safiya mana tunda ta iso idan baki san wanda zaki tambaya anan.
Waya ta dauko ta kira wani layi aka dauko ku kawo min abinci na mutum uku a hada komai a ciki ta fada.
Tana kashe wayan tare da jan tsoki kafin Aisha ta ce mami gobe fa ni dinner kawai zan yi attending.
Kina haukane gaba dayan ku da tan uwaki zamu tafi don duniya ta san ku ta fada sai yarinyar tace but mami kinsa, , ,
Hannu ta daga tare da fadin ban son korafi idan na fada kinsan iyakar maganata ke nan aka turo kofa wace ta kirane dauke da abincin wata hamshakiyar hajiya zakace ba zatai bara gidan kowa ba don bunkasanta sai gata itacs mai kasowa mami abincin .
Bayan ta aje suka dan tsaya magana da mami nidai duk sai naji na takura a cikin su don Aisha ita tana dawainiya ne da wayanta bata ma saurareb su.
Can mami ta juyo tana fadin zeey zuba muna abincin muci ko ?
Matar ta juyo tana kallon daidai lokacin dana tashi tana fadin wanan yar ina kika samotane don ban santa ba gaskiya.
Yata ce ta bata amsa kai tsaye tana jawo plate din abincin dana aje mata a gabanta inda ta idar da sallah.
Kije ki lissafa min matan nan da suka zo da yamman nan za a kaisu masaukin su idan sunci abinci tafadawa matar.
Yan kaduna ko na wani gari eh toh zaki iya lissafo min group group daga nan ki kiramin safiya tazo.
An gama hjy ta fada tana fita daga dakin Esha aje wayan nan ki dauki abincin nan kici ta fadawa yarta.
Ke kuma zuba naki idan kina zama da yunwa zaki jawa kanki matsala ba ruwana tana kai abinci a bakin ta.
Zuba wanda nasan zai isheni nayi na dauka zan fita daga dakin take fadin ina kuma zaki dawo ki zauna muci a nan .
Aka turo kofan yaya Mamud ne daddy su siyama ya shigo dakin da sallama ta karba mai tare da fadin har kun dawo ke nan yace .
Eh mami an samu inda ya dace saidai kudin kusan duk dayana ne ma mamud kasan kudi ba matsala bane ai a dai samu inda ya kamata din shine abu yanzu.
An samu mami kuma danki yace a tura mai ko nawa ne kudin zai biya munyi waya dashi ban samu ganin shi ba.
Ai da ya barshi tunda akwai kudi a hannu na don gwaunati ta bamu dan kudi a hannun mu ai.
Sun dade a dakin suna magana shigowan anty safiiya dakin yasa yafita ni dai ins zaune cikin su a tsawale.
Bayan na gama na fito na barsu tare da anty safiya din suna magana kayan abincin na kwasa nakai kitchen inda ake tarawa.
Nafito da zuman komawa falo in zauna muka hade da anty Rufaida wani irin shock naji lokaci guda saida na dan ja baya don tsoro.
Yar iska masuwa mutane asiri kin dauka ba wanda yasan abinda kukewa mami daga ke har wace ta kawo kine gidan.
Mu zuba dake a gidan nan ki gani idan zaki sha ruwa ya fada maki a ginan nan bakince kun iya mallake mutane ba ku.
Duk da ban gama fahintar inda zancen ta ya nufa ba na dan gane wani bangare na zancen nata kadan.
Tana fadin haka ta juya tabar wurin ba anty rufaida ba gaba dayan su yan kaduna dana sani a gidan wani kallo na kyamata suke bina dashi .
Na kulla da hakan ne idan sun hangoni sai inga suna kallona ana gulmata ma,ana dai sun sani a baki sun tsargeni ke nan a yanzu.
Wanda bansan wanan dalilin ba kuma banda wanda zaimin bayanin hakan sai kawai na fara kama kaina da kowa fiye da dacan baya dan dama anty salma idan mun hadu ba wanan kallon raini ko wullakanci sai dai idan na gaishe tace zeey din mami ke nan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA












🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅




1️⃣3️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA




YAN UWA FATAN ALHERI A GAREKU KO DA YAUSHE UBANGIJI YASA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA YA TSARE YA KARE MUNA IMANIN MU A DUK INDA MUKE AMIN.

YAR UWA KADA KI DAUKI HAKKIN WANI KARAMIN ABUNE KI GUJI CIN HAKKIN DA DAUKAN ALHAKI WASU MAI IMANI A ZUCIYA TA GANE MAI NAKE NUFI NAN KIWA KAN KI DA KANKI HISSABIN IMANIN KI TUN A DUNIYA.


DARI UKU NE NOVEL KI BIYA KI KARANTA CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA NAUYI KOWA BA A KANKI, , , , ,




Yau gidan ga baki daya ya kicime da shirin fita zuwa wurin taro duk da tun cikin dare an kwashe baki a gidan an kaisu hotel din da aka kamawa mutane.
Hakan bai hana gidan cika ba da wa yanda suka kwana a gidan basu samu zuwa hotel ba din mutane sunzo da yawa sosai.
Ban bar dakin mami ba tunda safe dana shiga don a falo na kwanta abina bayan na gama yiwa mami duk wani abinda zan mata a lokacin.
Tunda asuba kuma na tashi na yi sallah ko alwala a famfon dana gani wajen gidan na fita nayi alwala duk wanda ya wuce a cikin mazan dake haraman zuwa sallah asuba sai ya dan kalleni.
Nidai na gama na shigo ciki na shimfida dan kwalina nayi sallah daga gefen da mutane ke bi a lokacin.
Na idar na dan dade zaune gurin ina kallon masu shige da fice ina dakon mami ta idar don nasan a lokacin tana saman salayan ta tana zikiri ga ubangjin talikai don wanan dabi,an mami ce hakan.
Can na daidaici ta gama a lokacin na mike zuwa dakin don shine aikina kuma don shi akazo dani watau kula da al,amarin mami din.
Sai kuma yanzu da nakan dan wa yarta wasu hidima a gidan don bata da damuwa ko ci fuska gata bata shiga lamarin kowa halin su yana yanayi dana anty salma itama saidai salman wani lokaci zumace ita ga zaki ga harbi idan halinta ya tashi.
Da sallama na tura kofan na shiga sai dai nayi mamakin ganin su yaya mamud a dakin lokacin shida wanan bakon danta da yazo.
Da gani wani maganan suri suke a tsakanin su a lokacin hakan yasa na juya da sauri zan bar dakin har su fita don ban san shigarsu ba lokacin sai ganin su nayi kawai a dakin.
Muryan mami ke fadin shigo mana zeey ina kika shiga ne tun jiya da dare ban sakaki a ido ba na dauka nan zaki kwana ai tunda dakunan duk akwai mutane.
Yaya mamud ya juyo yana kallo na shiko dayan ko dago kai baiyi ba ya kalli inda nake na fara takowa ina fadin.
Falo na kwana mami na bata amsa kai tsaye kafin in karasa shiga dakin na durkusa har kasa gaban ta yadda na saba gaida ita kafi in jiyo i gaidasu daya bayan daya na mike.
Kada ki sake kwana a falo baki gudun sanyi ya kamaki ne ko wani abu ya sameki nan.
Nace mami akwai wa yanda muka kwana dasu ai koma dai menene amana kike a gareni ta fada ta juya tana fadin mamud kana da son gardama.
Nikan nasa kai na shige ban daki don in fara gyara nan kafin su gama su fuce in gyara dakin ga baki daya.
Har na gama da bandakin na fito suna cikin dakin basu fita ba haka yasa na koma falo na zauna har su fita .
Ina nan zaune falon saiga Rufaida ta fito daga dakin da suka kwana tana ganina tace yauwa ke zo nan ki dibo muna ruwa a waje.
Tashi nayi na karbi bucker

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login