Showing 42001 words to 45000 words out of 191310 words

Chapter 15 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

din a hannun ta na nufi hanya tana fadin kiyi sauri don gaba daya dakin zaki debo muna ruwa muyi wanka.
Ni dai na tafi bance komai ba na diba a mayawa na uku ne na samu masu aikin break fast suna wanke kayan miya dole na tsaya jiran su.
Don gaba daya ruwan gidan ya tsaya ba,a san dalilin haka ba sai ga Rufaida ta fito tana fadi ke karamar yar iska ko ?
Tun dazun ki debowa mutane ruwa kin tsaya iskanci dama ai tsiyan matsiyata ke nan basu iya samun arziki ba sai su ganshi a banza.
Excuse me ya fada daga baya ta inda take tsaye da hannuwa saman west din ta sai masifa take dani ni kuma na juyo ina fadin nba tsayawa nayi ba wa yan nan na sama suna aiki wurin.
Maza ki debowa mutane ruwa ko ranki ya baci shine taji ana ce mata excuse me ta dan juya don jin muryan wanda tayi a bayan ta.
Da sauri ta jaye mai a hanyar da tai banga banga tana masifa dani daga saman step din.
Wurin security din shi ya nufa yana saye da farar jallabiya kal mai sulbi a jikin sai kamshi ke tashi har inda muke saida kamshi yakai ga hancin mu.
Jin ta gaida shi bai aksa ba ya wuce ina jin matan dake wurin na fadin wanan duk cikin diyan hjy yafisu kyau da kwarji saidai shi din miskilin karshe ne sosai.
Sai lokacin na dago kai na dan saci kallon shi kafin in koma kallon Rufaida data suma a tsaye wurin da take kan kallon shi.
Dauko ruwan da ta farga nayi harna zo gabanta ina jin tana sauke wani irin ajiyan zuciya na shige ta biyoni a baya.
Daga ban dakin dana aje ruwan ina jin tana fadin kai yanzu naga hero a waje ashe fitan danayi bana banza bane tunda har na samu yai min magana yau.
Wai me kike nufi Rufaida kin san dai alkawarin su daddy ai ko tace ina ruwana da wani alkawarin su can in dai na samu ya kyasa min.
Da wanan cece kucen har na fito daga dakin suna kanyi na barsu nan dakin mami na nufa kai tsaye daga nan don in gyara.
Ina shiga ranan ne karo na farko da mami tayi min fada kan aikinta don ina sallama tace zeey mena kawo kinan kiyi tun dazun kin shige ba a ganki kin san zan fita yau da wuri.
Me ke damun ki yanzu ne tunda kikaje gida naga kina son ki sukurkuce min fa sai ayi ta neman ki kiyiwa mutum abu baki san kizo don kanki ba.
Mami kiyi hakkuri ba wucewa nayi ba dama daga bayana naji ana fadin is OK mami tunda tazo din.
Muryan ne ko mai maganan abin kallo na juya don ganin mai magana suka karaso tare da jamal, sai jamal ke fadin .
Wata kila wani ne yasa ta aiki don naga tana diban ruwa a waje zuwa ciki cikin harshen turanci yake magana shidai tun maganan farko bai kara magana ba ya samu wuri ya zauna.
Wa kike diban wa ruwa mami ta juyo tana tambayana tare da tsureni da idanuwan ta a kaina.
Anty Rufaida ne tace in diban masu ruwan wanka dukka dakin shine na tsayayi dama na bata amsa.
Wai mai Rufaida take nufi ne akan yar nan mami ta fada da hausa barta zamu hadu bari a watse gurin taron nan in mata tsiya.
Kayan dake saman gadon na fara tatarawa ina nadewa na tara gefe guda sun dan dade dakin don maganace mai muhinmanci sukeyi a lokacin naga an aiki jamal mami na fadin don Allah kada ka tsaya don munyi waya dashi yanzu.
Tare suka fita lokacin mami ta fara shiri tana fadin in miko mata wanan in bata wancan har ta shirya cikin wani rantsantsen lace da akai mata dinki ya sauko zuwa gwiwan ta.
Ga wani sarka da na fitar a cikin wani gida mai kyau da dauka ido ta nuna min yadda zan saka mata shi.
Ta tsaya a gaban mirrow dakin tana gyara kwalliyan ta da kyau da sauri na karasa gyaran dakin na share don ta fita zuwa falo.
Dakin ya koma tsab na saka mai kamshi gadon yayi kamar ba a kwana saman shi ba lokacin.
Gaba daya mami da yaranta har anty Aisha suka shigo dakin tare da ita sun sha ankon farar shada sai maiko jikin shadan da motsi yakeyi sun saka mami a tsakiya sai Aisha ce da wanab bakon da ban san dunan shi a baya suma magana sukeyi a cikin rada kamar Aisha zata shige mai jiki.
Ganin yadda suka shigo suna magana haka yasa da sauri na zo fita sai muryan jalal ke fadin ke yarinyar hajjaju ana magana dake fa.
Key ya mika mai yace ya bani shi jalal din ke min bayani wai inje in gyara mashi dakin shi yana bukatan gyara.
Na rusunan na karbi key din harna juya sai kuma na juyo ina fadin ina dakin yake yaya ?
Kwatance jamal ya fara min naji yaya mamud na fadin jeka nuna mata dakin mana har zan fita mami tace ki rike key din dakin nan guda tana nuna min kofa.
Na tsaya na cire na tafi yana waje yana jirana har muka nufi wani part ya nuna min da hannu.
Daga kofan shiga part din na hango wasu irin zaratan maza kartai dasu su shida kowa ya saka bakaken kaya a jikin shi.
Tsoron sune ya kamani da fargaba na nufi wurin na gaidasu na sa key ina bude kofan kafin in tura da sallama in shiga.
Bin ko ina na falon da nagani nayi da kallo komai yana a tsare ga wani kamshi yana tashi a dakin ta ko ina kada in tsaya kallo wani ya sameni haka yasa nasa kai zuwa kuryan dakin .
Nan ma nasha kallon saidai ban yarda na tsaya ba ina kallo ina abinda ya kaini dakin ko ina sako da lungun dakin saida na sharo shi tasa na goge kafin in fito sha daya saura.
Tun tun karowana part din da muka sauka naji gidan yai min tsit babu hayaniya har haraban wajen gidan babu wani motsi sosai kamar yadda na barshi .
Babu kowa a part din sai motsin masu aiki da nake ji a kitchen din gidan tsayawa nayi ina tunanen sun tafi ke nan inda zasu ashe ?
Ke nan na dade a dakin ina gyara ban sani ba har aka wuce akabarni sai kuma naba kaina amsa da fadin ke yar aiki wazai kaiki wurin taron manya haka.
Wanka bake bukata don haka na nufi dakin mami tunda can kayana suke tunda mukazo ina shiga na rufo kofan dakin na shiga ban daki a gurguje da tsoro nayi wanka har na shirya na fito na rufe dakin.
Kitchen din gidan na nufa don yunwa nakeji lokacin sosai gaida masu aikin dana sama nayi ina tambayan abinci.
Daya daga cikin su mai hausar gwarawa take fadin abinci yanzu sun cinye komai nasu sun tafi ai sai ta hada da yaren su kuma naji daya na mata yare sai matar tace in tsaya ta debo min akwai wanda suka ajewa wasu basu zo ba.
Suna ta yaren su har ta hado min na karba ina godiya tare da dawowa falo na zauna naci saida na koshi na kwashi kayan na mayar kitchen din da zuman in wanke da sauri matar tace ka bari wanan zaita wanke ai.
Nikan na fito na barsu don jin abinda ta fada na zauna a falon ina kallon tv dake aiki ganin yadda aka bar falin na mike na gyaro ko ina na gidan ban samu kaina ba sai daya da wani abu.
Alwala nake daidai lokacin dana fara jiyo hayaniyan dawowan mutanen gidan nayi alwalana na shige ciki a falon kamar yadda nayi da asuba ko wanan ma nan na tsaya nayi.
Suka fara shigowa daya bayan daya kowa a gajiye sai shigowan anty Aisha na mike da dan sakin fuska nake gashe ta.
Ta amsa min tare da fadin a, a yarinyar mami yaya bakije gurin taron bako kinje banganki bane tana fadin tana magana nidai nayi murmushi kawai.
Har ta danyi nisa ta juyo tana fadin zo zo zo yarinyar mami tana miko min hannu na nufi gurun ta tare muka shiga dakin bayan ta bude ta fara yarda jakkan hannun ta saman gado na dauka nakai wurin filon na aje mata shi.
Taje help me to remove dis cloth don Allah tun dazun duk na gaji dasu a jikina ja min zep please ko zanji dadi haba wanan wahalan yai yawa.
Naja mata zip tana ta tsuki da fada bata tsaya komai ba ta kwabe kayan ina kawar da kaina gefe ta fada ban daki tare da barin kayan a watse.
Tattara kayan na farayi ina nadewa kafin ta fito wanka na gyara ko ina na fito haka yayi daidai da shigowan mami gidan yan bambadanci suna bayan ta suna fadin saike hjy maryam mace mai kamar maza mata a gidan Alh ma,azu gin sun buga sun barki Allah dai yajikan maza maza sun kwanta.
Ko yanzu yasan baiyi zaben banza ba yabar baya a duniya uwar zaratan maza kece uwar gwaunan gobe kece uwar shugaban kasa, .
Wata ta karbe da fadin kece uwar manyan duniya ga gobe gaba sallama baya sallama yar manyan mutane.
Nikan na suma wurin kallon yadda ake masu barin kudi kamar ba neman su akeyi ba.
Zama mami tayi yayin da kawayen ta suka kewayeta ta ko ina ni sai lokacin ma naga wasu da ban gansu jiya ba.
Take falon ya cika da jama, a ta ko ina babu masaka tsunke a gidan wuri ya kaule da ci dasha ina labe daga kofa ina kallon ikon Allah don ni ban taba ganin bukin manya ba irin haka.
Wasu nacin abincin wasu na haraman sallah wasu kuma suna mayar da magana mai rabon abinci suna rabo kungiya kungiya.
Nama girman shi yakai dunkulen hannun mutum don girma duk nau,in da kake so na abunci shi za a baka a wurin.
Daga inda nake rakube naji mami ta fara kiran sunana da sauri na amsa da gani mami na isa guri ina gaida ita.
Gaba daya mutanen dake gurin sun zuba min idanuwan su hannu mamu ta mika min na isa wurin ta da sauri tajawoni tana rada min in shiga daki in duba cikin turamen zanin dake zube gefe a kasa in dauko guda biyar in ba matan dake mata kirari .
Na amsa ina gyada kai na matsu in bar wurin daki naje na bude na dauko kayan kamar yadda taimin bayani nazo dasu falon kowa ya saka min ido.
Ina takowa da zannuwan a hannu na daya daga cikin matan da akace in kawowa tana kyala ido ta fara fadin kaga inda kyau asali yake farar mace alkyaban mata.
Diyar hjy takawan ki lafiya dayan tace fari kun gadane ba ku ba shagon maida baka fara kaga jinin larabawa asali irin gado bana gada ba.
Yarinya sai gidan gwauna ko minister minister ma mai fada aji irin uwarki ba muna minister ba akoma gefe ba office .
Dayan ta karba da fadin haka yake don yau mun sheda mun gane bambamcin ayyah da tsakuwa a bainan jama, a.
Nidai har jiri nake gani don idanun da aka watso min a falon na nufesu na mika masu zan juyo mukayi arba da yan matan Rufaida da Nazifa tare da wasu mata a zaune suna magana kasa kasa sai hararana sukeyi.
Na raba na koma dakin mami na gyara wurin dana dauko kayan na fito har lokacin sai kirari sukewa mami din.
Ance massadan ka fadawan ka a inda na tsaya idanun su ya rufe basu san ina wurin tsaye suke gulma akan mami.
Wai haka duniya yake ai gashi bai gina kowa ba sai matarshi da diyan shi kawai ya inganta rayuwan su.
Har mami tana daga kai dama ba,a san asalinta bane ko yar waye yar hakimin kauye kawai da ita yanzu ta samu duniya taba ganin kamar tafi kowa.
Jifa kai duniya ina zaki damu kan hassada wai kuma sun zo ne har Abuja dalilin ta don tayata murna fa kuma suka koma gefe suna gulman ta.
Kafin dayan ta dago kai mu hada ido ina kallo ta zuguri dayan matar dake magana ta dago mukai arba na watsa mata wani kallo don girman ta ya gama zubewa a idona ko tunda na shedata tana zuwa wurin mami ko a kaduna.
Tun yamma nake ta kallon ana shiri muna idar da sallah mami tayi kirana muka shige dakin da wasu kawayen ta biyu.
Shiga ta alfarma mami tayi ina ciki sai faman miko muna wancan mayar da wanan dauko muna wancan abin ko mami ta ce zee ina abu kaza din nan ?
Haka dai har mami ta shirya wai dinner za, a tafi a wani katafaren hotel nan cikin garin Abuja.
Mami kan hankalin ta ya dauke bata takan kowa a gidan don uzurin gaban ta yau data zauna za a kirata gefe da magana kus kus.
Har aka fara tafiya gurin dinner din ina kallo su Nazifa da Rufaida da su Rubby suka fito sai wani shakiyanci sukeyi a tsakanin su.
Wanan na fadin yau kan akwai babban kamu don bazan fito ba sai na sace zukatan mutane da yawa .
Wanan ta daga tayi wani juyi tana gwada tafiya har suka gama iya shegen su suka fice gidan sai wani yauki da yanga suke yi nasan harda kari don inji haushi.
Saboda ina jin Nazifa na fadawa wata tsohuwa da ban santa ba a cikin dangin su tsofi da mara gata su zauna gida ba, a zuwa daku taron manya don darajan wasu baikai can ba .
Tsohuwar dai tayi mata dakuwa da hannu ta fita tana dariya ajiyan zuciya na sauke bayan fitan su falon ina wasa da yan yatsuna sai ga anty salma ma sun fito da wasu yan mata guda biyu ina ganin su nace anty salma sai kun dawo don dai tace inzo mu tafi.
Tunda nayi dan kwalliyana a lokacin amma sai ta daga min hannu kawai suka fita na koma na zauna ina tunanw kala kala a raina.
Can an dan dade sai ga anty Aisha ta fito tana tako daya daya tana waya na dago ina fadin anty Aisha sai kun dawo .
Ta juyo tare da fadin yarinyar mami baki tafi bane daga haka ta sa kai ta fice a gidan bayan fitan ta naji gaba daya zaman wurin ya isheni.
Don haka na yanke shawaran fita haraban gidan in sha iska duk da darene amma wajen kamar rana don hasken da ke akwai a wurin.
Wuri na samu na zauna gefen flowers ni daya sai tunane barkata da kalle kalle nakeyi kafin kamshin turaren nan da tun rana dana aiki a dakin yake a jikina badon na cire kayan na daina jin shi a yanzu ba.
Ta dan nisa kadan yazo ya wuce ni zuwa wurin motar shi lokacin ne na san da mutane a wurin sai ga bodyguard din nan nasa dana gani da rana sun taso zuwa wurin shi.
Kallona ya koma can na samu abin gani da zagi a raina ganin yadda suke mai kamar ba mutum ba dan uwan su.
Mota ya shiga suma suka shiga dayan motan bayan sun rufe mai suka tayar da motar hasken motar su ya haskani sosai inda nake nayi saurin dukar da kaina kasa.
Shiru shiru motar bata tashi ba na dago kai da zuman in kalle su sai ganin mutum nayi a gabana yana fadin cikin harshen turanci boss yace ki zo.
Na nuna kaina tare da fadin ni yace eh ya juya na mike na bi bayan shi zuwa wurin motar tun kan in karaso aka bude motar ina zuwa naji ance shiga mu tafi.
Murna zanyi ko mamaki duk babu daman wanan saboda tsoron daya rufeni lokaci daya banda zabi na shiga gefen da aka bude min din.
Wani sanyi da rabane ga kamshi ya dakeni lokaci daya sai dana zauna nake fadi ina wuni a cikin hausa ban sani ba ko ya amsa min don an rufe kofa a lokacin.
Har muka kai wuri ba wanda yai magana a motar ga wurin da gidan akwai nisa sosai a nawa ganin.
Wurin ya cika da motoci da ababen hawa ga jama, a wasu a wajen wurin sai security kala kala dana gani gani da tsoron yan sanda tun a kauyen mu.
Motar ta samu wuri driver ya tsaya daga inda muke muna jin magana da kidan dake tashi a cikin wurin.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login