Showing 180001 words to 183000 words out of 191310 words

Chapter 61 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

da dai ba wani sakin fuska amma zai shigo mu gaisa ya tambayeni idan banda wani matsala a tare dani ko kuma idan ya dawo wani lokaci ko dakinsa baya shiga zai shigo har dakina yayi min ya gida tare da tambayan badai matsala ko ?
Idan muna dashi zan fada mai ko idan muna son wani abu zan dan sake infada mai komai sai yin hakan da yakeyi ya dan jawo muna kusanci a tsakanin mu.
Inda nakan shiga part dinshi da safe in gaidashi kafin shi ya shigo nawa part din da sunan gaisawa dani.
Bangaren taju kuma yanzu ba kasafai nake ma ganin sa cikin gidan ba sai can ba a rasa ba zamu dan hadu dashi sama sama muke gaisawa dashi din ba tare da wani sakin fuska ba ga kowan mu.
Kwaliya kuma irin na daukan hankalin maza kamar yadda fadila tace na jajirce gutin yinsu iya gwargodon hali ina bakin kokarina saidai kallo daya zai min ya kawar da kanshi gareni.
Sai wanan abin kuma ya fara damuna a zuciyana mutum kamar dutse shi baya ko sanin na ina mai wani kwaliya a hakan.
Kamar yadda yace indinga nunawa udan baki sun shigo hakan na daure tun ina jin kunya har na fara daina kunyanshi ina nuna muna normal dashi ai a zaman mu .
Don a gaban baki mu har wasa da dab dariya zamuyi kamar ma,aurantan gaskiya ne ni da shi ai sai idan sun tafine mukoma kamar yadda muke baran baran.




ZAINAB IDRIS MAKAWA






ws🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅




5️⃣5️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA




FATAN ALHERI GAREKU HAR KULLUM MASOYANA TARE DA FATAN GAMAWA DA DUNIYA LAFIYA ALLAHUMA AMIN.




YAR UWA BAZAN GAJIBA WURIN TUNATAR DAKE SAUKE NAUYIN HAKKIN WANI A KANKI DON ALLAH IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WANI AKANKI NAGODE IDAN KIN FAHINCI MAI NAKE NUFI.

Rayuwa mai dadi haka rayuwan namu ke gudana a gidan har zuwa lokacin daya fara zancen komawa inda ya fito.
Ban dauki zancen wani abuba ni dai nasan ya share sati uku a kasan nan ban kuma san mr ya kawo shi kasan nan ba balle.
Iya ka dai nasan da cewa dan zunwan shi kasan yasa na dan saki jiki dashi don zaimun magana in bashi amsa ba tare da jin tsoron shi ba a yanzu, ko kunyar shi ba.
Inda shima kamar hakan yana mashi dadi yadda na dan fara sake jiki dashi din ba tare da nuna tsoro a garshi ba.
Don haka kawai tun ranan da ya mamud ya kawo su husna muka fita tare yawo dasu da halimatuna .
Sai hakan ya zama mai kamar jiki ina zaune kawai zai bugo in shirya mu shiga gari .
Inda a dan fitan da mukeyi din zai saya muna abubuwa mu dawo gida dashi sai dai duk fitan da mukeyi din bamu taba zuwa gidan mami har zancen komawan shin nan ya taso.
Zaki iya cewa banda zuciya don har yau ban manta da mami ba a cikin raina .
Ba hakana bane mai karatu mami ina jinta a wani bangare na zuciyana sosai ta yadda ba zan iya mantawa da alherin ta gareni ba har wanan lokaci.
Da yammaci ana gobe zai tafi ya shigo gidan ya sanemu zaune a falo a falon shima ya zube sabanin yadda yake idan ya samemu a zaune yawuce mu saidai mu gaida shi, ko juyowa bayayi garemu yake amsa muna gaisuwan mu.
Muna gaida shi ganin ya kai zaune ya zuben saman kujera tare da kai wuyan shi ga masangalin kujera ya nisa da dan karfi lokaci guda yasa duk muka sha jinin mu a falon don dama mu uku ne zaune a falon.
Zainab naji ta ambata a cikn wani murya dake nuna kasala a tare dashi har lokacin kanshi yana dage a yadda yake saman kujeran.
Yayin da idanuwan shi suke rufe har lokacin alaman lumshewa a dan sanyaye na amsa mai da na,am yaya hannu ya miko inda nake zaune din yana fadin zo ki min massage din kai.
Dan jim nayi kafin in juyo in kalli inda anty fadila take zaune daidai lokacin da take yunkurin tashi don barin falon lokaci guda.
Jin ban taso daga inda nake ba don ni ban ma fahinci mai yake nufi ba a lokacin yasa shi bude idanuwan shi ya sauke a kaina.
Babu kowa a falon dagani sai shi a lokacin don da hannu fadila tayiwa halimatu nuni da su bar falon har suka fice bai sani ba din idon shi dake rufe kanshi kuma dage a sama.
Bakiji me na fada bane ya dan fada cikin daure fuskan shi zubur nayi na mike ina fadin banji ba yaya .
Kizo ki tausa min kafa na da kai ki fara tausa min kafana tukuna ya fada yana mai da kanshi a yadda yake zaune da farko.
Mikewa nayi na fara takawa a hankali zuwa inda yake din a hankali kamar wace kwai ya fashewa a ciki lokacin.
Har na zagayo zuwa bayan kujeran saida na runtse idanuwana kafin in daga hannuna in dora a kan nasa a hankali na fara dan cakula mai kai din.
Wani irin shock naji a daidai lokacin dana dora hannuna saman kan nasa don taushin kan da kuma santsin sumarsa kamar na dan bature ba african ba.
A hankali na ci gaba da dan matsa masa kan ina jin yadda yake sauke numfishin shi shima kamar yana jin dadin abinda nake masa din.
Saitin goshinshi ya nuna min adaidai lokacin yana gyara zaman shi yana fadin ki tausa min nan gurin yana min ciwo sosai wallahi.
A raina nace yanzu da ciwo ya sameka ne kasan amfanina a gareka ko ko a fili kuma cewa nayi dashi sannu a hankali yace nagode.
Can naji ya sake wani irin ajiyan zuciya tare da fadin ki kara tausa min shi da karfi zaifi don ciwo yake min sosai.
Hakan yasa na takankare iya karfina ina dan dana masa saitin goshin nasa da dan karfi kafin inji ya rike min hannayen nawa lokaci guda yana fadin.
Ai sai ki fasa min goshi da wanan irin dannan da kike min a daidai lokacin kuma mukaji an shigo falon babu ko sallama.
Wanda haka yasa dagani harshi muka dago don ganin ko waye ya shigo a lokacin haka babu ko sallama tunma dai ni da naji kunyar yadda maishi ya same mu din.
Don sai a dauka ko wani wasan mata da mijine mukeyi a lokacin do yadda yake rike da hannayena a hannun shi.
Ba kowa bane sai taju tare da wani dayan security din shi suka shigo a lokacin idanuwan su kar akan mu tundai taju din da kamar idon shi zasu fado kasa don mamakin yadda ya samemu din a lokacin.
Ganin su baisa ya sake hannuna dake rike da nasa ba a lokacin saima kokarin zagayo dani ta gaban shi da yake kokarin yi din.
Ki matsa min kafana ya fada kafin ya sauke kallon shi garesu a inda suke tsaye di kamar an dasa su wuri daya.
Can na tsinkayi muryan shi yana fadin me kuke anan kun tsaya mi saman kai haka ?
Kamar wa yanda aka tsikara lokaci daya suka fara takowa zuwa inda yake zaune din ni kuma na kama kafan shi na fara murzawa a hankali lokacin .
Naji dayan yana magana duk da acikin harshen turanci suke maganan nasu na gane mai suke fada don zancen ticket din jirgi naji sunayi wai babu jirgin da zai tashi direct a gobe sai sun shiga na wani kasan an sauke su a can.
Tsuki naji yayi tare da fadin shi ba zai sauka ko wani kasa ba saidai su bari ranan da jirgin zai tashi suyi booking zaifi.
Yana fadan haka ya mayar da idanuwan shi a yadda suke mai da farko ya kara lumshe su a hankali.
Duk da ban dago kai ba nasan da mai kallona a cikin su don jikina da ya bani hakan lokaci guda yasa na dan dago kaina da yake a duke na dan kalli inda suke tsaye din.
Wani kallon tsana da ki taju din ke aika min dashi lokaci guda wanda yasa nayi saurin kawar da kaina daga inda suke din tsaye.
Daga haka suka juya dan barin falon saidana dan dauki lokaci ina matsa masa kafafun nasa kafin yace dani ki huta hakana nagode.
Daga haka kuma ya yun kura da niyar mikewa a daidai lokacin da nima na mike din muka dan gwaura kan mu da juna da sauri ya ja jiki shi yana fadin kiyi a hankali fa.
Nikan falon na bari gaba daya don a rikice nake sosai a lokacin tun wanan shigan da nayi ban kara lekowa falon ba sai washe gari.
Don dan tunanen dana fada yasa dana samu barci ban falka da wuri ba sai da gari ya waye tarrr, .
Wuraren takwas saura na safe aka buga min daki a hankali kamar maishi baison aji shi da mamaki na mike zuwa kofan na bude.
Anty fadilace a tsaye ina budewa ta shigo da sauri tare da mayar da kofan ta rufe taja hannuna zuwa bakin gado tana fadin.
Zainab kinji abinda naji jiya a gidan nan kuwa idan ba kunnuwa ke min karya ba wallahi tunane na ya zama gaskiya ke nan kan mijin ki.
Anty meya faru na fada a dan rikice tace wai kina nufin ke bakiji hayaniyar da akayi a gidan nan ba jiya duk saboda ke .
Ni kuma anty na fada ina nuna kaina a cikin mamaki da abinda ta fada din kaina.
Wai ke duk wanan hayaniyar kina nufin bakiji ba zainab wallahi fada sosai naji sunayi idan ma banyi karya ba zainab har djka naji wallahi a tsakanin su
Innalillahi na fada sai data kalli inda kofa yake tace cikin kashe murya wanan mai kama da mata din taju shine ke nuna kishi ki a kanki .
Ni meye ruwana dashi dan Allah na dai gane wanan mutumin baya kauna na sam a gidan nan don irin kallon tsanan da yake jifana dashi ko wani lokaci.
Ba zai kaunace ki ba don yasan kedin zaki iya canza mijin ki ga rayuwan da sukeyi a ko wani lokaci idan kuna kebewa daga shi sai ke a gidan nan.
Ke ni da farko har naji tsoro na dauka barayi ne suka zo muna saida na saurara na gane a cikin gidan nan muryan ke tashin kuma fada sosai naji a tsakanin su.
To Allah ya sauwaka na fada ba tare dana fahinci komai a cikin zancen nata ba takeci gaba da fadin wanan abin ya ban mamaki matuka wallahi.
Wata kila wani aikine ya hadasu fada don jiya naga sunzo mashi da wasu takardu a hannu su suna mashi bayani.
Zaisa su ambaci suna ki a cikin fadan su zainab ke yarinyace karama wallahi don magana a yanzu baida amfani dake sai nan gaba.
Baki na turo gaba ina fadin kai anty yanzu fa na girma nima ina da wayau kamar kowa.
Mikewa tayi tsaye tana tsuki tare da fadin ni bari in fita kada ya tsurani da farar safiya haka cikin dakin nan ya dauka gulma mukeyi.
Tana fita nikan ban kwanta ba na shiga wanka tunda gari dai ya waye tarr a lokacin na dan dauki lokaci a bayin don haka dabi,ana yake ina dan dadewa a cikin bayi idan na shiga.
Ina wanka zuciyana cike da tunane zancen da tazo ta fada min din sai cewa nake me ya hadasu fada hakane har da duka kamar yadda anty ta fada duk dai ba abinda ya shafeni bane don tare na gansu ai.
Na fito daga bayin ina tsane ruwan daya taba min kaina dagani sai dan tawul karami da daure gaba don dakina ne ko halimatu sai jefi jefi take shigowa inda nake .
Banyi sanyi a gwiwa ba don ganin ko waye ya shigo dakin a lokacin na dago kai da sauri ina kallon kofa da dan karamin tawul a hannuna.
Ar,ba mukayi dashi yana tsaye a kofan dakin bai karasa shigowa ba yake fadin ke me wanan matar ta shigo yi dakin nan yanzu.
Da sauri na dan kara kallon shi ina fadin wace mata ke nan yace wanan mai aikin nace abinda zata girka ta shigo tambayana.
Saida ya bini da wani irin kallo kamar yana zargin abindana fada mashi din don rashin yarda da hakan yace
Are you sure na daga mai kai kawai ashe bakin mu yazo daya da ita don itama data fita daga dakina ta same shi zaune falon sai data kadu tana gaidashi a cikkn tsawa yake fadin ina ta fito ?
Tace mai wurin madam ina son tambayan ta break fast ne ya bita da wani mugun kallo kamar na tsana ta wuce zuwa kitchen kai tsaye.
Abinda yasa nace hakan kuwa don akwai ranan da ta taba fadan haka a gareni a cikin wasa yasa na rike wanan kallaman nima a yanzu.
Fita yayi daga dakin da sauri ta hanyar bugo min kofar dakin da karfi da ganin sa a hasale yake dai a lokacin.
Nikan har na shirya ina mamakin hakan a raina duk dana shirya ban fito da sauri ba sai wuraren goma da wani abu na safe.
Da alaman har ya karya ya fita lokacin don kamshin turaren shi daya bari a falon wanda ke nuna ya shigo ya fita don wani lokaci da haka nake gane fitan shi gidan ko dawowa shi gida .
Zama nayi na karya kummallo nima ba tare da wani damuwa da kara bin zancen shi ba don na fawalawa Allah al,amarina da dadewa ko.
Ibadane dai akansa nake ko yaushe ina raba dare ina kai kukana ga Allah kamar yadda malam mijin mai zube da innan mu ke yawan tunatar dani yin hakan ko wani lokaci.
Sabbin masu gadi da security na forces ne aka watsa yanzu a gidan ta ko ina ban san da hakan ba saida fadila tazo tana fadi.
Banyi mamakin hakan ba don girman gida dama yaci ace akwai masu aiki wadattatu kamar hakan a gidan.
Kwana biyu tsakani suka bar kasa ya tafi ya barmu da tulin abi arziki a tare damu ta yadda ba zamu nemi komai mu rasa ba a gidan ko a waje.
Bai kira wayana ba tunda ya tafi har kusan sati uku da tafiyan shi gashi ina son zuwa wanke kai a saloon don yanzu na saba da hakan.
Gashi kuma fita bada yardab shi ba yana cikin gargadin da maizube tayi tamin kafin ta wuce hakan yasa na gane wanan dabi,an baida kyau.
Mace ta dinga fita gidan ta ba tare da sanin maigida ko umurnin sa tunda naji maizube tana faman jaddada min hakan ko yaushe yasa na rike wanan a raina sosai.
Don hakane nake faman jiran kiransa a waya don na fada mai ina son fita zuwa wurin wanke kaina da yake min kaikayi yana son wanki a lokacin.
Bai kira ba kamar yasan ina jiran kiransa sai bayan kwana biyu sai ga kiranshi ya shigo a wayana .
Banyi gagawan daukan waya ba don haka fadila ta koya min sai gab da zai katsene na daga wayan nasa da sallama a bakina.
Ke wata irin yarinyace wai a dinga kira baki daga waya sai ya katse sai naji yaja tsuki kayi hakkuri na fada a hankali .
Numfashi naji ya sauke tare dan ja kadan kafin yace ya kuke hope ba matsalan komai a gidan kowa kuma na aikinsa yadda ya dace.
Bamu da matsala na fada a sanyayye saidai wurun wankin kai nake son zuwa dama kuma sai baka kira ba in fadama.
Sai idan na kira zaki fita a wanke maki kanki ke wata irin yarinyace wai da gidadanci haka wai ?
Amma kasan fita bada umurni ba baida kyau a musulunci don haka iyayyena suka horeni dashi tun a gida .
Shout, up ki kama min baki da wanan irin maganan meye amfanin motocin dana aje maku a gida hakana .
Shiru nayi banyi magana ba sai sauraren shi da nakeyi kawai yadda ya hauni da bala,i don fadin gaskiya kawai.
Waishi wani irin mutum ne haka mai bahagon haki kamae dai ba musulmi ba duk wani dabi,a na musulmai shi sai a slow harkan shi dai .
Muryan shi na tsikayo a cikin wayan yana fadin akwai wasu masu aiki da kabir zai kawo maku yau zasu dinga dafawa masu gadi da sauran aiyukan gida abinci da fatan zaki kula da hakan.
Insha Allahu na bashi amsa ina sauke numfashi don tunanen dana danyi na da lokaci nasa saida naji muryan shine na dawo a cikin hankalina.
In tafi wurin wanke kai din na kara tambayan shi lokacin dana fahinci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login