Showing 102001 words to 105000 words out of 191310 words
Chapter 35 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
ke nan ni likitan bai gama dubana ba ai da nabika mun tafi tare zaman garin nan wuri daya ya fara isata yanzu.
Wa zai tafi dake ya fada yana kallon fuskanta tace bandai tashi ba yaro idan na tashi ai dole kaje dani.
Hannun rigan shi yake gyarawa tare da fadin wa ni in jera dake ki zama min matsala sai wurin fita jirgi kice min naki san hakan ba.
Dakuwa tayi mai da hannu tana fadin wani munafukin ne ya fada ma dama yaran nan biyu akwai bakin gulma ko kuma Indo ce don dai takwarana ba zata taba fadin wanan labarin ba.
Kinyi ke nan ya fada yana fita daga dakin tace miskilin banza nagama ma yaki a wurin uwarka, yanzu ka dawo zakai min sheri kuma.
Yana fita ya daga wayan shi dake ringing da security din shi yai magana na minti daya bai karasa fitowa ba har sun kawo mai mota bakin kofan shiga gidan.
Ya fito kamar mai kare rana fatar jikin shi yayi sumul dashi kamar jikin larabawa don farin shi na daban ne .
Bai tsaya jiran komai ba ya fada mota suka rufe a hankalin motar tafita daga tangamemen get din gidan mami din a hankali ya lumshe idanun shi yana tuna kalaman hjy data gama rabtabo mashi yanzu.
Wani shu,umin dariya ya sauke yasan waye mami don mahaifiyarshi ce ya kuma san halinta don ita hjy sanin da can baya tana karama taiwa mami din.
Lalai da akwai wani plan da mami ke kullawa tayiwa hjy wanan dadin bakin har yar tsohuwar tayi saurin yarda da maganan ta.
Gyara zaman shi yayi yana gyara lumshe idanuwan shi tare da fadin mami sai dai kiyi hakkuri dani don tun ranan dana fara dora idona kan yarinyar nan tausayinta ya rikede ya zama soyayya a zuciyar danki.
Shi kanshi yasan akwai kyawan mata dasukafi wanan yarinyar da idan yau yace a aura mai aure dasu zai yuyu.
Sai dai shikan ubangiji ya dagwara mai tausayin ta da sonta a yanzu don bai taba fadawa tarkon son wata mace ba irin wanan yar abin da mami ke rainawa.
Shiya idan mami na korafinta a kaina bai iya furta komai a yanzu don son da yakewa yarinyar baki ba zai iya furta shi ba har abin yakan bashi mamaki.
A wani babban shago motar ta tsaya ya dan dade kafin ya fito motae ya shiga shagon biyu daga cikin security din shi na bayan shi duk inda ya bi sai binshi ake da kallo.
Sayayya yayi sosai a shagon saga turare sabulun wanka manshafi da sauran kayan gyaran jikin mata ya biya suka fito daga shagon daga nan ya shiga wani shago na sayar da redmed nan ma ya duba ya zabo ya fito.
Bai dawo gida ba don ya wuce kallon ball sai bayan sallah isha,i ya shigo gidan ga security din shi har biyu da kaya niki niki a bayan shi suna biye dashi.
Daga mami Aisha da hjy duk suna falon sai ya jalal suna zaune a dining suna cin abinci suma.
Welcome ya J suke fada yana amsawa a cikin basar ya nufi kujera ya zauna security din suka shiga gaida mami da hjy.
Suna tsaye saitin inda yake zaune a bayan kujeran tsaye da ledojin da suka shigo dashi a hannun su.
Ya kalli Aisha yana fadin a cikin turanci karbi kayan nan ki shigawa yarinyar nan dasu dakin su.
Ba Aisha ba har mami saida ta dago kai a cikin mamaki tana kallon shi, shiko fuska a daure ya kara bata umurni yana fadin ki karbi kayan nan ki kaiwa zainab daki nace.
Ta mike simi simi don bata hango sassauci a fuskan shi ba lokacin idan taki tasan kwanan wasan a wurin shi.
Meye a cikin mami ta tambaya a hasale ba wani abu bane ya fada yana mayar da kanshi saman kujera tare da fadin john kuna iya tafiya yanzu and make sure by six kun fito don bakwai jirgin mu zai tashi zuwa kaduna.
Aisha dawo da kayan nan, nan mugani mami na fada maki ba wani abu bane a ciki perfume ne da kayan body odor da kikace tana wari na saya mata .
Ido waje mami ke kallon shi waje don jin abunda ya fada don ita har ta manta da tayi wanan maganan a cikin fada ashe shi yana rike da zancen a ranshi.
Wari kuma wake wari a gidan nan hjy ta tambaya a cikin mamaki saida ya mike tsaye bayan ya tabatar da shigan Aisha dakin namu yake fadin.
Tare da duban hjy har lokacin fuska a daure yace wai yarinyar nan zainab shine na sayo mata kayan kamshi.
Jafar zaka fice min a ido tun kan na feto ka ko sai kayi min rashin kunya a nan na fada bata warin ne ko wani oud take shafawa daba za aji warinta ba.
Ok fine mami shine ai na saya mata yanzu don ta dinga kamshi kamar kowa ya dan juyo ya kalli hjy yana fadin ya kike hope ba wani matsala dai ko ?
Ba matsala dan duniya hjy ta fada tana dariyan draman shi da mami din don ita abin ma dariya ya bata kuma.
Mami kan binshi tayi da kallon mamaki har ya bacewa gani ta ta juyo da kallonta wurin hjyn ta .
Iyami na fada maki kibi zancen yaron nan a sannu yanzu ina dadin wanan zancen da yaron nan ya fada koda yarinyar na wurin shi fada zaiyi abinsa namijine bai damu ba.
Hjy gaba daya yaron nan ya sauya akan yarnan don wanan ba halin shi bane musaya min magana ta.
Amma yanzu kan zeey yake kokarin saba min tun kan aje ko ina inaga ya riketa ta zama tasa ke nan.
Don nace zeey din tana da body odor shine ya nuna min shi yasan hanyar gyaranta ko ?
Wanda yaki jin bari ai bayaki gani ba dan zamani ne fa kike jayayya dashi iyami tunda baki jin zance ai yanzu sai ku zuba dashi namu ido.
A karshe idan an zugaki kin ma dan naki baki ya lalace sai ki dawo ku zauna a gidan ina shike nan dai tunda haka kike so.
Daga haka ta juya ta mayar da hankalinta gun tv dake aiki duk daba fahintar abinda ake ciki takeyi ba.
Daga hakan kowa yayi shiru a falon ba wanda ya kara magana sai Aisha data dawo tana zuburan baki take fadin gaskiya ya J ya jamin raini mami nice zankaiwa zeey sayayyan daya yo mata daki.
Ni wallahi dana sani da ban zauna falon nan ba yanzu ke enough kada ki cikamu da surutun banza a nan dan Allah mami ta fada a hasale.
Kafanta ta dauka ta dora saman dan karamin table din dake gaban ta tana karkadawa a hankali kafin ta juyo wurin zeey din tana fadin.
Jeki kira min zeey din tazo nan da kayan da kika kai mata dakin mu gani ikon Allah iyami yaushe kika zama haka.
Ashe bawa yakan canza rayuwan sa yanzu wani zubar da mutunci zai sa ki karbi kayan toshin yarinyar nan don baki data ido.
Daga yau ba zan kara saka maku baki a cikin zancen nan ba na fada tundazun karki dauka wasa nakeyi a zancen nan .
Hjy kiyi hakkuri yaran nan ne da abin bacin rai bawai karban kayab zanyi ba ai dubawa kawai zanyi idan babu na assha a cikin sa.
Barwa yar nan kayan ta a hannun ta koma meye a ciki ina kinfi karfin shi a yanzu hakan kamar zubar da kimar kine a idon ta ai.
Koda Aisha tazo daki ina zaune ina assgment na baje saman gado hakalina ya dauku ga abinda nakeyi.
Naji shigowan mutum dakin haka yasa na dago da sauri don jin karan ledan dake motsi a hannun ta don nasan ba hjy bace wanan mai karfine ya shigo.
Anty Aisha na fada ina niyar gayar da ita take fadin ke dan raini nine zan kawo maki kaya kallonta nake da mamaki don jin abinda take fada daga kofa ta dangwara min kayan tana fadin you will pay for this.
Kiyi hakkuri Anty na fada tare da fadin ba kayana bane don a zatona bata tayi dasu.
Ke dan Allah ja can ya J yace a kawo maki wai kazama kawai ta fada tana juyawa don barin dakin.
In kalli inda kayan suke aje a kasa in kalli bayan anty Aisha dake fita daga dakin ina mamakin kalaminta a fili.
Ni zainab na fada na tare da sake biron dake hannuna na kurawa ledan kayan idanu kamar mai nazari.
Da kyar na iya furta na shiga uku ni zainab me wanan bawan Allah yakeso danine a duniyan nan koso yake sai rayuwana ya salwantane ?
Shiru nayi cikin dakin na kasa cigaba da assigment din da nakeyi sai tunane da nakeyi barkatai a dakin.
Nasan sai tara hjy zata bar falon mikewa nayi na dauki kayan na nufi dakin mami dasu a hannuna bata dakin yasa na aje nafito ba tare dana bude ledan don ganin abinda ke ciki ba.
Gaba na faduwa na fito sai muka hade da mami saidana kadu don tsoron mami da nakeji yanzu a raina .
Gaida ita nayi ta amsa min da kyat na zata zatayi min magana me na tafi nema a dakin nata sai naga ta wuce ta shiga dakin.
Hjy na hango a falo na nufi wurin ta don tsoron zama dakin ma nake ni kadai don ban san abinda mami zata fada idan taga kayan dana kai mata dakin.
Yauwa yar albarka kin zo a lokacin daya dace yanzun nake shirin tashi yau sun watse sun barmu ki kama min kofin nan zuwa daki na amsa da to hjy na dauki kofin da sauri muka jera zuwa dakin.
Ina tsaye saidata zauna na aje mata kofi a gefenta na nufi bandaki don a tsure nake lokacin ina sauraren kiran mami a lokacin duk cikin tsoro nake don bansan abinda zata fadamin ba kan kayan da bansan dalilin su ba.
Na fito na dauke littafina dana bari saman gadon na koma sama kujera na zauna hjy na dan dube dube a cikin aljihu bujen yadi dake jikinta.
Don ko yaushe a cikin kidayan kudi take kamar wani na taba maga gashi idan ina kusa nice mai lissafa mata su kullun.
Duk da babu abinda take saye da kudin ta a gidan komai takeso saidai mami ta sayo mata ko daya daga cikin yaran mami din.
Yauma lissafin muka fara don anyi baki sun bawa hjy kudi da bana nan shi take son mu lissafa da ita.
Mamine ta tsaya daga kofa tana kwala min kira ke zeey na amsa da sauri ina fadin na,am mami tare da mikewa lokaci guda.
Nasamu tako daki ko duk saurin danayi na amsa kiran don naso kada mu kauce a gaban hjy lokacin.
Ina shiga ta zauna a bakin gadon ta kafunta a harde mami gani na fada bayan na shiga dakin da sallamana.
Wanan kayan fa da kika kawo min nan tana nuna kayan take tambayana ba tare data dago kai ta kalli inda nake ba.
Shiru nayi saidata sake fadin kayan nan fa me sukeyi a nan tafada a cikin dan tsawa.
Mami nima yanzu anty Aisha ta shigo dashi dakin mu wai ya J ne ya ce ta kawo nan .
Zeey ta fada tana dago kai ni sa,arki ce ita Aisha data kawo maki bata fada maki naki bane dauke min kayan nan a na tun kan ranki yabaci.
Da sauri na duka na dauki kayan ina kiciniya da ledojin saboda nauyin ledan su yi yawa sosai bazan iya dauka ba .
Hakana ja su zuwa dakin mu na ajesu da kyat ina nishi hjy dake zaune har lokacin tana lissafi ta dago tana kallona tare da fadin.
Ina kayan nan suka fito kuma a cikin mamaki take tambayana na aje a gabanta na koma na zauna tare da tin tagumi don fargaban abinda zaije ya dawo gareni kan kayan nan yadda naga mami ta dau zafi a lokacin.
Yaushe aka kai kayan nan can ko can dakin Indo takai maki don bakin ciki yaron nan fa ya yo maki toshi dazun a gabab kowa ya bada kayan a kawo maki nan dakin.
Hjy don Allah kice ya daina min hakan kada mami tayi min fadan haka sai ta dauko koni ke rokon su abu.
Ina roko anan takwara kayan nan fa keya sayowa su don kansa kuma a gaban uwar taku ya bayar a kawo maki ai.
Maza tashi ki bude muga abinda ya sayo a cikin ledan mai nacin tsiya shine ai daidai da uwar taku .
Kamar ba zan tashi ba ta kara fadi na mike badon nasoba na fara fitar da kayan ledan da man shafa suke su turare da kayan shafe shafen jiki dana wankin kai wasu ban san su ba.
Ja,iri hjy ta fada so yake yakai uwar taku kul idan tace katobara ta iya a gaban yara dayan na jawo na fara budewa dogayen rugana ne masu kyau da daukan ido.
Sai kamahin sabontaka suke duk wanda na daga ko anty Aisha ban taba gani da irin su ba dukda ko irin su take sakawa.
Dayan ledan kuma karami ina dagashi saida nakai zaune don photon waya danagani a jikin kwalin haka ya tabbatar min da cewa wayane a cikin kwalin ko ledan shi ba a cire ba saidai andan yaga gefe da alama a dan budeshine an duba.
Komawa nayi na kai zaune tare da kurawa kayan ido ina tunane kala kala a raina karshe dai tasa na tattara kayan zuwa drower kayana naje.
Har hjy taga ba anta ban samu bakin magana ba don tsoron da fargaban ganin ran mami yana a bace sai na dauka akan yaya jafar din take cikin yanayin dana sameta din.
Washe gari ana public holiday don haka kowa na gida bamu fita zuwa school ba ina idar da sallah na koma na kwanta saman gado don hjy tana zaune a gurin sallah har lokacin.
Muryan shine a kofan yana sallama ta amsa mai daga inda take zaune din saiya shigo daga cikin dakin .
Kafito ke nan hjy ta fada a daidai lokacin daya karasa shigowa dakin idon shi na akaina yadda nake kwamce nayi tub da ciki saman gadon.
Wanan barci takeyi ne ya fada daidai yana zama saman kujeran dakin inda nakan kwana wani lokaci.
Yanzu dai ta idar da sallah ta kara kwanci kafin gari ya waye tafi aikinta.
Wai hjy aikin nan ba a neman wata ta dinga yinsane a barta haka da aikin nan don Allah.
Fadawa uwarku nima na dade ina shawaran hakan a raina duba ga irin sakkon da takeyi na zuwa makaranta tunda safe.
Amma hjy yakamata iyanzu ace ta daina hakana kuna, , , , , ina kwana yaya na fada a daidai lokacin dana dan mike zaune saman gadon.
Lafiya ya fada tare da kawar da kanshi daga kallona ko ya fahinci fita nake sonyi daga dakin ne oho ?
Zauna abinki yanzun fita zanyi ni hjy nazo sallama dama ana jirana a waje ya fada.
Dan satan kallon shi nayi yayi wanka fes yana saye cikin suit baka ga farar riganshi ta ciki ta dan fito waje don aninaiyan su a bude yabarshi.
Zan tafi hjy sai na dawo ya fada tare da mikewa zuwa inda take zaune ya aje mata kudi a gabanta ta shiga jero mai adduan kariya a gareshi kwando kwando.
Har yakai kofa nace da sauri nagode yaya naga sako jiya Allah ya karawa dukiya albarka.
Kisa wayan a caji ya fada daga haka yasa kai ya tafi hjy da har lokacin sai albarka take zuka mai tace tashi ki saka wayan caji yadda yace.
Hjy mami batace min komai akan kayan ba kuma ni naga kamar ranta a bace yake dani .
Yaushe zaki tsaya jiran cewar ta ki saka waya a caji kada kija hasara kuma kudi daine ya riga ya kashesu sai dai tayi hakkuri.
KADUNA
Gidab ya nufa kai tsaye saida yadda ya samu gidane ransa bai masa dadi ba sai sha biyu yake da meeting din dayazo yi anan kaduna.
Yadda ya samu falon kamar ba mutane a gidan musanman ma mata ko ina ga kayanan ajiye sun baza.
Part din shi ya nufa ya bude da niyar ya dan huta a ciki saidai yaga kuran dakin da kyankyami kasancewar shi mai tsabta sosai.
Fitowa yayi don