Showing 108001 words to 111000 words out of 191310 words
Chapter 37 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
rayuwan ki gidan nan tunda safe nake ganin ki a haka.
Gida nake son komawa bakina ya furta kai tsaye gida yar nan kina nan kina rufawa kanki asiri da iyayyen ki zaki zabi zuwa kauye a yanzu.
Ke kuwa idan kinji zomo yaje kasuwa ai ba a banza bane dole saida dalili yar nan ina kula da ita akwai abinda ke cin zuciyar ta na kula matsalan nan ya kwana biyu a tsakanin ta da uwar dakin mu don yanzu dai tau Allah dai ya sauwaka.
Da gaske kande ke fadi zainabu lami ta jiyo tana fuskantata don son jin amsan da zan bata.
Taci gaba da fadin ina fatan dai ba wani abin kikai mata wanda bai dace ba har hakan ya faru ?.
Banjin hakan ne don ni dai nan hjy da kanta ta ban aikin sakawa zainabu ido sai dai ban yarda na taba fada mata komai ba yo mema zan fada tunda bangani ba.
Kallon kande nayi da mamaki lami kuma tana fadin akan me haka kande ?
Dan duban kofan kitchen din tayi kamar mai gudun wani yaji me take fadi kafin tace akan me kuwa sai mugun hali irin na wasu tunda mu masu aiki an dauke marasa galihu ma.
Sun manta su din ba rawa sukaiwa Allah da ya ba basu arzikin ba kai zai iya azurtaka a duk lokacin da yaso hakan.
Idan ba hakan ba dame wanan yan matan da hjy take kokarin hada danta dasu sukafi yar nan da Allah zai bata daulan itama sai kaga tafi dadin kallo da ma,ana.
Amma dayake shi ubangiji maiyin komai yadda yaso ne sai kaga yayo maikyau a gidan tallaka mumuna a gidan mai arziki kuma kowa a yadda ya tsunci kansa yake tawakkali ga ubagijin sa.
Amma da zaran anga tallaka yau yana kokarin tsallakewa talaucin sa yanzune zakaji an fara suka da sara akan sa duk da muma tallakawan muna da namu laifin a wani bangare don wani baya iya boye zalaman sa ga mai kudi.
Irin hakan shike kawo kaga masu arzikin suna kyamar tallakan ya shiga jikin su a dama dashi.
Saidai ba kowani tallaka ne yake zama butulu ba amma kaman wanan yar ai nata matsalan ma sai nace banga abin ki a cikin sa ba.
Waini kande tun dazun kina wanan bayanin nina kasa gane inda zanceki ya dosa tun dazun.
Cikin kashe murya ta dan duka tana fadin kinsan dan hjy ya turburewa uwarshi sai yar nan ita kuma uwar tace basu dace ba da wanan.
Cikin kashe murya lami tace wa ke nan a cikin su wanan dai dake zaune a turai dayazo shike da wanan maganan.
Ita hjyn da kanta yo ai idan ya samu yarnan yayi dace a rayuwan shi wanan son kowa kin wanda ya rasa ai itace daidai da irin su yarinya kin shigo birni a sa, a.
Saidai abinne kan da kamar wuya don masu kudin nan sai kansu suka sani sai yar wani da wance iyasu, , , ,
Ke mekike anan hjy nacan tana neman ki a daki ta aikeki kin dawo nan kin zauna Aisha ta fada a tsiwace.
Zeey din nan kin soma canza halin ki don kinga kamar kowa daidai yake dake yanzu ko ?
Mikewa nayi ina fadin ba zaunawa nayi ba aiki nake kama masu a nan tunda ban komai a ciki.
Kurban lemon dake hannun ta tayi tare da dan watsa min harara take fadin ni dan Allah wuce mu tafi mami ma tana kiran ki a ciki .
Da sauri nakarasa dakin wurin hjy na samu mami kamar suna magana na gaidasu lokacin Aisha ta shigo dakin mami ke fadin tana ina tundazun.
A kitchen na sameta zaune dasu kande suna hira da sauri na dago ina fadin ba hira mukeyi ba aiki muke tare.
Waya sakaki aiki hjy ta tambaya hjy aikin ne harsai an sakata yi nina bata umurni ta dinga zuwa idan bata zuwa school suna aikin a tare.
Tafada tare da fadin ke ina kudin dana aje dazun a daki gaba daya suka sako min ido don jin abinda zan fada a lokacin.
Kudi nace a cikin mamaki eh kudi dana zube saman gado dazun dana shigo wurin hjy da safe .
Da sauri na dago kai ina fadin sunan a dakin mami da zan canza zanin gado na saka maki cikin wardrobe.
Jeki ki kwaso min mami ta fada na juya da sauri don in dauko naji hjy na fadin na fada maki ba halin yar nan bane kada ki soma zargin ta da haka.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
3️⃣2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM WAHAMATULLAH YAR UWA BARKA DA WARHAKA FATAN ALHERI GAREKU YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI YA TAIMAKI MUSULMI A DUK INDA YAKE AMIN, , , ,
LITTAFIN DAI NA SAYARWANE DON ALLAHU MU SAHILEWA JUNA DANI DAKE KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON KI SANI NA FADA IN FITAR DA HAKKIN HAKA GAREKI, , ,
Gaba na faduwa na nufi wurin kayan saidai ganin yadda na gyara komai ba haka na samesu ba yasa faduwan gaban nawa tsananta sosai.
Kaf na bincike kayan basa wajen haka ya kara tayar min da hankali muryan mami ne naji tana kwalla min kira dakin hjy yasa na fito ba tare dana gama bincika ba.
Ina shiga dakin da sallama a daidai lokacin da nake fadin mami gani ita kuma take fadin fadin ina kudin tare da kallona.
Na duba inda na aje ban gansuba mami na fada a dan firgice don a rude nake lokacin dan rashin ganin kudin da banyi ba.
Kamar ya baki gani ba dazun nan fa da zan fita na barsu saman gado dama na fitarne akai lami kasuwa ta sayo cefane.
Mami basa nan inda na aje asalima kayan ba,a jere suke ba yadda na barsu wani ya taba wurin kayan.
Wa kike nufin zai shiga dakin mami ya taba wani abu a gidan nan baya ke saiko mami din dake da dakinta.
Ni ai tasan ko kaya zan dauka itace mai miko min ban damu da daukan wani abuba ciki ba.
May ta canza haline ta fara dan hali yanzu tunda taga kudin kamar banza a gidan Aisha ta fada a cikin wani irin yanayi tana dukar da kanta kan wayan ta.
Wallahi mami ban dauka ba a nan na saka yanzu kuma ban samesu wurin ba an canza masu wuri.
Ke zeey kada ki kawo min rainin hankali wani yarona kikaga ya shiga dakina balle ya kai har cikin wardrobe dina bayan ke ?
Haba haba yar nan yau kuke da ita a gidan nan meya kawo wanan zance haka babu dadin ji sam wanan zance bai dace ba ai haba dai ku dinga tunane kafin ku furta magana man.
Wanan tsohuwar haka kike fa ga magana ta gaskiya zaki daurewa karya gindi ke hjyn nan sai sakawa mutane baki ga zance baki san abinda ke faruwa ba.
Ke yar nan nizaki kawowa diban albarka yan zamani dubani da kyau banyi kama da tsofin banza ba da jika zai iya kawowa rainin wayau yan zamani.
Ko uwarki kyaleta nayi take min yadda takeso a gidanta nazo kinga ko a karkashinta nake yanzu.
Idan bashi ba ita ta sanni sarai tasan binta nake kafin in kai ga juya mata baya ga duk iya shigen da kuke zubawa a gidan nan.
Hjy kiyi hakkuri Aisha wani lokaci haka take abindaba wasa ba sai ta mayar dashi abin wasa a wurin ta.
Iyami wanan ne zancen wasa kina zaune tana kokarin dorawa yar mutane halin daba nata ba yau yar nan take gidan nan tare daku.
Ada can batai maku haka ba sai yanzu ne zaku dora mata halinda ba nataba don kawai a bata mata suna .
Shin ko kin mata ne da wanan watarana itama wani gidan zata idan an wa yarki wanan sherin yaya zakiji a zuciyar ki ko ince yaya zamuji a zukatan mu.
Yar nan amana take a wurin mu da duk kowa naki don karbota akayi a hannun iyayyen ta Allah ma,aiki yanzu kuma a binta da wanan barnan sunan haka.
Kuka nake wiwi mara sauti don hawaye ke tsiyaya a idona ina maijin dacin satan da mami da yarta ke kokarin dora min.
Nagodewa Allah nagodewa wanan tsohuwar datayi min tsaye ta hana kowa ci gaba da abinda ake shirin min don dai na fahinci kamar sheri ake kokarin min a gidan kan kudin.
Muryan mami ne ya katse min tunanena tana fadin hjy bafa wani abu bane kudin ne kawai akeson sanin ina ta zubasu don a kiramin lami su tafi kasuwan wanan kuma ta tsaya nata shirmen.
Jeki ki kara dubawa da kyau ko ina a dakin ko kin manta da inda kika sakane.
Na amsa da to da sauri na barsu a dakin na nufi dakin mami ko ina nake dubawa banga kudin ba na rasa yadda zanyi in fadawa mami ban gani ba a dakin ko ina na duba babu kudin a inda na ajesu.
Da kuka na dawo dakin daga kofa na dan tsaya ina fadin mami bangani ba na duba a wurin gaba daya kayan basa wurin.
Jeki Allah ya sauwaka ta fada a cikin wani daure fuska tare da fadin jeki ki kiramin lami a kitchen a bata wani kudin tunda wacan kan an kwashe ke nan sai dai ba zan kara lamintan hakan ba gaskiya.
Allah ya kyauta hjy ta fada tare da fadin nidai nasan ba yar nan ta dauki kudin nan ba tunda ba yau take daku a gidan nan ba komai bai taba faruwa ba irin haka.
Idan da yarnan tana dauke dauke da tuni ansan da hakan kadafa a maidani tsofuwar banza don nagane abinda ake kokarin kullawa yar nan kuma ba zan taba yarda haka ya faru ba.
So ai da laifine, laifin namu ya kamata mu gani domin shine ya nuna yana sonta ba wai yarinyarce ta nuna tana son shi ba balle mu dauki laifi mu dorawa yar mutane ga banza.
Don haka iyami ina shawartan ki ki dauki yar nan ki maida ita hannun iyayyenta tun kan shedan ya zugaki ki aikata abinda ba daidai ba.
Amma idan har yar nan tana zaune gidan nan tare daku kuna kokarin dora mata laifin daba nata ba.
Hjy nima naso hakan tun farko saidai ina tunanen maganan ki kan yaron nan kada ta koma gaban iyayyenta ya bita can ba tare da sanina ba wani abu yazo ya faru a tsakanin su.
Ko tana nan a gaban ki idan Allah ya nufa akwai aure a tsakanin ku sai angi iyami.
Kada ki manta a kullun ina tuna maki baya ki daure yadda Allah ya turo yarinyar nan a karkashin ku har danki yaganta ya nuna yana ra,ayin ta.
Shin me zai hana ki daina hattaran yar nan ki sanya ido ga danki shida ke faman bibiyar rayuwar mutane haka.
Ita metayi za aga laifinta waya take masa ko binshi takeyi, ko kulashi take tana bibiyan shi inda duk ya saka kafa ?
Daki iyami shike wa yarinyar nan duk wanan abinda na lissafo maki a gidan nan kullun yar nan a tashin hankali take gidan nan .
Don haka ina gargadin ki karo na karshe da ki takawa danki burki ya rabu da yar mutane tunda dai baki aminta da wanan abin ba.
Don iyayyen yarinyar nan suna can suna fadin kina nan kin rike amanan yarsu da hannu bibiyu basu san ba haka ba yarsu na nan cikin ukubar ki don kawai danki yace yana ra,ayin ta.
Hjy kin san halin dan yau shi jafar na rasa gane kansa kan wanan abinda yanace sai zeey ni fa bawai niki zeey din nan bane don ina kyamarta ko wani abu.
A, a ba hakana bane zabin nasane ni sam bai kwanta mun raiba don idan har ilimi ko kyau ko wayewa ko arziki yaron nan nasan duk zai iya samo macen data tara wanan abin gaba daya da kansa.
Amma wai hjy sai ace yau yaron nan ya kafe shi sai zeey a cikin kasan nan abinnne da ban haushi da ban mamaki don yi iya tunane na rasa gane dalilin shi na wanan kafiyan tsiyar ta kare tare da jan tsuki mai nuna takaici.
Koda ta dago kai sai duk ta tsargu da irin kallon da hjy kemata don haka ta dukar da kanta.
Mikewa tayi don barin dakin iyami hjy ta kira ta fuska a daure cikin murya mai kaushi mami ta amsa da na,am hjy cikin girmamawa.
Tace wai me yake damun ki ne iyami zaman turai fa ba hauka bane mami tayi shiru tana sauraren yar uwan nata.
Hjy ta sake daga murya cikin bacin rai tana fadin kul naji wanan maganan batar kudin nan ya karde gidan nan har yawuce iyamu nan rayuka zasu baci fiye da tsamani.
Don ina da tabbacin yarinyar nan bata taba maki komai naki a gidan nan don da tana tabawa da tuni an gama gane ta.
A, a hjy aini na gama maganan don ya, , , , sallaman lamine a kofan yasa su yin shiru gabaki dayan su tace lami muje falo in baki sakon a can.
Na dade a inda nake ina hawaye saida naga mami ta koma daki sun gama da lami naja kafata da yai min nauyi zuwa dakin namu.
Ina shiga tsohuwar ke fadin kina ina tun dazun acikin yanayin damuwa na iya budan bakina da kyar ina fadin waje na zauna.
Kinga sake ranki idan kin so nasan bazaki taba wanan halin banzan daba a sanki dashi ba tun farko.
Hawaye masu dumi naji sun fara saukomin a idanu hjy ta nuna min matukar tausayawan ta gareni tana ta bani hakkuri.
Hakan daya farune yasa ranan gaba daya na wuni sukuku dani a gidan ban ko leka falo ba ina kwance a daki zazzabi yana neman rufeni sosai.
Panadol hjy taban nasha sai barci koda mami tasa murya ta kirani sai hjyn ce ta amsa tana fadin banjin dadin jikina na kwanta.
Kamar mami zatayi magana sai kuma tayi shiru don tasan idan tayima yanzu hjy zata kareni gareta ne.
Karfe takwas ya kira wayan ina barci ba wanda ya daga wayan har saida y kara kiran hjy ta dauka zuwa falo don wani ya karba min .
Aisha ce da hjy zaune saman doguwar kujera suna zaune sama a guri daya ta mika mata wayan tana fadi karba min wanan wayan don Allah yar nan tasha magani ta kara kwanci.
Wayar waye wanan ta fada tana karban wayan a hannun hjy din mami ta dan juyo ta kalli wayan tare da kawar da kanta gefe.
Receive din wayan tasa tare da kara wayan a kunnen ta sweety rowan daukan wayan ma kike min kuma tun dazun ina kira ba a daga ba .
Ehhy, , , ya J to ba ita bace yace Aisha yah kuna lafiya lafiya ya mami na kira bata daga ba gata nan tana kokarin karawa mami wayan a kunnen ta.
Don't dear touch me with dis dirty phone mami ta fada a dan hasale Aisha sorry mami a dan shagwabe.
Ta mayar da wayan a kunnen ta yace bar mami nasan akan yaran nan marasa tarbiya take fushi dani haka.
Where is my baby girl ya fada cikin katse Aisha din tace who ya J ?
Yace the owner of the phone wai wanan stupid girl din zeey tana daki tana fushin banza after she steel mami money .
What, ya fada dan karfi kamar a fili yake kusa dasu ba a waya ba yace it can't.
Wani irin wasane wanan da sata kuma satan kuma na kudi hjy dake gefe tana fadin kai amma keko an daiyi yarinyar kawai a gurin nan.
Ban wayan mara mutunci ina saidana gargade uwarki kar zancen nan ya fita har yakai kunnen yaron nan.
Hjy why are you always abusing me bata dauki kudin nan bane ko me kina wani kareta can mami dake daga gefenta take wani tunane yazo mata lokaci guda.
Take fadin Aisha meyasa kika fara yawan surutu ne yanzu sai kuma ta juya harshe a cikin turanci tana fadin kinsan hjy akwai tsufa a tare da ita ki daina biye mata kuna haka mana bana jin dadi haka nima lalaba abina nake ta karasa fadi ki bata hakkuri please.
Hjy yi hakkuri bansan kin fadi haka ba ai ta fada a cikin fushi hjy da ranta ya gama baci take fadin yanzu ai kanku ake ji yar nan .
Duk abinda ake waya a kunne take har lokacin a hannun hjy data fisge gun Aisha