Showing 81001 words to 84000 words out of 191310 words
Chapter 28 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
ba hjy dama dai tambayan ta nake son yi kawai mami ta fada sai hjyn tace.
Koma menene tunda tayi barci ai sai a kyaleta har safe a tambaye ta itama fa mutum ce kamar kowa a cikin ku.
Hjyce ta ceceni a ranan don mami fita tayi a dakin ba tare data tasheni ba kamar yadda mahaifiyar ta ta hana.
Ranan idan nayi barci barawo ne ya sace ni don haka na kwana ina sake sake bani kadai ba har wanda duk abin ya shafa banda ya jafar dashi ko a jikin shima hakan.
Aiko gari na wayewa sai ga sakon mami inzo gabana na duka uku uku na mike daga inda nake zaune a takure na nufi dakin mami din.
Addu,a kan nasha shi yafi cikkn kwando ranan da sallama na shigo dakin daga ita sai Aisha da mama Ramatu.
Mami tayi tagumi tana zaune kasa a inda ta idarda sallah asuba ta rasa abinda ke mata dadi a rai so kawai take taji na bakina abindake wakana a tsakanina da danta.
Nayi sallama na shiga sai mama Ramatu ne ta amsa min a lalace koshi Aisha ko tana bina da wani irin kallon mai kama da mamakina a fuskanta.
Kasa nakai cikin karfin hali ina fadin ina kwana mami ban jira amsawan ta ba na juya airin mama ramatu itama na gaida ita na juya gun anty Aisha itama hakan ne.
Shiru dakin yayi na dan lokaci ina tsugune kafin inyi yunkurin mikewa don shiga ban daki in wako yaddana saba yi.
Dakata zainab komaki zauna mami tace dani na koma da sauri inda na tashi ta dan dago kai ta kalleni kafin tace zeey ban saki da karya ba ko wani abu makamancin hakan.
Balle boye magana don baki taba min shi ba tun zuwan ki gidan nan wurina.
Kaina dan gyada a hankali yayin da gabana yaci gaba da faduwa sosai jiya tare da wa na ganki zeey ?
Kai na dan dago da sauri na dan saci satan kallon mami na samu ta kafeni da ido tana son amsa daga gareni.
Shiru na danyi tare da dukar da kaina kasa ina kallon carpet din da nake saman shi.
Bakiji me aka tambaye ki bane mama Ramatu ta fada daga inda take zaune din da dan karfi hakan yasa na dan zabura tare da dago kaina ina fadin babu komai mami.
Babu komai kuke haka jiya tare dashi a gaban kowa Aisha ta fada a dan hasale tana watso min harara.
Ni ban san komai ba tun bayan da kikace mai kwaliya ta shiryani yadda ya kama kika fita kika barni da ita mun gama na fito na samu duk kun tafi babu kowa da zanbi sai gashi shi yace nazo mu tafi.
Wani ajiya zuciya mami ta sauke har ina jinta daga inda nake Aisha ko na kokarin fadin wai kina nufin ni No wallahi mami ban san komai ba a kai kawai dai ya ban kudi a gyara mata kai daga can kuma ya kara turo kudi waina saya mata kaya expensive one don kin manta ki saya maya yanzu hjy ke fada mai.
Jeki zan kara nema ki mami ta fada tana kallon mama Ramatu da itama din ita take kallo don jin abinda ta fada.
Kai mami ta gyada mata alaman ta bari in fita daga dakin tukun suci gaba da magana zan shiga ban daki tace barshi anjima ki dawo idan mun fita.
Na juya na fita nan na barsu a dakin sai da na fita ta juya tana kallon Aisha dake zaune tana fadin duk abinda aka kitsa tare dake aka shirya hakan ashe kika boye muna.
Wani mami wallahi ban san komai a kai nima iya abindana sani ke nan na ta fada yanzu dana sani ai dana fada maki komai tuni.
Daki na koma na takure a wuri daya ina faman funane a raina don na kara daure kaina again ban san da wani ido zai kalleni ba kuma nasa bangare ga mami bawai ta yarda dani bane tunda har tayi mi abinda bata taba min ba yau shine.
Wai in fita idan sun gama na dawo in gyara dakin kenan da sauran maganan da zasuyi a kaina ke nan a dakin.
Shirun da nayi yasa hjy dake magana still kan daren dasu mami sukayi jiya a waje taji nayi shiru hakan yasata jutowa gareni.
Hawayen da ban san yana zubane daga fuskana ta ganin haka ta fara sake salati tana tafa hannu tare da fadin yarnan an maki wani abi ne ko kiranda iyami ke maki jiya na hana a tasheki tai maki fada a kansa yanzu don naga bata so hakan ba dama.
Saboda shine ta bata maki tunda farar safiyan nan ko da sauri na girgiza kai don nasan baida wuya yanzu ta sauke wa mami bala,i akai ta kara jamin wani tsana.
Kofan dakin aka turo Aisha ce tsaye a kofan tana fadin zainab mami na kira daidai lokacin da hjy ke fadin.
Ke kan yar nan arr da halin nan naki ace dan musulmi bai iya sallama idan zai shiga guri gara dai da uwarku ta raboku da kasan kafiran nan tun kan kufi haka ai.
Sai kuma jin abinda ta fada ta sake fadin wai wani laifi tayi maku haka baku bari yarnan ta hutane wai ?
Ba laifi tayi ba naji Aishan ta fada a daidai lokacin da zan fita daga dakin bayan fitana asheta fada mata komai dake faru tun daren jiya din a bayana.
Sai da tsohuwar ta gama ji take fadin meye laifi a cikin zancen nan idan shi jafarin yace itace zabin sa ai baiyi zabin banza ba nake gani ko ?
Haba hjy yar aiki ce fa wanan yarinyar da bata waye bane zai dauka a matsayin matarshi yadda ya J yake wayayye dan boko mai ilimi din nan dashi.
Yo wani waye akwai wanda yafi wani a gurin Allah ne idan ba Annabin rahama ba shi kadai zai fadi haka sai ko wa yanda sukai zamani dashi aka tabbatar masu da aljanna .
Kai don Allah hjy ki daina danganta wanan da yayan mu please ai abin kunyane ace wai wanan ce zabinsa haba dai.
Kaji min ya da wani maganan banza meye laifin zabin nasa har idan da gaske yakeyi ba wasa ba uwarku da ubanku ya aureta takai wanan din wayewa ne a lokacin.
Aida ba yanzu bane Aisha ta bata amsa tana fita tace kinci gidan ku nace kinci gidan ku yarnan da wanan maganan banza kece zaki zauna mashi da ita koshi zai zauna da abinsa.
Fita tayi ta kyale tsohuwar tana jin zancen ta na kara mata takaici a ranta sai ta dauki zancen tsohuwar ga tsufane kawai ke damun ta ba wani abuba don da tasan abinda takeyi da bata fadi hakan ba ai.
Ina shiga dakin mami ba tare data kalleni ba tana jin sallamana take fadin jeki ki wanke muna bandakin nan idan kin gama ki daukowa hjy abin karyawanta a kitchen.
Don mami ta dauki zugin mama Ramatu da wata kawarta da tun jiya ta zugeta a kaina baki daya don haka ta kudurta canza min daga wanan lokacin tun ban dauko mata magana ba a cikin diyan ta.
Wanan zugin kan mami ta haushi ta zauna akai sosai har yakai ta fara ganin aibuna a gareta yanzu.
Kafin in fito har ta shirya zata fita ta gaisa da mutane take fadin yi ki karasa ki fufo min dakina na amsa da toh kawai a cikin sanyin jiki ga canjin da nagani gareta.
Dakin mu tashiga gaida mahaifiyar ta inda ta samu hjy har lokacin tana mitan zancen ita kadai a dakin.
Koda mami ta shiga amsa sallama dai tsohuwar tai mata babu sakin fuska suka gaisa tayi mata ya jiki ?
Mami bata tsaya ba ta juya tana fadin bari ta leka yan uwa a dakin in dawo tana fadar haka ta fice daga dakin.
Har na gama gyaran dakin na jawa kamar yadda ta umurceni in mata da dakin na wuce kitchen na karbowa hjy abincin.
Ban daki na shiga nayi wanka na fito na shirya a cikin wani atamfa da Aisha ta bani dinkin buje da riga bujen dai bai matseni sosai ba yadda ita yakan matse jikinta idan ta saka a jikinta kafinta bani .
Ban zauna a dakin ba na nufi kofan fita daga dakin ina zuwa kawata hjy ta fada zan je in karbo abincine a kitchen na bata amsa.
Yau kuma ba a nan mukeci tare ba dake mazaki dawo ki dibi abincin nan kici karna saba maki.
Ko ta fahinci tsoron mami nake sai tace kowa yasan tare dake nake cin abinci sai yaune zasu kawo min wani zance.
Dole na dawo na rakube a gefe ba tare dana yi yadda na saba muna wasa da dariya a gurin ci ba haka hjy ta sakani gaba dole na debe abinci mai yawa tana kara ina ya isheni haka ta kyaleni.
Na fara ci ke nan mami ta shigo dakin tana magana sai ta dagata da maganan tana fadin ke kuma meye haka ?
Me tayi hjy ta tambaya tana kallonta da mamaki hjy don me zata zo ta zauna tare dake a nan tana cin maki abinci ?
Yau din kuma iyami ina har ke muna zama da ita ana aci abinci baki taba fadan wani magana sai yau ?
Daga yau din ban son in kara ganin hakan ta koma can wurun yan aiki ta dinga ci tare dasu kande da lami.
A, a iyami bana son irin haka wanan ba halinki bane hakan ban san kuma yaushe kika fara hakan ba.
Hjy na canza tsarinane yanzu a gidan nan don a fara bambamta yan aiki da yan gidan nan iyami dakata hakana hjy ta fada tare da juyawa inda nake tana kallona kafin tace dani kinga kawata.
Jeki falo kici abincin ki ki bamu wuri zamuyi magana da uwar ki ina jin hakan na mike da sauri don barin dakin.
A daidai lokacin mami ta kai zaune a kusa da mahaifiyar ta saidai ita saman kujeran ta zauna ba a kasa ba inda hjy take zaune.
Ko dana fita ban nufi cikin falon inda nake jin dan dararakun mutane na zauna dan filin da zai sadaka da falon da gefen dakunan mu din.
Ina kallon abincin ba tare danayi ko yunkurin cin cibi daya daga abincin ba sai idon dana zuba mai kawai.
Iyami kada ki bari shedan ya rudeki kiyi yunkurin yaki da ubangijin ki kan abinda Allah shida kanshi ya halasta hakan.
Yarki dazun ta fada min komai dake faruwa daku tun jiya wanda na hango kina kokarin fita daga ilimin ki da irin tarbiyan ki dana sanki na girmama dan adam a duk yadda yake.
Hjy ba hakana bane ni yaran nan zasu kunyata a cikin taron jama, an arzikina wai yaron nan ya nemi ya raina min wayau ya hada baki da yar nan a kunyatani hjy ?
Akunyataki kamar yaya hjy ta tambaya shi auren ne kunya ko yarinyar ce kunya a gareki yau kuma kina kunyan a santa da ahakin ki kika ajeta a gidan ki har kika jata a jikin ki kamar kece kika haifi abinki.
Wani irin shedani ne yayi saurin tasiri haka a jikin ki har kika manta da bayan ki ke ?
Da sauri ta dago kai ta kalli tsohuwar hjy tace eh kin manta da naki bayan kina son ki maimaita tarihi a kanki yau.
Hjy bawai hakana bane ni abinne yai bala,in bata min rai kawaion su wullakantani har jafa, , , , ,
Hannun da tsohuwar ta daga matane ya dakatar daga karasa maganan ta datayi niyar fadi a kanmu.
Iyami na haneki tun wuri da wanan halin abinda zai kawo dana sani daga baya wanda zai zama keya gareki.
Yaya zaki idan Allah ya nufa wanan abin mai yuyuwane garesu ko kina son in kin matsa da jayayya da ubangiji ya dauki ranki ayi a bayan ki.
To ina baki shawara ki natsu ki shiga hankalinki tun wanan abin bai fita waje an dawo ana maki dariya ba daga bayan ki.
Ina yar nan ke kika kawota gidan nan har danki ya ganta ya nuna sha, awan shi gareta duk ko da yadda take ba yar kowa ba kamar yadda ku kuke gani.
Shin iyami kin manta da yadda akayi lokacin auren ki da mahaifin yaran nan sam ban taba zaton zaki manta da hakan ba har ace yau ke da kanki kike kokarin yin wanan halin da ba, a san musulmin kwarai dashi ba.
Ina wanan abin ke kanki kamar darasine a gareki ban taba zaton har zaki yada kiyi ko maka mancin hakaba a yanzu.
Daga inda nake zaune naji takon tafiya haka yasa na dago kai da sauri ina kallon mai zuwa a lokacin ya Jafar ne da yaya mamud suna tafe suna magana a tsakanin su.
Saidai ganina a wurin yasa sukaja suka tsaya suna kallona da sauri na gyara zaman da nayi da farko ina gaidasu.
Duk kallon mamakin ganina a wurin sukeyi sai ya mamud ke fadin lafiya kanwata kika zauna a nan haka a kasa baki je dinning kin zauna ba.
Wani kallo ya Jafar ke min ba tare dayayi magana ba sai hannayen shi daya zuba a cikin aljihun wandon shi bakin wandon jeans dake ciki ya dan fito waje ya wani kara haske ko kallon tsoro nayi masa oho.
Badake ake magana ba ya jafar din ya fada na dan dago kai na kallesu sai nayi saurin dukar da kaina don duk idon su yana a kaina.
Ganin ina kokarin mikewa yasa ya mamud ya fara tafiya shima ya mara masa baya zuwa dakin dana baro su mami din da hjy.
Da sallama suka shiga dakin saidai ganin yadda daga hjyn har mami suke sai yasa suka dan tsaya daga kofa basu karaso ba sai ya mamud ke tambaya lafiya dai mami ko wani abinne ya faru ?
Shike nan ma hjy ta fada ga magani ga ciwo Allah ya kawo ki tambayi dan ki a gaban mu yanzu aji idan da gaske yakeyi ko wasan da kike tsamani kika tsani yar mutane haka ba gaira ba dalili lokaci guda .
Kin hana yar mutane tun jiya kwanciyan hankali duk kunbi kun rikita yarinya ga baki daya ni bani son irin haka wallahi abu baikai abin daga hankali ba zaku sakawa mutane rigima a gida.
Kallon mami yayi ya karaso inda take yana kaiwa zaune ta gefen gujeran tare da kamo hannun mami din yana fadin wani abu ya farune mami ?
Bai faru ba zai dai faru ka gaya muna meke tsakanin ka da Abu dana ganku jiya a gurin taro har kana nuna muna wai surprise din ka ke nan garemu ta fada rai a bace.
Abu mami ?
Waye hakana mami ban gane wa kike nufi ba hannun ta dake rike a nashi ta fisge tana fadin zeey yar aikina nake nufi ba wani ba.
Kai ya girgiza tare da dukar da kanshi kasa can ya dago yana fadin mami ba ke kikace na fito da yarinyar data kwanta min a kasan nan ko diyar waye ba ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUKU 🦅
2️⃣5️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH MUNA ROKON RAHAMANKA DA KARIYAN DAGA DUK WANI ABIN CUTARWA A GAREMU ALLAHUMA AMIN, , , , ,
To ka samo din ta tambaye shi a cikin gatse ?
Eh na soma mana mami kuma ai a karkashin ikon ki take itama yarkice kamar su Aisha.
Wa ke nan ya mamuda ya tambaya wanan yatinyar taki da kika dauko a kauye mana ga zahiri kun gani jiya tunda kun gamu tare.
Mami kan yake tayi wanda yafi kuka ciwo kafin ta tattaro natsuwa don hjy dake wurin a zaune bata da halin furta mai wani abu a lokacin.
Saidai duk da hakan sai da mami tayi bajintar fadin wai zeey dai kake nufi ai zee din kasan a matsayin dana daukota kuma bayan haka karatu take a yanzu.
Mami nasan da hakan saidai ai takai munzalin aure a yanzu don haka aurena da ita ba zai hanata karatun ta ba.
Ko kin manta kin fada muna kema kina karatun secondry daddy ya ganki ya aure ki lokacin.
Look jafar bana son shirmen banza mata nace ka fito da ita in maka aure at dis stage bawai ka tsaya kana min wanan shirmen ba haka.
Zainab na fadama karatu take kuma bata cikin zabin matan da nake son ka aura don tayi kankanta gare ka yanzu.
Hjy dai da yaya mamud na gefe zaune suna sauraren draman uwa da danta sai murmushi suke masu kawai.
Mami to