Showing 138001 words to 141000 words out of 191310 words
Chapter 47 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
ina kokatin fita daga motan don zumudi naji hjy na fadin ki bi a sannu ki tuna kina da aure a yanzu din.
Don haka ki natsu sosai ki tuna ko a nan din kina da makiya tare da mahasda da zasu so suga faduwan ki don haka sai ki natsu kiwa kanki fada da kamun kai ki fara nuna yanzu ba da bane garesu.
Hakan yasa naji wani iri n natsuwa yazo min lokaci guda na tuna da abinda na bari a gidan namu tun farko don haka har gyalen jikina saida na gyara yafashi kagin a bude muna mota don mu fito a lokavin dirin motar yaja hamkalin kannena sun fito don ganin ko waye yazo.
Sannu a hankali aka bude kofan daga waje a bangaren da hjy take zaune kafinta ta fito a hankali ta sauka daga motar.
Driver ya dawo bangaren da nake zaune ya bude min kofan a hankali na dan dauki lokaci kafin in sako kafana a kasa na sauke su a cikin kasan kofan gidan namu.
Kyau ta kalman dake kafana kawai ya isa daukan hankalin wanda ke gurin a lokacin na karasa fitowa waje ina dan gyara gyalen kaina da kyau a hankali.
Duk yadda zan kwatanta maku haduwa a lokacin ba zaki gane yadda shigan ya mayar dani ba sai dai idan kin gani a gaban idon ki.
Takalma iri hill shoes din nan ne fari sol a kafata sai madaurin sarka fari da yake dashi.
Dinkin material din dake jikina mai kama da half gown sai ta kasan shi akai ado da wani yadi mai kama da lace mai kore da baki a jikin shi.
Hannun rigan yana da dan shara sharan hannaye har zuwa kasan hannun.
Hjy ce gaba ina daga bayan ta rike da yar karamar jakka mai kama da post a hannuna shige guda da takalmin kafana ina takowa a hankali.
Ga kannena ina gani kamar in shaka in rugume su sai dai ina ganin irin kallon basu gane mai shigowan ba da suke min a lokacin.
Sai da muka karaso gaban sa,ade a hankali na bude baki kamar ban son magana tare da fadin haka aka koya maki taron baki.
Wani ihu ta yanka tare da fadin wallahi yayan muce ta kwasa cikin gida da guda tabar kayan da take suyan awara a kofan gida.
Ihun tane ya jawo hankalin kowa a gidan yayi daidai da Abban mu na gida dakin lantana a lokacin duk da misalin sha biyun rana ne lokaci ya nuna a garin.
Abin mamaki sai ga innan mu a guje don ranan bata nuna wanan kawaicin ba nata da take nunawa a kaina na yar farin ta.
Saidai gani tare da hjy yasa taja ta tsaya kuma da dan tsohon cikin ta da ya fara baiyana a lokacin a jikinta.
Nikan ganin inna taja baya ta tsaya don ganin tsohuwar mai kamala da muke tare yasa na kasa daurewa na nufi wurun inna a cikin sarsarfa na rugumeta.
Ina jin wani farin ciki da shaukin ganin mahaifiyata da nayi yau sai nake jin kamar anyayye min duk wani matsalolin da nake ciki a lokacin don ganin mahaifiyana a gabana.
Wai abune kowa nake gani haka a idona Asabe ke fadi daga bayan mu ta fito daga dan lungunta ds yanzu duk ya gama yakucewa ba gyara kamar farko da Abban mu ke yawan gyara mata idan ya dauko lalacewa.
Itace fa Asabe sa,adaty ta cabe tana fadin yau Allah ya dawo muna da yar uwan mu gida yan bakin ciki yau kan sai dai su mutu ko a kasa barci don bakin ciki.
Masu farin ciki kuwa yau barci harda nasari don Allah ya baiya na gaskiyan shi a filin Allah kowa ya gani.
Daga inda hjy take ta amsa da fadin kwarai yar nan dama haka al,amarin Allah yake ai idan ya tashi ikon shi ba wanda ya isa ya hana hakan.
Yau ga yar ku ta dawo gare ku a matsayin matan jikana al,amarin aure daga Allah yake matar mutum kabarim sa.
Da sauri Asabe tace balle munan ai kowa dan farin cikine da hakan ai hjy kayya hjy ta fada a daiyi sha,ani ai da ba haka akaso gani ga jikan nawa ba.
ZAINAB IDRIS MAkAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4️⃣1️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE YAR UWA DON GIRMAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA , IDAN KIN SAN DARAJAN ALLAH, , ,
DOMIN BIYA ZAKI IYA TURA KUDI TA WANAN LAYIN BAKIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI TURA KATIN WAYA NAGODE, , , ,
Bayan an zauna an natsu a dakin inna ina sai yan dabarun mata takewa hjy don taron ta duk da bata san ko wacece hjyn ba a lokacin.
Saidai cikar ido irin na hjy da kamala yasa kwarjinta ya dauki hankalin ko wa a gidan sai ga Asabe ta dawo tana fadin .
Sannun ku dai da zuwa ta kara fada tana kokarin shigowa daga cikin dakin takai gurfane.
Kaga Asabe do kinga yayar mu tazo da kama mai kyau har kina wani rawan jiki da zuwan ta a yanzu.
Duka inna takaiwa sa,adatu da bayan hannu tayi saurin gwaucewa tare da mikewa tsaye tana ja da baya don barin wurin tana magana ciki ciki.
Asabe na fadin rabu da ita sa,adatu ba hankali gareta ba ai koma me ye ai wanan zancan baya ne kike daukowa.
Duk abinda ke faruwa hjy na zaune ta lura da komai daga inda nake zaune ina mamakin yadda sa,adatu takewa asabe a yanzu.
Kamar ba Asaben da ko muryan ta mukaji a sa can baya sai gaban mu ya fadi don masifa da irin matsawa innar mu da sukeyi lokaci.
Amma sai gashi yanzu na dawo na samu suna mata abinda sukaga dama a gidan.
Haba dai sa,adatu ki daina haka mana na fada ina kallon ta don naga ran innan mu ya baci sosai a lokacin.
Kinga kawata yaki zonan ki kyale su naga sun taru a kanki ke kadai haka hjy ta fada tana mikawa sa,adatu hannu tazo wurinta.
A lokacin ne Asabe ke fadin ita wanan din ne hjy da kike aiki a gidan ta ko waye ita din tana kallona.
Kafin na bata amsa hjy tace a, a , aha nidin dai kakar mijin tane nice na haifi uwar mijin nata don haka ita din matar jikana ne yanzu.
Ikon Allah asabe ta fada sai mukaji zancen aure kamar a mafalki daga sama ba tare da wani sanarwa ba kawai.
Ai kin san aure habo ne shi idan lokacin yinsa yayi koda shiri ko ba shiri ranan sai anyi shi Allah ya nufa matar shice shima.
Har hakan ya faru da yar nan yarinyar arziki yar kirki aka dauketa aka mika a birni ba tare da an taba bin sawun wanan yar ba anga a inda take zaune ba.
Sai gashi ubangiji ya tarfawa garin ta nono ta shigo birni da kafar dama tayi gamo da arzikinta taci kuci har wani nata shima ya raba yaci ya huta a karkashin innuwar ta a yanzu.
Wani kuka Asabe ta sake daga gefen da take gurfane tana fadin yar nan naso cutan kaina da kaina da badan Allah ya gyara ba ki fada hannu na gari wa yasan hannun da zaki fada haka.
Na aikata abu a cikon duhun kai nabi zugin da ya jawo min zagi da zunde a gari kan na sayar dake a hannun yan birni.
Har zaure mai gari muke da iyayyen ki saida nayi rantsuwa akan ba sayar dake nayi ba a garin nan.
Allah da ikon shi an gama kulla min wanan sherin da kwana biyune zancen auren kin nan yazo muna garin nan a cikin bazata.
Wanda hakan kuma ya kara jawo muna kace nace a cikin garin nan wanda har yanzu mutane a kanshi suke wai ba a san mutum ba an dauki yarinya an bashi don kwadai.
Cike da takaici nake sauraren abinda Asaben ke fadi na rasa abinda ke mun dadi sai hawayen dake zubo min a lokacin a raina nace ni haka rayuwana zai kasance da barnan suna.
Wanan wace irin kaddaran rayuwace Allah ya jefoni a cikin sa don kawai ina ya mace nake gamuwa da wanan kaddarorin haka ko me ?
Da sauri hjy take fadin yo meye haka ana zaune kallau zaki sakawa mutane kula a nan haka godiya ya kamata kiwa Allah da yanufa ba abinda mutane ke zargi bane ya faru dake din.
Inna ma kuka take a lokacin cikin kunar rai tana fadin bari hjy munga abu a rayuwan mu kamar kaina farau haihuwa diya mata a duniya.
Diya mace alherine hjy ta tare inna tana fadi don ni nan nafi kowa sanin dadin hakan don uwarsu ce ta zame min gata ga zuri,a na.
Don haka ba za a zagi diya mace a gabana ba ban bada amsa ba don na haifa nasan dadin su a rayuwana.
Gyaran muryan da Abba yayi daga kofa inna yasa mu dan dago kai muka kalli kofan da alama daga barci yake a lokacin saboda yanayin shi ya nuna hakan.
Me kuma ya faru nake jin kamar kuka ke kenan baki gajiya dayiwa mutane kuka akan abunda baikai yakawo ba a gidan nan.
Bawan Allah kada kaga laifin yarinyar nan raba da da mahaifi ba abin wasa bane don kukan yanzu na zuwan yarta ne takeyi.
Sai akace don yarta tazo su mayar muna da gida kamar na makoki dama haka yana kallon Asabe data fada mai magana kamar ba Abban mu dana sani da farko mai taushi da sanyin raiba.
Fuska a daure ya juyo yana fadin mama sannun ku da zuwa ashe kuns hanya tafe ?
Hjy ta sauke ajiyan zuciya tana amsawa Abba gaisuwan a cikin dan sakin fuska sai bin kowa da kallo take tana mamaki a ranta.
Taci gaba da fadin tafe nake da jikana don taki sake jiki tun bayan zancen daurin auren nan dayazo muna bata a cikin walwala sam.
Shine na kawo ta gida zata kwana biyu mijin ta zaizo ya dauke ta su tafi don jerabawan da zata fara wani sati mai zuwa in Allah ya yarda.
Saidai zanso nasan ko akwai wace zamu samu daga nan da zata tafi ta zauna muna da ita a can gidan nata na Abuja.
Duk wanan bayani da hjy kewa iyayyena sai a lokacin nake jin komai daga bayanin da take masu din a yanzu.
Abban ya gyara zama yana fadin tau hjy abune dake son natsuwa a yanzu zamu zauna bayan tafiyan ki mu duba wace ya dace ta bita can din inda halin hakan.
Ba damuwa hjy ta fada tare da kara basu hakkuri kan yadda auren yazo batare da an gudanar da komai yadda al,ada ya tanada ba.
Duk sai naji na muzanta sosai yadda hjy din ta samu gidan mu duk da dama ai tasan tunda har na iya zuwa aikatau a birni babu abinda zata sama a gidan namu.
Ina tuna irin kallon kaskancin da Aishan mami ke min tun fara zancena da ya Jafar din wani kallon banza da raini take watso min aduk lokacin da zamu hadu.
Da ace daga cikin su ne sukazo gidan namu a haka Allah kadai yasan irin abinda zasu fada akaina kan hakan.
Saidai ita hjy babu hakan gareta zaune take saman tabarma da inna ta shimfida a dakin ta mike kafa hankalinta kwance dasu tana masu bayanin komai.
Abba ya mike ya fita yana fadin bari ya dan fita sai ya dawo a daidai lokacin da ya jamal ya bada tsaraban da sukazo dashi da kayana a shigo dashi gida ke nan.
Akuma fadawa hjy ta fito don rana nayi yau yake son ya koma Abuja ba zai kwana ba kaduna .
Har lokacin banga lantana ba ba kuma danta a wurin har nakai ga tambayan sa, adatu wai lantana fa ?
Saida ta tabe baki kafin tace dani tana dakinta mana tana bakin cikin da dawowan ki tunda tayi shela a gari da cewa wai an sayar dake gun yan birni.
Wanan bakin cikine irin na hassada ga mairabo taki ne don tasan yanzu kinfi gaban ta har abada don haka ki daina saka zancen irin su a gaban ki yanzu.
Fitan Asabe a dakin ya ba hjy dama yin zancen siri da innar mu sun dan dauki lokaci don gaba daya hankali na ga yan uwana da muke zuba hira agefe daya suna murnan ganina.
Yan iya magana sunce kafin kaga biri biri shiya dade da hango ka tundaga nesa karfe goman safe dirka dirkan motoci uku suka tsaya a kofan gidan da muka baro zuwa kaduna yau da safe, a daidai lokacin da mu ke kan hanyar anchau zuwa garin mu.
Su shiddane tafe mutum.bibiyu a mota dayasuke tafe saida suka karewa gidan kallon mamaki dan girman shi da tsaruwan shi kafin su nufi hanyan shiga daga ciki.
Masu tsaron gidan ne suka dakatar dasu da tambaya wurin wa suka zo kallo rainin wayau hjy saudat tayiwa security din tana fadin zai bude kofa su shigo ko sai ranshi ya gama baci yasan kosu suwaye da zai tsaya tambayan su suda gidan dan su.
Yana tsaye ko wace ta fito da abinda take fada mai a lokacin saidai ya kallesu kawai bai iya furta komai garesu ba.
Yasan mami don suna haduwa a can gidan da wani lokaci yasa mami karasowa wurin da kanta gaisuwan girma yaiwa mami din tare da nuna sanaya a gareta.
Tambayan shi tayi da fadin ko grandma da wanan yarinyar da ogan su ya kawo suna cikin gidan nan ?
Da sauri ya girgiza kai tare da fadin babi kowa a gidan su kadai ne a ciki ko zan iya shiga in gani da idona mami ta fada.
Kofa ya nuna tare da dan dukar da kanshi alaman girmamawa a gareta ta nufi kofan sauran dake mara mata baya suka bi bayanta zuwa cikin gidan.
Bin ko ina na gidan da kallo sukeyi komai na gidan abin kallone don ya tsaru iya tsaruwa dai a kasan nan ba karya a cikin sa.
Saida suka gama duba ko ina na gidan guide din na tsaye daga kofa ya rufe fuskan shi da madubin ido baki fuska babu sauki a gareshi.
Da hannu mami ta yafutu wanda ke tsaye a kofa kamar an dasa shi a gurin yazo da saurin shi cikin girmamawa gaban mami din.
Are you sure grany bata gidan nan ko ta zauna tare da wata farar yarinya haka kai ya girgiza yana fadin baiga kowa ba a gidan nan yana fadi yasa kai ya bar gurin ya koma inda ya fito da farko yaja ya tsaya ba tare daya kara kulasu ba.
Yaran nan me suka mayar dani mami ta fada a hasale ta soma tafiya sauran suka mara mata baya suka bar gidan cike da takaici a ransu.
Duk da mami bawai ta saba da ciwa mutane mutunci bane a yau kan data sameni a gidan nan da tayi min cin mutunci ta uwa ta uba don ta kula ba karya mutane ke fadi ba na asirce mata dane da saddabarun mu na yan kauye.
Don wai ba a sako mu daga gidajen a banza kafin mu bargida sai anshirya mu da asiri idon mu idon mazan wasu da yayan su kamar yadda ya faru a tsakanina da ya Jafar din yanzu.
Duk abinda hjy maria ke fadi a gefenta mami bata samu bakin bata amsa ba a lokacin don burin mami ranan shine ta same tayi min koran kare tsakani na da danta.
Inyaso daga baya sai ta nemi shiri da hjyn su su shirya a tsakanin su sai gashi tazo ta samu gaba daya ma yadda ta samu labari mun rigada mun bar gidan a lokacin.
Gida ta dawo bayan ta sallami kawayen nata na birni da yanzu suke manne da ita koda yaushe suna kara sakata shagalta da duniya .
Dakin ta nufa kai tsaye don ta samu natsuwa a yadda take jin kanta magani ta fara sha kafin tabi lafiyan gado ta kai kwance.
A daidai lokacin da barci ke shirin daukanta ne wayan ta yake ruri a jakka har ya katse bata daga ba .
Wani kirane ya sake shigowa again da tsuki a bakin ta takai hannu tana daukan wayan dake cikin jakkan tare da duban screen din wayan nata taga sunan mama Ramatun tace ke kiranta.
Ramatu ta fada a fili tana dauko wayan zuwa kunnen ta tayi sallama tare da gaida ita da kwana.
Sama sama ta amsa mata gaisuwan mama Ramatu ke fadin sai ga hjy ta dawo yanzu wai ashe tana kaduna duk wanan neman da ake mata haka.
Kaduna fa mami ta fada da mamaki kafin tace kaduna