Showing 186001 words to 189000 words out of 191310 words
Chapter 63 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
aka ganka wanan aure ya saka zama mara kunya yanzu.
Mama ai idan ban kulata kuma bakwa jin dadi don amana take garemu baki daya a wurin nan ai.
Ni kaina nayi mamakin yadda ya bushe idon shi haka a wanan lokaci yana zuba masu rashin mutunci mutumin da baya magana sai yaso hakan.
Yanzu dai kinji mamaku tace saida matana zatai tafiya don itama tasan amdanin ta gareni ai shike nan gobe za a fara shirin tafiyan mu a tare.
Amma sai naga kamar ku tafi kawai da Ramatu don ko anje da zainab din can me zata iya maku banda karin nauyi kuma.
Wata daga cikin matan tace ba haka hjy je so ba ai gara dai a tafi da ita din zaifi ko banza ai gidan mijin tane za a.
Ni dai ina daga tsaye ina jin irin shawaran da ake yankewa a kaina akan tafiyan da hjy tace ayi dani tare da ita.
Mami bar wanan zance don Allah tunda hjy ce ta zabi yin hakan ya mamud ya fada a dan hasale yana kawar da kanshi gefe daya dan baiji dadin yadda mami din take nuna min a gaban mutane ba.
Saida muka fito daga asibitin yana waya har lokacin da muka baro dakin wani kuka yazo min lokaci guda tun ina kokarin rike kukan ban san lokacin da yazo min ba da karfi.
A rude yake fadin subbahanallahi ke ke maye haka wani abin akai maki yanzu ko meye ki keyi kuma zaki tayarwa mutane da hankali a banza.
Ban sauraren shi ba illa sheshekan kukan da nakeyi wiwi kamar an aiko min da mutuwa don bacin rai.
Umurni ya bawa driver da karfi ya dakatar da motar har na bayan suka tashi dakan motar da muke cikin sa Allah dai ya gyara basu dake mu ba din.
Wai me ke faruwane haka kika tayarwa mutane da hankali haka da kukan banza kaina na nade cikin gyalen dana yafa a jikina sai sharban kuka nake babu kakautawa.
Shirune ya dan biyo a mitan bayan security din shi sunzo ya karesu ta yanyar dakatar dasu da hannun shi suka koma baya da sauri.
Can na dago kaina a hankaki tare da hade hannayena a wuri daya ina fadin don Allah yaya ka mayar dani wurin iyayyena don mami ba zata taba kauna naba muddin ina tare da kai.
Ke kanki daya kuwa kike fadin wanan maganan gareni yanzu zaman mami kike a yanzu ko nawa da tasoki ko kada ta so ki ai ba akarkashin ta kike ba .
Dan Allah rufe min baki kada na saba maki yanzu a wurin nan haka kawai dan shagwaba zaki saka mutane a gaba kina min kukan banza.
Dan Allah yaya kayi hakkuri ka mayar dani gaban iyayyena ba zan iya zama haka mami tana kina a kullun ba tsanar da mami take min yana min yawa a zuciyana.
Maimakon inga yayi fushi sai kawai naji ya dan rungumoni zuwa jikin shi yana rarashi a cikin tsigan da ake rarashin yaro idan yana shagwaba wa iyayyen shi.
Saida yaga nayi shiru ya ba driver umurni ya tayar da motan har muka kai gida ba wanda yai magana a cikin mu.
Mota na tsayawa nayi saurin kokarin budan motar ta gefen da nake zaune saidai motar tana rufe har lokacin ba,a bude ba.
Sai lokacin na dan juyo da fuskana zuwa duban shi a hankali da fuskana daya koma ja saboda kukan da nasha a lokacin abu ga faran mace take gaba daya fuskana duk ya sauya kalar ja lokaci guda.
Ban yarda mun hada ido dashi ba nayi kasa da kaina don nauyin shi da nake ji yadda ya zuba min ido yana kallona da yanayin dana kasa fassaran shi ko na tausayine ko kuma wani abu.
Ki share haayen ki ya fasa a hankali don kada su dauka anyi maki wani abune idan kika shiga masu haka kinsan halimatu nada wayau sosai zata iya gane kinyi kuka.
Dole badon naso ba na share fuskana da gyale na yana kallona har lokacin kafin yaba driver umurnin ya bude motar na fita a hankali shikan ko motsi baiyi ba alaman fita daga motar.
Haka na dinga hada kafana har na shige cikin gidan nayi arzki babu kowa a falon suna cikin dakunan su do magariba daya kawo jiki.
Gado na fada na saki wani kuka gwanin ban tauayi ni kadai a dakin har na gaji naba kaina hakkuri na mike don gabatar da sallah saboda lokacin dake wucewa .
Ina wurin da nayi sallah a zaune na kasa tashi aka turo kofan dakin nawa fadilace ta shigo don ta duba ko mun dawo a lokacin ta samu mun dawo din.
Kallo guda tayi min ta fahinci cewa nasha kuka tare dani da sauri take fadin zainab meke faruwane yanayin ki ya nuna kinyi kuka haka mai yawa.
Zuwa tayi inda nake zaune din tare da zama a kusa dani tana fadin meya samu kuma zainab kun fita lafiya kin dawo da kuka haka ko yayi maki wani abinne kuma.
Kai na girgiza idona yana kawo hawaye nace a cikin kuka mamice dai ta tsanane bata kaunana har cikin ranta yanzu.
Meye laifi ne anty don kawai ya jafar ya aureni meye laifina tasan bada yarda na haka ya faru ba tsakanin mu ?
Baki da laifi zainab kowa ya sani amma zata daina ai idan ta gane hakan ba laifin ki bane kema nan gaba zata gane dantane mai laifin bake ba ni abinda na yarda dashi ke nan kedai ki kara hakkuri zainab.
Bafani nace ai tafiyan nan dani ba anty hjy ce ta kafe sai dani zata yarda ta tafi can inda yake zance ba zan tafi bane ni ?
Dake zai tafi zainab ta tambaya cike da mamaki a fuskan ta tana kallona kai na gyada mata alaman eh.
Za ako samu matsala wallahi saidai idan kin daure hakan ba komai bane zai zamo maki alheri ta wani bangaren rayuwa.
Anty idan mami ta barni ke nan har haka zai faru ni dai kawai gara yaya yace ya sakeni ko rayuwana zai zauna a cikkn sallama yafi.
Ina amfanin wanan zama namu da mukeyi hankalin kowa a tashe gara kawai ya sallameni na koma gidan mu in zauna a gaban iyayyena ko kasa sukeci muci shi tare dasu.
Ki bar fadin wanan magana kiyi addu,a Allah yasa hakan shine alheri a rayuwan ki dama kowa da abin ya shafa.
Anty kina ganin haka zamu zauna da sunan aure tsakani da mami da danta har ma da kowa daya shafi mami din ?
Yanzu fa a asibiti babu wanda ya nuna damuwan shi a kaina danaje sai hjy hjy kuma kinga ai tsohuwace basa jin maganan ta ko a yanzu.
Duk zasu bari ta fada amma fa idan kin jajirce wa kowa haka zai faru nidai shawarana har gobe gareki shine .
Kiyi kokari shakuwa da sabo ya shiga tsakanin ki da mijin ki har ki fahinci wani abu daga halayen shi na boye da baki sani ba tayi min wanka da jurwaye cikkn maganan ta.
Kaina daga hawaye naci gaba da zuba min a idona take fadin kwarai zainab don ba mami bace matsalan ki a yanzu matsalan ki shine mijin ki ya daukeki a macen aure ya dauko ki.
Kada kiji ina yawan fada maki haka ki dauka da wasa nakeyin zancena a a zainab akwai matsalan da nake hango maki nan gaba wanda yafi wanan da kika saka a ranki duk na mami shirmene gaskiya .
Anty wani matsalane wanan na tambaya cikin son karin bayani daga gareta kafin tayi murmushi tana fadin ba zaki fahinceni ba a yanzu.
Saidai shawaran da zan baki shine ki sa ido ga wa yanda mijjn ki yake mu,amula dasu sosai ki fahinci wani irin rayuwa yakeyi dasu.
Musanman wanan taju din don ni sam ban yarda dashi ba amma don Allah ki boye wanan zancen a cikin ran ki har lokacin da zaki gane wani abu din.
Sai ta kawar da zancen data dauko din da fadin yaushene tafiyan naku yanzu kuma mu a nan za a barmu ke nan ko me ?
Ban sani ba anty saidai tunda hjy za a kai asibiti ban tsamani tafiyan zai dauki lokaci ba don naji yana fadin za a soma shirin tafiya daga yau din nan.
Kai amma zanso na danje maki wani guri kafin tafiyan duk da hakan ba matsala bane gobe insha Allahu zan fita na dan je wani guri ai gara da naji da wuri tun lokaci bai kure muna ba.
Don haka kada ki yarda ki saka uwar miji a damuwan ki don irin su mami hakan suke son gani a gareki ko yaushe sai ransu su kuma yayi dadi da hakan .
Sun san komai ya lalace maki ke nan daga bangaren su har na mijin naki baki ba sauran kwanciyan hankali a tare dake.
Don haka ki saki ranki ki duba matsalan mijin ki dake gaban ki ba wanan shirmen ba da tana da iko ko auren ki ba zaiyi ba ai.
Ta fita ta barni da funanen meye wanan matsalan da kullun take kiramin ne ni har yau na rasa gane me hakan ke nufi waine wai ?
Ina shiri kwanciyane ya shigo dakin nawa ina saman mirrow zaune halimatu bata dade da fita a wurina ba don tun tafiyan msizube ta koma kwana tare da anty fadila watarana kuma mu duka ukun muke kwana a daki guda idan mu kadai ne a gida.
Wuri ya samu ya zauna bayan na amsa maushi sallaman daya shigo dashi fuskan shi a kaina yana kallon yanayi na a lokacin .
Saida ya zauna yake fadin kin gama kukan shagwaban naki ke nan ke sai yaushe zaki girma ne wai a gidan nan?
Daga cikin mirrow na dago kai muka hada ido dashi nayi saurun dukar da kaina kasa da sauri don ba zan juri kallon da yake min ba din saboda yanayin da hakan yakan sakani idan yana min wanan kallon.
Gobe sai ki shirya zamuje ai maki photo na fita waje saura idan mun fita kuma ki min wanan shagwaban naki da kika iya .
Ban tankashi ba har ya kare maganan shi ya fita waje sai lokacin na sauke ajiyan zuciya tare da fada da kaina watau shi wanan mutumin bai ma san ina yi ba ke nan ya mayar dani wahalalallah .
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA BAZAN GAJI DA TUNATAR DAKE KAN HAKKIN WANI BA WANAN LITTAFIN NA KUDINE DON GIRMAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA.
Yar uwa kada kiga namatsa da magana don tunatar dake sauke nauyin haki nake fadan wanan kalman a kullun don akwai ranan tambayan hakki ga kowan mu.
Kamar yadda fadila tayi alkawari hakan ne ya kasance don tun safe yati muna sallama kan zata duba haifiyarta da yara.
Sako ta bari a fada mai idan har ya neme ta bata gidan a fada mashi ta tafi duba mahaiyar nata bayan tafiyan ta sai gidan ya koma muna shiru.
Don hakane ba fito ba tunda ni kadaine a gidan kwanciya nayi daga nan barci mai nauyi ya daukeni har tsawon wani lokaci ina kwance.
Ashe shima ya fita zuwa asibiti duban hjy tun safiyan har lokacin daya dawo gidan baiji motsin kowa ba sai yan aiki dake aiyukan su a kitchen da wajen gidan.
Hakane ya bashi mamaki don rashin jin duriyan kowa daga cikin mu ba yasa shi zuwa dakina direct daya fito daga part din shi.
Kofan yake ta bugawa har sau uku ba a bude ba yasa kai tsaye ya turo kofan ya shigo dakin nawa.
Akwance ya hango saman godon nayi ruf da ciki ina sharan barcina hankali kwance sai hannuna dana danne da zai iya min ciwo idan na falka daga barci.
Sai gashina dake daure dan kwalin dana daure ya koma gefe daya da barcin da yai nisa a lokacin ban ma sanda hakan ba.
A hankali ya tako zuwa inda nake yana tafe yana kare ma fuskana kallo mai kama da barcin ma a wahalce nakeyin sa a lokacin.
Da dukawa yayi a hankali yana kokarin dan dagani tare da ciro hannun dana danne saboda dadin barci tare da sauke idon shi a kan fuskana kurruciyana da yake gani ko yaushe ya kara fito mashi fili a idon shi.
Yanayinb Numfashi da naji ya surku min duk da a cikin barci nake lokaci hakan bai hanani sanin bakon yanayi ya surkumin ba a lokacin.
Da sauri ba bude idona a daidai lokacin daya kura min idon shi a kaina shine tsaye a kaina saidai ina ganin hakan kamar duk nauyin barcine mafalki nake a lokacin.
Don haka na mayar da kaina saman hannun shi din da yake kokarin gyara min kwanciyan tare da juyawa a yadda nake kwance din.
Bai san lokacin daya dan saki murmushi a fuskanshi ba don wautan kurciyan daya ga nayi a lokacin har da Ac dakin ya rage min yadda yaga na koma takure na kwanta kamar sanyin yana damuna lokacin.
Saidaya fita daga dakin karan rufe kofan yasani bude idanuna da sauri tare da kallo kofan shigowa dakin.
Ya riga ya fita a lokacin sai kamshin turen shi daya bar min a dakin lokacin yake tashi ta haka na gane cewa ya shigo dakin a lokacin ba mafalki akeyi ba ashe.
Da sauri na zabura na bude idona tare da mayar da hankalina gun agogon bangon dake manne a bangon dakin.
Mika nayi kafin in koma in lafe ina runtse idona a hankali tare da tunanen meya kawo shi dakina a wanan lokacin.
Ganin anyi azahar har ana neman uku da wani abu yasa na mike zuwa ban daki da sauri na dauro alwala don sallah a zahar.
Ban fita ba bayan na idar don sanin da nayi yana gidan a lokacin ya hanani fita duk da na fara jin yunwa a cikina amma haka na daure na lake a dakin ban fito ba.
Banyi tsamani akwai wanda yasan tare da halimatu zamu tafi ba don koni sai a wanan shigowan na san da zancen tafiyan ta a bakin shi.
Ya shigo yana fadin yau ina wanan mai aikin naki ta shiga dago kai nayi na dan saci kallon shi tare da fadi ina wuni yaya.
Saida ya da bata fuska kadan nasan halin malam baushe ne yaki jini maikom in bashi amsa sai kuma na dauko mai wani topic yanzu na gaisuwa.
Bayan ya amsa min tare da maimaita tambayan shi garen ta tafi gaida mahaifiyan ta tace a fada ma kara daure fuskan shi yayi kamar hakan baimai dadi ba.
Kada ku dauki kaya mai yawa don tafiya ya fada yana daidai fita daga kofan dakin nawa daya shigo jin haka yasa nake masa kallon mamaki ta hanyar binshi da idanu.
Ko baki gane abinda na fada bane cewa nayi kada ku dauki kaya mai yawa daya wuce kala biyu ko ukku .
Nida wa kenan na tambaya batare da na shirya tambayan shi a lokacin ba saiji kawai nayi bakina ya subuce min lokaci guda ina tambayan shi.
Dake da sadiya mana ko a nan dama zaki barta kike nufi ya jefo min tambaya kamar a hasale yana kokarin juyawa ya fita daga dakin.
Nan ya barni zaune mamaki da imani ya cika min ciki don ban taba zaton haka ba daga gareshi sai tunane nake ni kadai a dakin .
Wai shin dama haka rayuwan shi yake kodai nine yakewa hakan yanzu don ina matsayin matar shi amma kuma naji ko anty fadila takan yaba kokarin shi sosai garesu kaf masu aiki a gidan.
Sai lokaci na tuno da ita don haka na mike ina zaton ta dawo zuwa wanan lokacin sai bayan magariba ta dawo gidan.
Inda ta leko dakina ta samu ina sallah a lokacin ta wuce zuwa dakinta ban fito ba saida na gama duk ibadan dana sabayi kafin in fito zuwa dakin nata.
Na shiga da sallama tana waya sai ido datayi min nuni dashi in zauna na nufi bakin gadonta na zauna tare da bin dakin da kallo.
Zainab kingani sai wanan lokacin na samu dawowa ko da sauri na juyo inda take tare da dan nisawa nadan sauke a fili na mayar da hankali gareta ina fadin sannu da dawo ya su mama yaran ?
Ban samu ganinsu ba don na fada maki inda zantafi ai tun jiya dan dama mama na bita wurinta na karbi sako tare da fada mata zancen tafiyan ki.
Dan murmushi nayi cikin jin kunyan abinda ta fada taci gaba da fadin tayi murna kwarai dajin haka tana maki fatan Allah yasa ki zauna can daga wanan tafiyan kusa da mijin ki kada