Showing 153001 words to 156000 words out of 191310 words
Chapter 52 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
gaban diyan nata ba a lokacin.
Mamud naci amanan mahaifin ku nayi sake da zamani ya cuceni ta fada tana komawa zaune yarfan saman kujera a cikin wani irin yanayi na damuwa da tashin hankali.
Jalal ya mamud ya kalla tare da fadin kai wai meke faruwane hakane naga mami a wanan yanayin ?
Ina fa daki kwance yazu ta kira ina zuwa take tambayana wai irin su culties din da turai da saura Asian countries ke sashi nake mata bayani shine na ganta a hakan ?
Da sauri ya juya inda mami take zaune yake fadin haba mami hakan ai ba kyau ki fara zargin dan cikin ki da kanki har duniya ta zarga mai hakan akan shi.
Mamud idan har jafar ya kasance a cikin irin wanan kungiya bazan taba yafe mashi ba a rayuwana ku sani.
Haba mami ki bar wanan magana don Allah ko akan dan wani ne balle naki yana illiminaties zai dinga sallah jamal ya fada .
Da sauri ta mayar da kallonta gun jamal din tana fadin Allah yasa hakan ne jamal na shiga uku da wanan yaron abinda ban taba zato da tsamani ba a cikin zuriata yana kokarin faruwa dani haka.
Jin sam batun na mami yai yawa yasa ya mamud dagowa da sauri a cikin bacin rai yana fadin kai jalal take her to her room kai jamal zo muje ya fada tare da fara tafiya.
Jamal din ya mara mai baya nan suka bar mami da Jalal yana kokarin lalashin mami din don ta daga su shiga part din ta su kaucewa idon yan aikin gidan a falo.
Ranan dai haka suka kwana a cikin tashin hankali a don kosu hankalin su a tashe yake kan wanan zancen sabanin mu dake gidan nasa tsundum ciki zaune sai damuwa da kewan gida kawai a lokacin ne a ramun babu wani tunanen komai a tare damu.
Kusan zance zuwa da matar malam.yai min dadi don sai ta zame min kamar hjy data tafi ga kuma halima da ba abinda ya dame ta a rai sai faman zuba surutu da tambayayoyi da takeyi hankali kwamce tana ci da sha duk ko da dare ne muka shigo gidan bai hanata bude ciki ta dura abinci ba.
Duk da munga shigan shi gidan a lokacin hakan baisa ya kwana nan tare damu ba gidan mami ya wuce ya kwana a can kamar yadda ya saba kwana din .
Da safe dan uwan shine ya tayar dashi daga barci ta hanyar buga mai kofa ya fito da mamaki yake kallon ya mamud din dake tsaye a kofa ciki damuwa.
Lafiya dan uwa ya fada bai bashi amsa ba tasa kai zuwa ciki dakin kai tsaye ya bishi a baya daga inda ya barshi tsaye a kofa .
Zama sukayi suna fuskantar juna na dan lokaci kafin mamud di yace kai abubuwa fa suna son baci a bangaren mami don yanzu kokarin zarga wani zance takeyi.
Daga baya ke nan ya fada yana mikewa tsaye don ni yau zan bar kasan nan da dare zan koma baki aikina ba zan dawo ba sai yarinyar nan ta gama zana exam din ta zanzo in tafi da ita.
Ya zakayi da mami mamud ya fada yana kallon dan uwan nasa yace cikin ko in kula akan mefa ?
Komai ma kana ganin zancen nan data dauko zata barka ka koma idan kuma har ka tafi kabar yarinyar nan baka gudun wani abu ya biyo baya .
Wani abin me zai biyo baya matace fa ba zaman kowa takeyi agarin nan ba yanzu sai zamana don haka duk wani mataki daya kamata na dauka akan hakan na riga dana dauka a yanzu ko.
Saida ya mamud din ya dan kurawa kanin nasa ido na dan lokaci kafin ya ware hannayen shi yana fadin shike nan har idan ka shiryawa hakan ai ba matsala.
A shirye nake ga duk wani barazanan da mami zata iya kawo min kan wanan matsala ya kare da fadin OK ga dan uwan nasa sai ya gyada mai kai alaman gamsuwa.
Bayan fitan dan uwan daga part din shi ya dade zaune a wurin yana dan tunane a ranshi kafin ya mike ya shiga bandaki ya watsa ruwa jikin shi tare da shiryawa kafin ya fito.
Kai tsaye part din mami ya nufa daga nan dakin yana rufe yasan tana gida don babu inda take fita idan ba wani dalili ba a irin wanan ranan ta jumma,a.
Da sallama a bakin shi ya turu kofan tare da dan rike hannun kofan kafin ya sake turawq ya shigo cikin dakin gaba daya.
Tana zaune a cikin shirin ta na doguwan riga leshi sai mayafin kayan dake saman jikinta da alama dai shirin fita take a lokacin itama duk da baranan fitan ta bane yau.
Tunda mami ta hango dan nata taji gabanta ya fadi don kwarjin sa sai kara fita fili taga yana mata tunda zancen auren nan nasa ya taso .
Wanda take gani a yanzu zancen sa ta fara zargi nasane ya fara baiyana mata hakan gareshi don wani asirttacen baiwa nasa da yanzu ta kara hangowa gareshi.
A hankali ya kai zaune a gefenta yana kamo hannunta tare da fadin mami antashi lafiya ya gida ya aiki ba tare dajin shakkar komai ba.
Cikin basarwa mami din ta jaye hannun ta tana fadi kalau nake tunda yanzu kana ganin kakai ba zaka iya bin umurnina ba koka fada min idan zakai abu.
Jiya me ya kaika kaduna ba tare dana san zaka shiga ba sai kawai wai inji kana min gida da wanan shegiyar yarinyar kauyen.
Yasa na ce ace kabar min gida tun kan na bata ma rai daga kai har ita sai in saba maku ba wani aiki bane gareni hakan.
Mami ai ba wanda ya fada min sakon ki sai yanzu nake jin hakan garwki but iam sorry hakan ba zai sake faruwa ba insha Allah.
A hankali ta lumshe ido cikin jin wani irin yanauin amsan daya bata din a cikin rashi damuwa da furcinta garshi ke nan.
Yau kaduna zan tafi ta bashi amsa tana mikewa daga inda take zaune lafiya dai mami zaki tafi kadunan ya tambaya cikin son jin amsan da zata bashi.
Eh akwai abinda zai kaini mai muhinmanci can yau din idan na gama da wuri yau din zan dawo garin nan.
Tana magana a cikin wani irin yanayi dake nuna akwai abu a zuciyar ta sake damun ta a lokacin shidai shiru yayi bai tankata ba a lokacin yana zaune a inda ta barshi.
Saiga jalal ya shigo dakin kallo daya yaiwa yayan nasa ya kawar da kai a cikin tsarguwa mami take fadin dauki jakkar can fita min dashi gurin mota kafin in fito.
Ok mami ya fada ya nufi jakkan ya dauka Allah Allah yake ya bar dakin a lokacin don a tsarge yake kada yai laifi a wurin yayan nasa kuma don ya dauka mami ta fada mai komai zai zargeshi.
Bayan fitan dan uwan da kaya shima ya mike yana fadin mami Allah ya tsare hanya ya dawo daku lafiya sai dai yau da yamman nan na nake son in, , , , ,
Jafar wani kungiya ka shiga da ban taba sanin kana a cikin wani hali ba sai daga bayan nan nasan da hakan tare dakai ba.
Mami kungiya kuma name ya fada yana kallon ta a ciki mamaki karara a fuskan shi don jin abinda ta fada mai din game dashi.
Wani cultu kakeyi jafar don jikina ya bani wani abu a game dakai ba dadewan nan ba.
Mami ya fada a cikin mamaki tare da fadin cult kuma ai da ina cikin wani cult din daba haka ba da yanzu na wuce sanin kowa a kasan nan ni wanan baya gaba ko kadan ya fada yana hade rai ya nufi hanyar fita daga dakin ta bishi da kallo kawai da nazari a zuciyar ta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4️⃣6️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GAREKU YAN UWA TARE DA KARA BAKU HAKKURI DA YANAYIN DA LABARIN YAZO MUNA SABODA KARATUANA A YANZU DON ALLAH A KARA GAKKURI DANI YAN UWA NAGODE, , , , ,
Zan iya cewa tunda gari ya waye ban leko waje ba daga dakin da muke ciki zaune mu uku din kamar muna gidan kaso don tun shigan mu gidan muka shiga sakin ba wanda ya fito daga cikin mu har halima dake daukin zuwa abuja din a lokacin.
Sai gata baki ya fara mutuwa tun ba,aje ko ina ba a lokacin tunda taji matar malam na fadin Allah ya cecemu da wanan gidan har za a yanka mutum a bizzime ba,a san an yanka kaba.
Hankali halima din ya fara tashi tun jin furcin Maizube matar malam din muna zaune ga gari ya waye zugun zugun a dakin da muka kwana din wanda shima munsan da zamu kwana ne ta hannyan kai muna kaya dakin danaga anyi yasa na jasu zuwa dakin muka shiga.
Kofan aka kwankwasa wanda yasa kusan lokaci daya muka dago kai zuwa kofan kafin a sake nocking na biyu wanda yasa nayi karfin halin mikewa zuwa kofan lokavin guda .
Na bude tare da kallon wanda ke bakin kofan a lokacin shine yana tsaye yabawa kofan baya ta hanyar saka hanayen shi a ciki aljihun wandon jikin shi.
Wanda jin karan budan kofan shima a lokacin yasa shi dan juyowa zuwa gun kofan mukai arba dashi da sauri na zube kasa don girmamawa ina gaida shi da kwana.
Bai amsa ba sai cewa da yayi zaki kashe mutane karfe sha daya ake nema baku fito kun karyaba har wanan lokacin haka ?
Dan daburcewa nayi na rasa me zanyi a lokacin don rudewa da nayi yau shine a gaba muke magana haka kai tsaye dashi sabanin da can da hjy kan muna shamaki a tsakanin mu.
Zasu fito yanzu na samu bakina na fada lokaci guda na fada ya juya ya bar kofan kamar maiyin sauri kada wani ya ganshi wuri lokacin.
Dakin na koma tare da fada masu abinda yace sai maizube ke fadin aiko nan ma aka kawo saimu karya ko.
Ciki da daurewa nake fadin kinsan su a table ake karyawa nan saboda haka mu fita zuwa falon inda zamu karya din yanzu, don yana fada wai naki fitowa daku can ku karya.
Maganan da maizube keyi yanayine dake nuna alaman tsoro da karfin hali a lokacin don gaba daya ta gama tsunkewa da al,amarin gidan ga baki daya.
A takure dai kowa yake haka muka iso falon dana lalubu muna inda dinning din yake da abunci a jere sama shi a aje muna.
Dole na nemo karfin hali da jarunta lokaci guda na sakawa kaina don kawai halimatu da matar malam da kiris suke a lokacin su fasa ihu a gidan don tsoro.
Basu ba ni kaina duk da zama a gidan mami ya taimaka min matuka saidai duk da hakan wani abu ban san shiba a gida wanan ne farkon ganina a gida nasa.
Abinci ne mai rai da lafiya aka shirya muna don karyawa wanda nasan halin yadda ake abin karyawa nawai don mu din bane yasa aka shirya hakan .
Kawai dai haka abin yake a garesu ko yaushe dan magana halima tayi min na zuba mata harara daga inda nake take fadin yayan mu duk wanan mu zamuci duka ?
Na watsa mata harara tare da cigaba da kurban tuwan shayin da nake kurba a lokacin a hankali duk zuciyana ina ji wani irin yanayi a lokacin.
Text ya shigo min a wayana na dan saci duba a hankali ko daga waye duk da wayana layin mutum.dayane a cikin sa lokacin.
Ki bisu a hankali kada ki takurawa bakina a gidan nan yin hakan yana cikin bin umurni na a yanzu kiyi duk abinda zakiyi su kwantar da hankali su gidan nan da kowa, ya rubutu min saida hakan ya ban mamaki don ban san a inda yake tsaye yana kallon mu ba alokacin.
Ki dibi duk abinda ranki ke so a gurin nan halimatu duk namu ne do mu aka ajeshi a nan na bata amsa a cikin dan wayen cewa da fuskana kamar babu komai a raina.
Ba laifin sun sake jikin kamar yadda ya kamata sunci abinci daga nan bamu koma daki ba a kokarina na bin umurnin shi a lokacin kamar yadda yace din.
Sai zuwa karfe daya saura ya shigo suka gaisa da maizube matar malam kamar yadda muke jin a gida kowa na kiranta da wanan sunan na maizube matar malam.
Ba wani sakin fuska ko sabo a gaisuwan ya mike tare da fadin halimatu zo naji mana ya fada ba tare da ya tsaya ba na kalleta itama ni din take kallo da mamaki tare da jiran umurnina .
Dan dukar da kaina kasa nayi kafin na dago na kalleta ta mike don ta gane me nake nufi da hakan daga kallon ta danayi din.
Tun ina zuba idon ganinta har na dan far tsoron haka sai gata tare da security din gidan niki, niki da kaya ana shigo mata dasu cikin gidan.
A hankali na sauke ajiyan zuciya tare da bin kayan da ake shigo dasu da kallo inda na dan fahinci wani abu a lokacin.
Maizube tana gefe a zaune itama dai ba sai an tambayi damuwa a yanayin nata ba lokacin har zuwa lokacin da suka gama shigo muna da komai acikin gidan.
Wata mace tayi sallama ta shigo da fara,a a fuskanta ta zauna suna gaisawa da maizube tare da muna bayanin itama a gidan zata zauna tare damu .
Itace wai mai aiki kula da komai yadda ya dace da fatan zamu ji dadin zama da juna yadda ya dace ta kare da fadin .
Itama dai musulmace yar uwan mu don haka mu sake jiki da ita don Allah don komai ya tafi daidai a gidan.
Abubuwan dake faruwa a lokacin koda nake yarinya mai san karancin shekaru da ban wuce sha shidda ba na dan fahinci wasu abubuwan a lokacin saboda natsuwa da fahintar dake gareni .
A waya yai min bayanin komai yadda zan fahinta daga kayan har yadda zamu zauna da matar data gabatar muna da kanta a matsayin mai kula da gida ya min bayani tare da ja min kunne akan komai.
Yana fadawa halimatu a ranan zaiyi tafiya bata fada min ba sai bayan mun sallame sallah a azahar tana muna hira fitan su da inda sukaje ashema ba tare dashi suka fita ba da wanan bakuwar matarce ta sayo muna kayan nan da akazo dashi gidan.
Kallom halimatu nayi tare da fadin yau zai koma ina ya fada maki halima tace yace wuri aikin shi kuma wai muyu karatu sosai kafin ya dawo.
Na dauka shirmen halimatu ne sai gashi da yamma kawai ya shigo yana sallaman maizube da niyar zaiyi tafiya a ranan zai dan jima bayana nan .
Ta shiga jero mai addu,an neman tsari da kariya a gareshi da alaman yaji dadin hakan don irin alherin da ya aje mata yana karbawa da amin ya mike.
Ta kalleni tana fadin wai nikan ba zaki bishi baje harda kinji zaiyi tafiya kina zaune a daki kinki ki motsawa tun dazun.
Ba don naso ba dole na mike nabi bayanshi kamar yadda tace dani din inyi sai gashi har muna kokarin cin karo dashi a kofan da sauri naja dan baya kadan kada mu gwaure .
Ya lura sarai da yanayin kaduwa dana shiga na kaduwa dana ganshi a gabana lokacin.
Tsadadiyar muryan shi ya ratso dodo kunne na yana fadin lafiya ina zaki tafi ko wani abu kike nema ne ?
Dan dukar da kaina nayi kasa tare da fadi a cikin dan damuwa dama dama dai na fito ne don in sallameka kawai ina wasa da yan yatsun hannuna duka biyu nake magana.
Yana tsaye yana kura min ido yana kallona tare da dan sake murmushi a fuskan nnasa tare da dan gyara tsayin sa dakyau har lokacin idon sa a fuskana.
Kamar aafalki naji muryan shi again yana fadin to ai gani saiki sallameni din inji tunda ke baki san abinda ya dace ace kinyi ba.
Kada ki manta komai da zamuyi a tsare yake a kan mu ba tare da kowa ya fahinta a gidan nan ba ina nufin kuwa har wanan yar aikin da zata zauna daku ba zata fahinci zaman mu dake ba kawai dai a matsayin mata da miji masu kula da junan su kowa zai dauke mu.
Na dago kai da sauri na kalleshi do jin abinda ya fada din sai yayi daidai da idon shi a kaina ya daga min gira da kafada tare da fadin idan kinyi hakan