Showing 132001 words to 135000 words out of 191310 words
Chapter 45 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
Babu wanda yazo wurin mu a gidan har kwana biyu tun hjy na daurewa har ta fara magana a fili ina jinta don ba wani magana nake iyayi ba a lokacin don zunlumin da nake ciki da fargaba.
Naji hjy ta fara fadin kamar tana zargin jikokin nata anya kuwa ya yan nan suna da gaskiya kuwa zasu dauko mu su dangwaran a wanan gidan babu wanda ya waigomu a cikin su kaf.
Idan an dan jima kuma zakaji tace ni mamuda nafi ganin laifi shi da keda wayau ya barmu a nan zaune ga masu zubin kafirai din nan sun hanamu motsawa nan da can.
Da iyanzu ai mun tsufa a gida da wanan zaman bamzan da bamu san dalilin yin shi ba a nan, wa yan nan katan banzan da suka saka gadin mu kamar mun aikata wani mugun abu.
Nidai bankan tankata idan tana wanan magana don tsorona Allah tsorona mami da bansa matakin da zata dauka a kaina da iyayyena kamar yadda ta fada ba.
Don har yanzu idona yana da kwancin jinin marin da taimin a fuskana yasa idona yai alaman kwancinyan jini ta geden dama.
Ga damuwa fara exam dina dake damuna shima don ina ganin nayi hasaran shi ke nan idan ba, Allah ya gyara ba ina da rabo a rayuwa lokacin.
Wanan yawan jininin na hjy yake kara tayar min da hankali tare da sakani tsoro da abinda take yawan fadi ko yaushe.
Saida mukai kwana hudu cur a gidan ba tare da wani ya lekomu ba ga zaman kamar zaman takura da mukeyi .
Iyakan security din nan ya shigo ya tambayemu abinda muke bukata duk daba wani amsa yake samu ba wurin hjy bai hana idan lokacin cin abinci yayi ya dawo garemu yana tambayan abinda muke so a kawo muna.
Koda bai samu amsa ba haka zai kawo muna abinci mai rai da lafiya da kuma abin motsa baki wani lokaci.
A yammacin kwana na hudune hjy ta sha fada har ta gaji saiga yaya mamud da Jamal sun shigo gidan muna zaune a falo mukaji shigowan su.
Da sauri na mike zaune don a kwance nake a lokacin don jikina babu karfi saboda tunanen da yai min yawa a lokacin.
Har kasa nake ina gaida su kamar yadda na saba a koda yaushe idan ina gaidasu din a cikin girmamawa.
Da sauri na mike don barin falon a lokacin hjy ta dubeni da kyau tana fadin ina zaki kuma ke ?
Dan dago kai nayi na kalli hjy tare da fadin zan shiga dakin ne hjy ki tsunci uwarwa a dakin ai yanzu tunda sun tuno damu fitan su fitan mu a gidan nan.
Shiru su yaya sukayi sai dan bina da satan kallon tausayi da yakeyi yana kawar da fuskanshi gefe daya hjy dake gefe taci gaba da masifa tana fadin.
Haka kawai , daku da uwarku zaku sakamu a gaba haka da wullakanci kamar kun samu marasa daraja da galihu kuna wullakantawa kamar baku san inda muka fito ba.
Ko uwar takuce ta hana ku biyoni nan don na mara maku baya kan abinda Allah bai haramta ba take kokarin ita ta haramtashi.
Dan murmushi ya mamud ya sake yana neman inda zai kai zaune da kyau tare da fadin korata kike kenan yanzu mu tafi.
Ba koranka nake ba ta sake fada gwanin ban tausayi kafinta tace kasan hakan da kukai muna baida kyau mamuda dole raina ya dinga baci.
Hjy kinsan lamarin mami saida tako dan haka muka nuna mata muma bamu san inda kuke ba a yanzu haka.
Don ta dauka kuna gida samu,naka sai yau da mama Ramatu ta bugo waya take jin bakuje can ba hakan ne ya tayar da hankalinta yau ga baki daya.
Kun min daidai yaran nan gara da kuka nuna mata hakan itama dana haifa bata san darajana ba ta barni a cikin dare nabar mata gida.
Kada ku yarda ku nuna kusan inda nake wasan dadi sai kun barta ta ji jiki da kyau kafin ku nuna mata inda nake.
Ke wanan tsohuwar da mugunta kike yanzun ma da mami ke cikin wani hali bai maki ba sai kin kara fitgita muna ita ke nan .
Ja,iri uwarka kake goyon baya ko mai na kasa daurewa daga inda nake zaune haka yasa na mike tsam zuwa dakin da muke kwana da hjy.
Gaba dayan su suka bini da kallon tausaya min hjy dake zaune ta nisa tare da fadin ina shi jafarin yanzun ?
Yana gida baida lafiya ne aida kun ganshi nan tun ranan ya mamud ya fada yana mikewa tsaye tare da fadin .
Yanzu ma shiya turomu muyi maki bayani don kada kiji mu shiru don baida lafiya sosai yace a gaida ke a tambaye ki idan ba wani matsala a tare daku.
Ko kuma idan wanan gidan bai maku ba a canza maku wani ya fada kai wanan shike kara saka kuna shagala da duniya diyan nan.
Wanan gidan ko a fina finan zamani ina na taba ganin irin shi da zai wani ce idan bai muna ba a canza muna wani.
Fada mai ni ba wanan ne yanzu a gabana ba canjin gida ko wani abu kawai ina son in koma dakin mijinane albshin shi yazo ya dauki matarshi ya san inda zai nufa da ita kuma .
Don dai yar nan ba zata koma gidan iyami da zama ba har abada indai da sunan irin wanan zama na wullakancin nan da tayi a yanzu.
Shima ai ba zai taba hakan ba hjy yanzu damuwan shi shine da wanda yarinyar nan zata zauna a karshe a gidan nan don ta karasa karatunta kafin ya bar kasan nan da ita.
Hjy bata iya ma ya mamud magana ba sai wani kallo data watsa mai kafin tace au ashe shi ba zancen mayar da yar nan hannun iyayyen ta yake a yanzu ba ?
Don Allah hjy ki bar wanan zancen kedai yanzu munzo muji zaki zauna a nan tare da yarinyar nan nadan wani lokaci ko gida samunaka zaki koma a nemo muna wace zata kula da ita.
Jikin hjy gaba daya yayi sanyi lokaci guda ta fara fadi a hankali yanzu yar nan idan na tafi na barta a haka yadda take tsorancen nan anya ba zata fada wani hali ba nan gaba don ko yanzu a firgice yar nan take nan.
Goshi ya dafe kafin yace hjy mami ta kafe shima jafar ya kafe da nashi kudirin wanda kowan su yana da nasa manufa a nan.
Zama hjy ta gyara a cikin mutuwan jiki ta fuskanci ya mamud tare da kura mai ido tana fadin mamuda ka hango abinda na hango gun dan uwan ka ke nan ?
Wanda uwarku ta kasa zama ta natsu ta gane me yake nufi da kakaman shi a kullun kan wanan yarinyar don ni har gobe zuciyata ta kasa sakewa da wanan zancen.
Don girman Allah idan akwai wani abinda kasani a game da dan uwanka ka fada muna mu sani tun yanzu.
Ina mara masa bayane ga kudirin sa don samawa kanmu mafitan da yake fada a kullun daga bakin shi kada idanuwan mu su rufe akan kudi daga baya muzo aji kunya.
Hjy abinda nake fadawa mami ke nan amma mami ta rufe idon ta gaba daya da za,a barni sai ince an canza mana mami din mune yanzu.
Murmushin manya hjy tayi tare da fadin yaro yarone itace dai iyamin ba wanda ya canza maku uwarku, sherin mulkine da lokaci ke rudin rayuwan ta ya aiki a kanta yanzu.
Sun dan dade zaune da ita suna mata bayani yadda zata fahince su a karshe dai suka yanke shawaran daya dace akaina da kuma hjy din.
Sun dawo gida sun samu mami zaune a falo suna shigowa mami ke fadin mamud anya ba boye min kukeyi ba kusan inda hajiyan mu ta shiga kuke boye min haka ?
Mami anbicika yarinyar ma bata gidan su ne ya tambaya kamar mai son jin amsa a lokacin.
Ni rashin sanin inda take bai dameni ba yanzu inda mahaifiyata take shine damuwana a yanzu mami ta fada cikin kunnan rai.
Mami ba saidana fada maki ba a ranan kinsan hjy sarai da rigima wai ita ta waye yanzu gashi tana shirin ballowa mutane aiki yanzu.
Jamal ka fice ka ban wuri kafin ranka ya baci a nan mami kyaleshi hjy ba zata bata ba a cikin garin nan ai insha Allahu.
Ta juya tana basu baya a cikin damuwa satan kallon juana sukayi kafin ya mamud ya mike yana fadin barin leka part dina in fito mami.
Har ya fara takawa yaji muryan mami ta tana fadin shi jafar din har yanzu yana kwance ne wai yake nufi ?
Mami yau fa saida dr Smith yazo har gidan nan ya dubashi jin bata furta komai ba yasa ya fara tafiya don barin gurin nata sai yaji tace me yace yana damun sa da yazo.
Jin abinda ta fada yasa shi juyowa gareta ya fasa tafiyan da yakeyi a lokacin yana fadin mami ba wani abu sukace ba ai su hudune da abokan aikin shi suka shigo dayan ke fadin ya saka wani abu a ransa sosai ne ya jawo mai hakan.
Baki mami ta tabe kafin tace idan ya halaka kansa akan wanan diyar tallakawan shiya sani don dai a karshe shizaiji kunya akan wanan yar har yake wanan shegantakun haka.
Dan murmushin takaici dan uwan ya sake daga haka ya juya ya fice zuwa part din su bai nufi wuri shi ba saida ya biya ya gaida jafar din wanda a lokacin ya dan ji saukin jikin yana zaune a saman dogon kujera a mike kafa.
Jikin shi na saye da jallaniyan maza sai bakin dogon wando dake kafan shi sai fararen santala, santalan kafanshi da suke a mike yana dan karkakadawa a hankali.
Jin shigowan mutum a dakin yasashi dan juyowa yana kallon kofan tare da sauke idanunshi kan dan uwan nasa daya shigo.
Har kun dawo ke na ya fada a cikin wani yanayi mai nuna alaman yana dan jin jikin shi har lokacin.
Mun dawo ina tare da mami a falo tun dazun ya mamud ya fada yana kaiwa zaune tare da kallon dan uwan nasa kafin yace dashi kun zauna da hjyn dai ko ?
Hjy ko yar rigima mun zauna saidai ta kafe akan lalai sai su tafi har gurin iyayyen yarinyar nan zainab sun zauna dasu kafin ta dawo nan ta zauna da ita ko kuma a turo wani ya zauna tareda ita din.
Saidai ita ta tafi ta barta nan don ba zan so tayi missing din exam din ta ba a yanzu bana son tayin kukan hakan akaina ya fada yana yamutsa fuska.
Yau zan je gidan da dare idan naji sauki da sauri ya mamud ya dago kai ya kalleshi tare da fadin kasan duk wani motsi mami ta saka muna matakan tsaro ko dazun da dabara muka kai gidan ai.
Baida matsala don ni a yanzu ko mami ta sani ba matsala bane a gareni yanzu don kawai kace mu fito mata ta wanan hanyar.
Kasan mami yanzu sai a hankali lamarinta zan daiso mu bita a sannu din ya mamud ya fada yana mikewa tsaye.
Bai samu zuwa gidan ba kamar yadda yacewa ya mamud sai kashegari ne da ya kasance weekend ya fito zuwa don fita .
A falo ya samu yan uwan shi tare da mami ya fito cikin shirin shi tsab ya nufo inda suke zaune ya zauna a tsakiyan mami da Aisha yana dan jingina jikin shi a jikin mami din .
Cikin rashin ko in kula abinda ke faruwa a tsakanin su da mahaifiyar nasa normal kamar yadda suka saba a tsakanin su.
Daga haka kowa na fira ya ja bakin shi yai shiru lokaci guda sai Aisha dake zaune a kusa dashi takura mai ido cikin tausayin yanayin shi take fadin.
Ya J jiki yai sauki ke nan sai ina kuma yanzu ta fada a cikin zolaya sai taga bama sauraren ta yakeyi ba a lokcin.
Aisha tayi masa kuri da idanuwa tana kallon shi sai tausayinshi ya kamata lokaci guda ta sake fadin ya J ko jikinne har yanzu you look so warried.
Shiru bataga ya motsaba hakan ya tabbatar mata cewa yayi zurfi a cikin tunane gyara zama tayi a cikin kulawa a gareshi ta kara ambatar sunan shi da ya J ya akayine wai ?
Yayi firgigit ya dawo cikin hayacin sa tare da sake mata takaitaccen murmushi a fuskan shi cikin dan basarwa ya fuskamceta yana fadin.
Aisha ina tunanen tafiyanane ga kuma yarinyar nan zata fara zana exam a cikin kwanakin nan.
Da sauri Aisha ta dan saci kallon mami dake zaune a gefen su kafintace ya j wace yarinyar kake magana ?
Yace wife dina ko akwai wata da zanyi zancen ta haka a gaban ku bayan ita kin sani kin san ba wanan a gabana ai Aisha.
Da sauri Aisha ta dukar dakai kasa a daidai lokacin da yake mikewa tsaye yana fadin zan fita daga can zan leka asibiti in dubasu.
Aisha najin abinda yayan nata ya fada tayi saurin dago kai ta kalleshi da mamaki take girgiza kai tana kallon shi tare da fadin.
Amma ya j ka tafka babban kuskure da har ka daurawa kanka aure da wanan yarinyar da tsiya ya saka iyayyen ta sakota shigowa duniya don neman kudi.
A fusace ya juyo yana fadin shut up Aisha enough enough what ever she is, now she is free from that.
Idan ba zaki taimaka ki samo min mafita akan zainab ba to ki ja bakin ki kiyi shiru da maganan matana a gabana haka.
Kar ki manta she is part of us now don ta zama daya daga cikin mu ke nan kamar kowa wani kallo mami ke jefa mai kamar an hanata magana a lokacin.
Ba wai wani abu bane ko tunane mami keyi tsaban mamakine kawai daya rufeta a lokacin ya hanata nagana don gaba daya sai take ganin yanayin shi ya sauyawa sanin ta a yanzu.
Itako Aisha sai kai take girgiza mai tana fadin ya j kada ka tafka babban kuskure kazo daga baya kana daka sanin hakan da kayi.
Don tallaka ka barshi yanzu inda ka ganshi da tsiyar shi shine mami ke maka nufi ba komai ba ya J a matsayina na kanwarka ina mai baka shawara domin mami ba zata taba yarda da ita a matsayin daughter inlaw din ta ba tunda tasan asalin ta tun farko.
Waike Aisha ba zaki kamawa mutane baki ba a nan ke meye naki a cikin zancen nan manya na magana ki dinga saka masu baki haka.
Har ya fice falon mami sai faman tunane take akwai wani abinda ke damun dan nata domin gaba daya shi yanayinsa ya canza mata.
Babu alaman jin nauyin ta a idon shi ko bin zabin ra,ayinta kamar yadda ya saba nuna mata a baya don zata rantsewa da cewa yafi ko wani yaro mata biyayya a cikin yayanta kaf.
Duk maganganun da yayi a lokacin bai daga mata hankali ba sai bakon yanayin data fara hangowa a tare da dan nata ne hankalin ta ya fara tashi da hakan.
Ta shiga sake sake a kasan zuciyar ta ya zama dole gateta ta fuskacin danta tasa yanayin da yake ciki har ma idan asirine ta san wani irine aka jefoshi dashi.
Don tasan matakin da zata dauka kafin dan nata ya kaiga shiga wani hali bata farga ba do zuciyar ts na raya mata jafar din yanayjn sa y canza ga baki daya a dan kwanakin nan.
Ina zaune na rafka uban tagumi sai hjy dake sallah a gefe naji an turo kofan shigowa falon da muke din.
Jin haka yasa ni saurin dago kai don ganin wanda ya shigo falon duk da dai nasan mazan nan ne dake faman dawainiya damu tun zuwan mu gidan basu huta ba.
Saidai kuma dago kan nawa yayi daidai da shigowan ya jafar din falon da daddadiyan muryan shi da yake sallama daga inda yaja ya tsaya tsaye fuskan shi a gurina kai tsaye.
Sallaman na amsa a daidai lokacin da yake lumshe idon shi a cikin wani irin yanayi kafin ya bude yana mai takowa zuwa in da muke zaune.
Kaina na sada kasa cikin sauri a daidai lokacin da hjy ta shafa tana fadin yau a gidan duk da ina cikin fishi daku har uwar taku.
Ya karaso inda take yana murmushi mai hade da sautin dariya yana fadin a yafe muna nima hankalina yana gurin ki ga baki daya wallahi.
Sai daya zauna suka fara gaisawa dashi yana tambayan ta ya zama kadaici ya kuma hakkuri da abinda ke faruwa.
Tace duk suna nan tanayi saidai zaman ne gaskiya guri