Showing 87001 words to 90000 words out of 191310 words

Chapter 30 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

cewa da tayi min in yawaita yawan ibada in roki ubangiji sauki.
Naji dadin wanan shawaran da tsohuwar ta bani sosai don duk kunci dake zuciyana sai na nemeshi na rasa washe gari naji na tashi raina ya sake duk da mutanen gidan basu daina halin da suke min sai dai ko dunyima hakan bai damuwa na yanzu don shawaran dana samu daga tsohuwar.
Ga kuma iyayyena da nakejin tsoron lefin da basuji ba basu gani ba yazo ya shafesu ya zama dole a gareni in daure ga duk abinda zan gani don yakin nawa ni kadai kamar yadda hjy din ta fada min kar in yarda in kada iyayyena ga tashin hankali.


ZAINAB IDRIS MAKAWA








🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅




ZAINAB IDRIS MAKAWA




JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI FATAN ALHERI GA MUSUMAI DUNIYA BAKI DAYA AMIN, , , , ,



Yar uwa ban son ki da shiga hakkin wani ko wata don Allah kiyi kokari ki biya kafin ki karanta kada ki raina hakkin wani a kanki gara ace kece mai bi da abiki.
Allah ubangiji ya bamu ikon aikata alheri da fin karfin zukatan mu Allah ka sadamu da rahamomin sa amin.
Mami ta shigo dakin wurin hjy a lokacin ina zaune ina gyarawa hjy kayan ta da aka wanke don da ta cire kaya zan dauka in hada danawa in wanke tas.
Shine hjy ta tsayar dani in gyara mata jakkar kayanta muna dan hira ina dariya don gareta kadai nake jin dadi a gidan bayan ita sai dan dama anty Aisha duk da yanzu itama akwai sauyi sosai a fuskanta gareni.
Mami na shigowa dakin saidana kadu dan fargaban daya ziyarci zuciyana lokaci guda don yanzu ina tsoron ta sameni a dakin tare da hjy saboda kada ta yi min cin mutunci.
Don haka nake iya kokarina wajen kaskantar da kaina a garesu kamar yadda suke nufi da zancen su gareni.
Ba wai suna takuramin ga hakan bane saidai ko sakin fuska ance rahamane to babu wanan yanzu tsakani da kowa a gidan sai hjy sai ko yan samarin mami jalal da jamal da basu taba nuna min wani canji ba a fuskokin su.
Kamar yadda muka saba hakan ne har yanzu a wurin su do shi jalal sarkin wasa har yakan min ba, a da fadin amaryan mu.
A cikin wasa hakan yasa yanzuma dana fito daga dakin hjy na sameshi zaune tare da yan matan gidan yana cin abinci suna hira nazo zan wuce zuwa kitchen wurin su mama kande.
Muryan shi naji yana fadin a, a ke kuma armaryan mu yau ko dan gaisuwan ban samu ko dai har kin fara amarcin ne mu fara kawo gaisuwa don yanzu ke dan kin zama key a gurin mu sai an murdaki za a bude,
Kai kai haba jalal wanan irin maganan kesa kuna kara hurawa yarinyar nan kai amaryan wa kuma wanan yar kauyen yar aikin kakewa irin wanan maganan.
Sai ta dauka kamar daidai take da kowa a gidan nan yanzu don dan kauye bai iya samun wuri ba.
Wuce daidai yanzu tunda har ta iya halbo zuciyar ya J aiko tafi kowa ke nan dai a yanzu tunda ta doke duk yan matan dake garin nan kai bama garin nan kadai ba duk kasan nan zance.
Ya jamal naci karo dashi da sauri na dan duka ina gaidashi da kwana yadda na saba na shige kitchen haka yasa ban ji sauran maganganun su ba a wurin.
Ashe a bayana har zancen yaso koma masu fada don Rufaida ta dauki zancen da zafi har gaban mami saida maganan ya kaisu.
Mami kan jalal taiwa fada sosai a wurin jamal yace haba mami kina wanan maganan haka gaban kowa bayan yarinyar nan kin sanda cewa itace dai ya jafar ya tsayar zai aure kice kika sanda wanan zancen a yanzu.
Amma shi ya J din ai ya dade da nuna yana kaunar zeey din ki tun muna abuja da kika fara ganin su wurin dinner rantsar daku .
Dalilin kine fa har ya J ya fara kula yarinyar nan yanzu kuma kina fadan wanan irin maganan a kanshi idan bakya son wanan abin ki mayar da yarinyar hannun iyayyenta kowa ya huta idan yana so sai yaje can gurin iyayyenta ya nemeta.
Kai jamal ka rufa min baki da wanan bakar maganan da kake fadi duk yan matan dake garin nan ace baiga wace tayi mashi sai wanan zeey din da bata da asali yar kauye.
Meye to aciki mami ya tambaya da mamaki yana kallon ta tare da fadin itace fa zabinsa mami don me kike kokarin kawo matsala a cikin zancen nan yanzu ?
Jamal ta fada a cikin tsawa tare da fadin ka fita a idona tun kan ranka yakai ga baci dama halin ku daya da Jafar ai don baku san ciwon kanku ba.
Mami don kawai na fadi gaskiya ki barshi mana yayi abinda yake so zaifi ace kin takura kanki akan wanan magana.
Yana fadin hakan ban tsaya sauraren me zata fadaba ya juya wurin jalal yana fadin kai ya mutafi ko ?
Jalal din dakewa mamin su kallon mamakine ya mike yana fadin mami zamu tafi wurin ticket din don a samu da wuri sai dai bamu san na mutum nawa za,a saya ba idan munje.
Ajiyan zuciya mami ta sauke don yanda ranta ya baci da zancen yaran da safen nan tana fadin naku sainawa da hajiya da Aisha Nuriya da yaran tunda shi mamud din ya tafi tun jiya.
Mami zeey din bada ita za, a tafi bane wanan karon ko a nan za a barta ne wanan karon kinsan fa basu haduwa dasu Rufaida a wuri daya ko banza.
Ya za a barta a nan jamal ya fada dole ai da ita za a tafi ko dan taimakawa hjy wa zai iya da lalurar ta idan ba ita ba.
Jin wanan zancen yasa mami ta danyi tunane kafin tace da ita zamu tafi amma mota zatabi wanan karin ita dasu kande da lami da drivobi.
Haba mami ai hakan ba girman ki bane yarinyar nan meye laifin ta dankine fa duk yaja mata koma meye a wurin ku zeey din nan tana da halin kirki gun kowa.
Kallon data watsa masune yasa su fita daga dakin da sauri har suka kai wurin sayar da ticket din suka sayo jamal yace su hada da nawa su saya koma me mami zatace dai sun saya ai.
Hjy kawai zamu fadawa da mun koma gidan zai fi suna wanan maganan ne wayan ya jamal yayi kara ya dauka da mamaki yake kallon wayan daya nuna lamban kasar South Africa.
Waye kuma ya kirani daga south africa ya fada yana nunawa dan uwan nasa dayake tuki a lokacin.
May be wani friend din kane ko ya fada shima yana kallon lamban kafin ya mayar da hankalin shi ga tukin da yakeyi din.
Jamal kuma ya dauki wayan da hello muryan dan uwan shi jafar yaji yana fadin kai jamal ya kuna lafiya ya mami.
Ya Jackson kaine kayi nisa fa ka daga hankalin mami sosai don har yanzu bata koma daidai ba rashin jin inda ka shiga.
No ball kawai nazo kallo don in samu natsuwa a tare dani ya kana gidane ko waje ya tambayi dan uwan nasa.
Wallahi ya gamu nan munzo yankar ticket gobe zamu koma Abuja mami zasu fara aiki monday din nan mai zuwa.
Wanan yarinyar fa ya tambaya sai jamal din yace yanzun haka zancen ta muke a mota don mami tace wai kada mu yanki ticket da ita a mota zasu tafi ita da sauran yan aiki kamar ta.
Yanzun fa ya tambaya No mun yanko da ita zamu hada da hjy saitawa mami magana fine idan ka koma gida kayi flashing layin nan zan yi magana da ita ok ya nagode take care.
Sun dan biya wani guri kafin su dawo sai bayan sallah azahar suka dawo gidan a dakin hjy suka sameta ita kadai a dakin sun gaisa take fadin yau bata gansu ba tun safe.
Jalal yace dazun na shigo da niyar idan nagama karyawa in shigo mu gaisa sai wa yanan yan rainin hankalin suka so raina min wayau suka ja har mami tayi min fada kan yarinyar nan zainab.
Nan dai yake fada mata komai har zancen sayo ticket din da sukayi dani take fadin sun mata daidai don daba haka ba ko ita ba zata tafi ba idan ba wanan yarinyar cikin su don ko taje wa zai kula da ita a can kamarta.
Karbi waya wani ke son magana dake ya fada a dake sai ta watso mai wani irin kallo tana fadin wani wa ka samomin da yake son magana dani.
Wayan ya kara mata a kunne jafar din yana jin rikicin da sukeyi a dakin yana murmushi kafin yace ke tsohuwa kanki nake so nawa zaki sayar min a turo maki kudi gobe nazo na sare.
Dan nema mai muryan turawa ka dauka ba zan sheda muryan ka bane halan ?
Jafari ina ka shige kabar mutane a cikin damuaa haka kan dan magana kankani ka yankewa kanka wanan hukucin.
Ashe kai baka cika jarumi ba kaja fadan da baka iyawa da uwarka na dauka kai cikkaken jarumi ne ashe ba haka ba.
Matsoraci kawai yace lailai tsohuwar nan kin gama sani yau zan ko gwada maku ni jadumine da bai magana biyu.
Ni baka da bakin fadar komai yanzu a gabana tunda kaja fada kabar yar mutane nan da yaki ita kadai.
Hjy wa ya isa ya yakar min mata ban gama dashi ba ai ita mami ta sani tasan bana magana biyu yasa na bata wuri ta sauko daga fushin data dauka.
Yanzun dai ba wanan ba wallahi tafiya ne ya kamani gani nan a kasan africa ta kudu nazo wani abu zan dawo da yardan Allah nan zuwa jibi idan Allah ya kaimu.
Nikan daka ban mamaki sai ince wanan jarumin nawa bai cika jarumin maza ba ashe a duniya.
Yanzu dai hjy ina yarinyar take don nasan nabar sarkin yaki a gida yasa ban daga hankaliba ga zancen.
Yarinya kan na nan tana fuskantar matsi da tsangwama don har tayi niyar guduwa wallahi na dakatar da ita daga hakan.
Kallon juna jamal da dan uwanshi sukayi shikuma yana fadin hjy don Allah kada ki bari ta gudu daga gidan nan idan na dawo zan sake zama na karshe da mami akan zancen.
Bazata ko ina ba a yanzu kan sai dai ban sanarwa gaba ba idan ka kasa shawo kan uwartaka kan zancen.
Ba jamal waya yace jamal din ya karba yake fadin idan mami ta tambaya ka fada mata nine nace a saya da ita.
An gama yaya ya fada yana dariya suka danyi maganan su kafin yace jamal din ya ban wayan.
Ina kitchen abinci lami ke kwasa ina mika mata ledan da take saka tuwon data tuke a cikin sa naji muryan ya jalal na fadin ke zeey karbi waya ana magana dake a bayana..
Sai da gabana ya fadi kanfin in juyo ina fuskanta shi bai tsaya jiran komai ba kawai ya ban wayan na karba.
Tare da karawa a kunnena gami da sallama duk da bansan mai magana ba a lokacin amma sai da nayi sallaman dan koyi da sunan ma,aiki S A W .
Ajiyan zuciya naji an sauke wanda hakan ya tabbatar min dashi ne a layin duk da ban tabbatar da hakan ba lokacin.
Ido lumshi yana maijin wani iri a zuciyar shi ya amsa sallaman tare da fadin ya kike kina lafiya ko kina nan kina aikin kuka da tunane ?
Ko baki maganane ya fada kamar bashine jafar din mami mai yawan daure fuska ga kowa na gidan ba in badon ina yawan zama da hjy ba ina ganin yadda yake sakin jiki a gaban tsohuwar zan iya rantsaewa da baya dariya tunda yake don yawan daure fuskanshi koda yan uwan shi maza.
Sai yau gashi shike min magana mai kama da ba,a a kunnena haka ina jin shi.
Sake maimaita abinda ya fada yayi yana fadin ko bakiji mena fada ba kina nan kin saka kanki a damuwa ko ?
Aa,a na samu kaina da fadi a cikin sanyin murya ina mai girgiza kai kamar yana gabana a lokacin.
To ki daina damuwa don banga laifin ki ba ko kadan a ranan don na gama fahintar dama ke matsoraciyace sosai.
Ko kin fasa taimakawa yan uwar ki da innan kine in sani don in kyaleki in neme wata.
Daga inda nake na dan runtse idanuwa don da ace shidin sa,a nace da zan so haka ya kasance ko dan kyaushi da wayewan shi saidai nasan shirme nakeyi don wutsiyan rakumi yayi nisa da kasa.
Shi din ba ajin irin mu bane yayan talakawa kamar yadda mami ta fada muryan shine ya katse min tunane yana fadin.
Da kun koma abuja zakici gaba da karatun ki don nayiwa mamud magana yanzu ma abinda ya kaishi Abuja ke nan zancen karatun ki don zanfi son sai kin kamala secondary kafin in aure ki mu tafi.
Nagode yaya na fada a dan kunyace danaji zancen karatu Allah yasa dai kina da kokaerin karatun kamar yadda nake zafo ya fada.
Gane bazanyi magana kamar yadda yakeso ba yasa shi fadin ni zan kashe tunda har da magana a hanaki yi dani yanzu.
Sai an jima nace a kage don na matsu ya kashe wayan in huta da wanan bugun zuciyar danake ji a lokacin.
Maimakon naji ya kashe din sai ji nayi yana fadin kingaji dajin muryana ne to idan kin gaji ni ban gaji ba zan iya barin wayan a haka har lokacin dana gama sauran bugun zuciyarki da numfashin ki tunda naga a tsorace kike.
Ban kaiga sani anmsar da zan bashi ba sai muryan Nazira ke fadin ji min yar iska ana aiki kinzo nan kin labe kina waya da maza ko ?
Uban wama ya baki wanan wayan dake hannun ki haka ko sato wayan mutane kikayi kina waya dashi yar iska muga wayan har sata kika fara a gidan nan ashe yau Allah ya tona maki asiri magen banza mai kwanciyar kwanto ayi sake tayi wuf da abin mutum.
Duk abinda take fada a cikin kunnen ya Jafar yana ji bata farga ba don bata kai ga karban wayan ba tana shirin tara min mutane a wurin.
Shigeya yar kauye mara gata da asali watau ke kinzo birni kinsha jan miya har kina kokarin sace zuciyar dan masu gida da kissan ki na yan kauye ko ?
Ki rasa wanda zaki likewa kamar chewing gun sai ya J da kowan mu a nan take zaman jiran shi mutumin da ko ganin shi tsadane a wurin mu.
Ke amma dan bakin tsafin ki da maitar ki har kika iya sanin yadda kika ja hankalinki gareshi yasan da zaman ki gidan nan maza ban wayan naga ko wayan waye kika sace.
Idona ya riga daya ciko da ruwan hawaye a cikin karfin hali nake fadin ni ba barauniya bace kuma bana maita waya kuma ba satan shi nayi ba ya jalal ne ya kawo min shi yanzu da kansa.
Lami daga gefena take fadin haba Naziran hjy yanzu fa jalal ya kawo mata wayan nan muna tsaka da aiki ya miko mata shi.
Karyane wallahi satoshi tayi yar iska watau ke zaki goya mata baya ta dinga muna barna a gidan nan wallahi yau sai kowa yaji sata ta fara muna don kowa ya kankanta kayan shi tunda muna tare da barauniya.
Wallahi ni ba sata nayi ba na fada don ni ko tsinken wani ban taba tabawa a gidan nan na samu kaina da fada cikin sheshekar kuka sai ga Rufaida da salma dake falo sun shigo suna tambaya take fada masu.
Wallahi yarinyar nan na kama ta sato waya tana magana dashi a nan Allah ya kawoni da maishi yau yayi hasara iphone ce kamar ta jamal salma ke fada.
Ba sata nayi ba anty salma yanzu ya jalal ya kawo min wayan inyi magana karya take Nazifa da Rufaida suka hada baki wurin fada.
Satan shi kikayi ke har kina da darajan da zasu baki wayan su shegiya yau Allah ya tona maki asiri don dole sai kin bar gidan nan yau.
Hasken da wayan yayi daga hannuna yasa salma fadin dawa kike waya yar mami a hankali na dago kai na kalleta kafin in mayar da kaina a kasa ba tare dana bata amsa ba.
Dawa ko zatai waya banda munafukan iyayyen tan nan dake mata tsafi a gida.
Nazifa kin san koda ya J take

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login