Showing 120001 words to 123000 words out of 191310 words

Chapter 41 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

hjy dake zaune a kasa ta mike kafafuwan ta tana daga zaune.
Anchau ne garin mu na fada a sanyayye sunan mahaifin ki fa ma,ana yadda za,ayi saurin gane shi a garin.
A hankali na dago kai da yan yatsuna dake a harde guri daya ina wasa da yan yatsun hannun nawa nace.
Unguwar sarkin harbi muke da anje akace Habu mai faci dan gidan Asabe za a nunawa mutum gidan.
Dago kai sukayi suka kalli juna da hjy kafin yace dani ida an fadi hakan kawai za a gane nace eh ko ace gidan su Asaben sarkin harbi marigayi.
Yace shike nan jeki bayan yayi dan rubutu a wayan dake hannun shi ya juya wurin hjy yana fadin hjy zan tafi ina da inda zan tafi wanan ne ya dawo dani dama.
Sai bayan danaga fitan shi na dawo dakin na samu hjy tana kokarin diban abinci da kanta taci nasan ta gaji da kirana ko yaushe tunda ta gama fahintar halin da nake ciki na tsoro a gidan yasa ban faye zama kamar da a dakin ba yanzun.
Da sauri na karasa na karbi cibin a hannun ta na fara zuba mata a plate na gama ina rufe warmer din abincin take fadin kefa ba zakici bane yanzu ?
Da sauri na dago kai ina girgiza kai tare da fadin mami tace in daina ci a nan yanzu naci a gurin su kande ai.
Ikon Allah ita iyamin ta fadi hakan akan me zata hanaki cin abinci tare dani zama a gidan nan bai ganni ba don iyami ta bata wayau ta gareni yanzu.
Tsoro da fargaba ne suka ziyarci zuciyana lokaci guda nan na shigawa hjy magiya don nima saida na fada nagane nayi kure wurin fadin hakan a gaban hjy.
Zauna maza ki debi abinci muci ta fada a hasale rai bace da sauri na zauna na dibi abincin na fara ci don kada ta kawo wani zance.
Kamar daga sama ya fado dakin da sallama yana saye cikin shada mai ruwan dark ash karamin dinki na maza akaiwa shaddan ta dan matse a jikin shi kadan.
Ya shigo dakin a daidai lokacin da hjy ta mike zata shiga bandaki ganin shi bai hata shiga bandakin ba a lokacin.
Dadircewa nayi na rasa inda zan saka kaina ganin dagani sai shi a dakin ina wuni yaya na fada tare da dan rusunar da kaina dake kasa ina wasa da spoon din da nake cin abinci dashi.
Queen baki ganni ba baki ji wayana ba baki damu da kisan inda nake ba kuma ko ?
Saida nayi dan dum kafin in samun kaina nayi bakina na fadin kayi hakkuri yaya .
Yaci gaba da fadin a cikin harshen turanci a yanayi na tausayawa yake fadin Queen idan na kira wayan baki dagawa ya kike son inyi da raina ?
Queen kin kuwa san halinda nake a ciki saboda ke yanzu kuwa akan ki Queen zan iya komai, komai ma da baki zata ba my Queen.
Ki kallafa yadda na koma dan rikicin ki da mami ban taba samun matsala da mami irin wanan ba a rayuwana.
Na rame saboda ke saboda kece zabina duk nayi wanan lalacewan haka ke bakya tausayina ne wai ?
Nikan kasa magana nayi kaina yana duke a kasa din ba zan iya dago kai koda wasa in kalleshi ba a lokacin.
Don na shiga tsananin rudani da tashin hankali ga kalaman shi don abin kamar almara wai a kaina mutum kamar ya jafar ke wanan maganan.
Addu,a na soma don kariya daga ko wani irin masifa da yake son jefani a ciki don har lokacin duk da nake yarinya kalaman hjy yana yawo a raina.
Da take fadin ta fahinci yana da wani manufa daya boye akan aurena daya nace sai ni wanda mahaifiyar shi ta kasa gane hakan.
Wanan tambayan nakanyiwa kaina har yakai ina tsoron idan ba yankani ko sayar dani yake son yi ba don kawai banda gata a rayuwana don idan maganan hjy ba gaskiya bane don me yaya jafar zai tsalake kyawawan yan mata da mami ke taya mai ya nace saini.
Ji nayi ya sake tausasa muryan shi yana fadin Queen kece zabina don nasan kece zata iya hakkuri da yanayina da yadda nake.
Nikan kara tsorata nayi a raina don tabbas maganan hjy ya tabbata ke nan tunda yanzun ma ya fadi hakan da bakinsa a gabana.
Ban kai ga karshen tunane ba naji yaci gaba da fadin ni nasan kina sona Queen don ba zaki kini ba saidai saboda mami kike kokarin boye hakan ga kowa a zuciyar ki.
Zamu taimaki junane dani dake a rayuwan mu don kece kadai na yarda da inzauna da ita a tsarin rayuwana ba ko wace mace nake son aura ba.
Don haka ki taimakeni Queen ke kadaice na yarda da ita a rayuwana ina son na kasance a tare dake don mu taimakawa juna dana tare damu duk hukkuncin dana yake kada ki ki hakan ki yarda da kaddaran rayuwan mu.
Kaina na sunkuye a kasa nakai hannuna na share hawayen da suke zubo min don tsananin rudanin da na tsunci kaina a lokacin ciki.
Na ringa addua ya Allah ka kubutar dani daga sherin wanan mutumin da bansan abinda ke cikin zuciyar shi ba a game dani.
Ido kawai ya zura min yana kallon yadda nake faman sharan hawaye daga idanuwana a lokacin tabbas na bashi tausayi don nayi kankanta da abinda ke faruwa dani a yanzu.
To yaya zaiyi hakan ne kawai mafita a gareshi da irin fitinan da mami ke shirin kunnu mai a rayuwan shi na yarda ya auri yar kawanta ko daga cikin yan uwan shi kamar yadda baffansa ya fada harda diban mai wa,adi akan hakan.
Ya haka kuma ka zauna ka saka min ita a gaba tana sharan hawaye haka wani abin kuma ka sake mata na samu hankalinta ya fara kwanci a gidan nan yanzu .
Hjy ce data fito daga bandaki tana tsaye tana muna kallon mamaki take fadin hakan cikin kure shi da idanuwanta fuska daure.
Ya juyo gareta tare da wani irin sauke ajiyan zuciya yana dan gugan gaban goshin shi zuwa wuyan shi a cikin wani irin yanayi.
Hjy na gane yarinyar nan tsoron mami takeyi kamar ranta ba zata bani goyon baya yadda nakeso da ita ba.
Yadda yake magana ba kunya ta bude baki da ido tana masa wani irin kallon mamaki don hakan har hjyn ma saida taji tsoron shi a lokacin.
Kubi yarinyar nan a sannu kaida uwarta wanan rigiman jafari yafi karfin daukar zuciyar yar nan a yanzu.
Cikin takaici yace hjy kin san dai bana magana biyu na fadawa mami ban yarda da zabinta ba kuma zan taba yarda da hakan ba ta barni in zabi zabina shine kwanciyar hankalin mu gidan nan.
Ta kaici ya kama hjy take fadin dan nan wai kana a cikin hankalin ka kuwa wanan zancen da kake fada haka koda yaushe.
Shi kadai yasan halinda yakw ciki don haka ba tare da ya iya ba hjy amsa ba ya mike daga inda yake zaune cikin wani yanayi ya bar dakin namu cikin kunar rai.
Haka ya fito a dakin yana maijin zuciyar shi na masa wani kuna da suya don rikicin da suka kwasa da mami a office din ta a kaina kafin ya dawo gidan ya sameni da zancen.
Har dare banji hjy tayi min zancen ba ni kuma ban iya sake jikina da itaba har lokacin sai yawo muryan ya jafar kemin a kunnuwana kamar yanzu yake fada min maganganun daya fada dazun.
Sam ban san suna falo ana rikicin abu daya ba a gidan don dai shi ya dage akan zai tafi don aiyuka sun taso masa a lokacin mami kuma tace bata yarda ya koma batare da aure ba.
Shi kuma yace ta yarda da zabinshi don shi abinda ya zaba ke nan mami tace bata yarda ba ta fada mai a fusace.
Yadda na fadama ko yanzu zan sake maimaita ma hakan don ba zan taba yin magana biyu ba mun shirya zancen auren ka da Iyayyen Suraiya kafin ka koma za ayi bukin ka da ita ku koma tare.
Ta kare fadin hakan rai bace idanuwan ta sun kada sunyi jawur don masifa da takaicin sa da taji a lokacin.
Ya dago idanun shi da suka canza kala alaman idan ya fadi magana baya canzawa yace mami na fada maki yarinyar nan ce zabina.
Ni abinda nake nufi da yarinyar nan ba zaki taba ganesa ba a yanzu da na auri wanan din da kike nufi na aura mami gwara na zauna a hakan banyi aure ba.
Ni da farko nayi hakan be don sama mata jin dadi da walwala na dauka don ke nayi hakan mami a matsayinta na wace bata da gata a yanzun.
Koma meye manufan ka akan yarinyar nan nace ban yarda da hakan ba, idan zaka yiwa kankane kuma sai mu gani a yanzu.
Ya mike tsaye yana fadin shikenan mami zan zauna hakan tunda haka kika zaba min amma ni nasan akwai ranan da zakiso hakan ace ya faru da kinsan abinda nake nufi da hakan.
Ya mamud dake zaune yana sauraren su yace mami ki kyaleshi yayi abinda zaifi kwanta mai arai da wanan yawan gardaman da akeyi kan wanan zancen.
Rufa min baki idan ba zaka tayani yakarsa ba ya amincewa abinda nakeso don kawai wani ra,ayinsa can na banza da baida dalili.
Shima ya mike yana fadin kiyi hakkuri mami Allah ya zaba muna abinda yafi zama alheri a gareshi yai mata saida safe ya fita.
Wanan zancen da sukayi ne a gaban hjy dake zaune tare dasu bata tofa uffan ba ta kafa hujja ga hakan..
Bayan kwana biyu da zancen ne ya shigo dakin bana ciki a lokacin yake tambayan Hjy a cikin dan zolaya ina matana ?
Hjy ta dago ta kalleshi tare da fadin ubana ai ba wanan zancen tsakanin ka da yarinyar nan har abada.
Ka tsaya tsakanin ka na dan uwa mai tausayawa a gareta ko a hakan idan kayi niya zaka iya tausaya mata ka taimaka mata babu mai hanaka wanan a gareta.
Zuciyar shine ta harba da zancen hjyn take yaji wani irin kunci ya ziyarci zuciyar shi lokaci guda.
Kasa daurewa yayi take idanuwan shi suka kada sukai ja lokaci guda bai iya magana ba ya mike tsaye dan barin dakin.
Hjy ta dakatar dashi tana fadin kaga kada ka dauki wanan abin da zafi kaje kayi addua shine mafita ga mumini aduk sanda ya tsunci kanshi a cikin damuwa.
Har yakai kofa yaji tana fadin ina son ka rabu da uwarka lafiyane jafari don yadda ta hau wanan zancen a karkace bata jin kira ga kowa a yanzu.
Don dai yarinyar nan bata da wani gata a yanzu ka sani sai uwarka data daukota ta kawota gidan ta.
Ya juyo yana fadin mami ta yanke min hukunci mai tsauri wanan karon kuma hjy ba zan iya jure hakan ba a kaina.
Ka barta da yarta don Allah kaje ka auri wace take so din ita wanan din tunda kayi niyar taimaka mata sai ka zama mata gata nan gaba a rayuwan ta.
Amma idan kaki jin maganan mahaifiyar ka sai ka kara jefa yar nan a wani hali nan gaba wa kake tunanen zai zame mata bango bayan ku da uwarku din a duniyan nan.
Anan kuma ya kara dago kai ya sake kallon hjy din kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru ya juya ya fara tafiya yana fadi a cikin wani murya mai kariyan zuciya yana fadin sai da safe hjy daga hakan ya fice dakin rai bace.
Da safe ne hjy take min zancen mai kama da warning a gareni tana fadin duk da nasan baki dauki wanan zancen ba tun farko a ranki.
Hakan yai min dadi a yanzu yadda baki saka son yaron nan a zuciyar ki ba kamar yadda shi yasakaki din nan.
Don haka kici gaba da nisantan duk wani da na iyami da komai nata a rayuwa ku samu a rabu lafiya.
Saboda bana son ki sake shiga rayuwan kowa daya shafi a halin nan na iyami kiyi addu,a Allah ya kawo miji daidai ke a rayuwan ki.
Idona ya ciciko da hawaye tabbas nasan iya gaskiya hjy ta fada min don tsakani da Allah tsohuwar nan take zaune tare dani.
Na dinga share hawaye da bayan hannuna hjy tayi tankar bata ga me nake ba a lokacin tana maijin tausayina a kasan zuciyar ta.
Hakan yasa dakin yayi shiru na dan lokaci kamar babu kowa a cikin sa lokacin dagani har ita kowa da nazarin da yake a zuciyar shi.
Tabbas nasan nikan gaskiya hjy ta fada mami da ahalinta a yanzu sune gatana don a karkashinsu nake zaune idan wani abu nema ya same dolen dai sune zasuyi min tsaye akan hakan.
Sosai hjy take kara jana a jikin ta hira zamu zauna muyi sosai zata tsaya ta zauna tana ban labari ko shawara.
Na hanyoyin da zanbi na manta da komai har na taimaki rayuwana a cikin kwana biyune na sake sosai kamar baniba don har dan jikina ya fara dawomin a lokacin.
Hakama mami duk da daure fuskanta gareni bai hana in samu kulawan da nake samu ba da farko a gidan nan.
Iyaka dai zance nafi samun matsala gun mami da anty Aisha sai nuriya matar ya mamud ko shi din sai idan wani abu ya dan hadamu da su.
Sai dai su samari mami din jalal da jamal babu wani sauyin fuska da suka canza min don har yanzu mutuncin dake tsakanin mu yana nan a yadda yake.
Hankalin kowa a kwance don kowa ya fita wanan zancen shirmen da ya jafar ya tsiro min dashi tunda suna ganin ya fita zancen a yadda sukayi da mami a karshe.
Sai gashi ranan ya shigo gidan ina daki kwance ya shigo dakin namu wurin hjy don dai kakarsu tana dakin ne duk wani na gidan yakan shiga dakin namu don gaida hjyn .
Ina ganin shi na rikice ina kokarin barin dakin bayan mun gaisa dashi na mike da sauri zan bar dakin don har lokacin tsoron shi nakeji.
Yake fadin karki fita dakin nan don ni ba dodo bane ya fada cikin daure fuska.
Na juyo da sauri ina fadin kayi hakkuri ba don ka zan fita ba sai muryan hjy ke fadin ka daina kula yarinyar nan.
Don kwanciyar hankalin kowa a gidan kaga kwanakin nan komai ya gama lafawa a tsakanin ku da mahaifiyar ku.
Kwatsam sai ga mami ta bude dakin ta fado tana fadin me kake a nan ke kuma fice daga nan ki ban wuri.
Juyawa tayi ta fara fadin hjy kina zaune zai shigo ya kebe da yarinyar nan bana son wani abu ya sake faruwa a tsakanin su kuma




ZAINAB IDRIS MAKAWA




🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅


3️⃣6️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA




BARKA DA JUMMA,A YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMIN, , , ,




Bayan kwana biyu da faruwan hakan da har hjy da kanta tayi mai iyaka dani a gidan don samun kwanciyar hankalin kowa a cikin maganan.
Sai ya zamanto banda wani lakka a tare dani ni dai har ga Allah nasan bawai son yaya jafar nakeyi ba a raina.
Saidai na rasa me yasa na damu da yadda hjy din tayi a lokacin hakan ne ke wayan sakani a cikin damuwa har yakai na fara rama a jikina wanda ban taba irin saba tun zuwana gidan.
Da darene ni kadai a dakin ina kwance ashe hawayen ke zuba min a idanuwana ba tare da nasan hakan ba.
Ba komai nake tunawa ba a raina sai yadda iyayyena sukai watsi dani haka kan abin duniya har hakan ke faruwa dani ba tare da kowa nawa ya san da hakan ba.
Irin wanan tunanen da nakeyi yanzu ne ya karkare ramar dani hakan duk nabi na susuce har sai mutum ya dauka akan zancen mu da ya jafar ne nake wanan ramar haka.
Hjy da dawowan ta ke nan daga falo taja tayi turus tana kallona a cikon mamaki da al,ajabi yadda ta sameni din a dakin.
Jikin ta yayi sanyi lokaci guda tana fadin au kuka ke rusa haka yar nan ke kadai a dakin nan .
Da sauri na gyara ina kokarin goge hawayen dake fuskana a lokacin shiga tayi bandakin ba tare da ta tsaya sauraron abinda zan fada ba a lokacin.
Ta fito ta tayar da sallah da nake ganin shafa,i da wutirine zatayi har lokacin ina kwamce a yadda nake nade cikin kujera ban motsa ba.
Muryan ta naji kamar daga sama tana fadin ni yar nan meye abin kuka yanzu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login