Showing 66001 words to 69000 words out of 191310 words

Chapter 23 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

Oh mami rely iam sorry for what i have done wanan tsohuwar ne ta dameni kuma nasan ba bari zakiyi in dawo ba idan na fada maki kai tsaye zanzo inyi wani abu a nan a ranan nima tafiyan ai da niyar in komane idan na gama sai gashi ban samu komawa ba.
O hjy ce ma ta dameka har kana fadi a gabana forgive me mami iam sorry wlh wani abu nazo yi garin nan na lake a cikin sa.
Alhalin tunda yazo yana gida bai fita ba yana daki yana ragewa kanshi zafi abindake tsunkularshi kwana da kwanaki.
Is your on business koma meya baro ka da garin mu dai ai ba zaka hanamu yin kwanakin da mukai niyar yi ba a can.
Ya dan laso bakinshi yana shafan kai don ya fahinci mami ta hau sosai dashi kan abinda yayi din na barin su can ya dawo nan shi kadai.
Ke wai lafiya kin tsawa mutane saman kai haka kina bin mutane da kallo don rainin wayau Rufaida ke fadi a hasale.
Keko gulma mana tana bin bakin kowa da kallon abinda ake fada kamar ba yar aiki ba ta dinga shiga cikin mutane tana kutsa kanta.
Ikon Allah da alama yar nan dai bata jin dadi a wurin ku meye matsalanta don ta tsaya a cikin mu ita din ba mutum bace kamar ku ai dan mutum daraja gare shi tsohuwar ke fada tana kallo.
Zo ki zauna a nan gaki tsaye kinyo tafiya baki zauna ba take fada tare da kallona tana nuna mi wurin zama.
Nace dama ledan nan ne ban san dakin da zan kai maki ba shine na tsaya na fada a dan marairaice.
To kuma ji da abinda ya tsayar da ita a gurin ba tsayin banza tayi ba ta mika hannu in miko mata ledan dake hannuna.
Mami tace na rasa me yarinyar nan ta tare masu a gidan nan da basu bata salama sai hattara da tsana.
A,a in kinga hakan wata kila dai sun hango wani abune a gareta sukewa kyashin sa ko don yanzu ta karbe masu fada gurin ki.
Su dai daina haka don ban so banyi sharawa da kowa ba da zan kawo ta gidan nan do haka ba zan dauki hakan ba gareta tunda ban bari uta ta raina ku ba.
Gaban mami bazo na tsuguna ina fadin mami bani key in bude daki zan gyara ne kafin ki shigo.
Ga dai key din gyara ki bari sai anjima yanzu dai ki kwashe kayan mu kikai min daki hjy kuma nata dakin ki kai mata sai ki koma dakin Aisha da zama ke .
A, a barmu mu zauna dakin ta a tare dama kawatace ki n ga ai ko tausa tayi min a dakin idan ina so naji kuma dumin mutum a kusa dani ai?
Ko ba zaki zauna tare dani ba kawata tana tambayana cikin dan dariya tana kallon fuskana.
Murmushi na sake wanda yasa fararen hakora dan baiya diple dina ya dan lutsa daga gefen fuskana ina fadin ina so sosai hjy .
Ya daifi ni dama ba zan zauna da kowa a dakina ba Aisha ta fada tana mikewa tsaye mami tace hakan baidai taso bane .
A nan na barsu ashe baya barina wurin Rufaida tayi fushi ta mike ta koma daki su waya ta jawo tana fadawa uwarta wai mami tana disgata kan yar aiki ita gida zata dawo don hakan da ake mata yana ci mata rai.
Duk da mami tace kada na gyara dakin ba yarda na barshi hakan ba don sai dana kara gyarashi tas na dawo dakina na gyarawa hjy yadda ya dace na dauko wani zanin gado dakin mami mai kyau na shimfida mata.
Falon na dawo inda na samu sun fara cin abinci har lokacin mami na zaune tare da yaran ta gaba dayan su a wurin sai salma da hjy ma kakarta ce don itace ta haifi uwarta a gurin tana nuna jin dadin ganinta.
Yau zee kici abinci ki dauko zanin gado a daki ki shimfidawa hjycdakin ki .
Nace na dauko na shimfida mami tun dazun ai tace kai zee na gode sa wanan karama hjy din da kike yi yamafi min ku zauna tare da zamanta da wanan mara moriya din tana nuna Aishan ta.
Mami nice banda moriya bari ki gani har wanka zan dingawa hjy har ta bar gidan nan kuwa hannu mami ta watsowa Aisha tana fadin karbi naki nan ko uwarki Ramatu tayi kadan tayiwa hjy wanka yanzu ai.
Abinci na diba na koma can gefe guda ina dan duban inda zan zauna mami ke fadin wanan abinci zai ishe ki ke nan zeey ?
Ya isa mami na fada ina nufar can nisa dasu don in zauna tsohuwar take fadin wanan ya da dadin zama take wallahi.
Wanan ba irin yarwa bace a cikin ahali yarinyar ta samu tarbiya a gun uwarta kada ki bar wa yan nan marasa ta ido su kore maki ita gidan nan.
Ai ba zan barsu ba mami ta fada duk wanda bai iya zama da abindanake so yayi gaba hanya a bude yake mai ai.
Baidai kai can ba kowa ya tsaya a matsayin sa tsohuwar ta fada mami ta nuna salma tana fadin sune ai marasa hankalin yarinya ta girmamasu sai sun zubar da mutuncin su gareta zasuji dadi.
No mami ba salma a ciki zancen nan don da kanta zeey ke fada min tana jin dadin zama da anty salma sosai idan muna hira da ita.
Salma tace mami ni ina ruwana da harkanta gidan nan tunda bata tare min komai ba ga kowa.
Shine daidai hakan ai kinji itama tana yabon ki a bayan ki gashi yanzu yar uwan ki tana fadi kuwa kafin ta juya wurin yaya jafar tana fadin.
Kai gwauro ba zakaci abincin bane kai ko sai yayi sanyi ka tsikara ka tashi tunda baka aje ba balle a dumama shi.
Zaki fara tsokanarshi ko hjy yaya mamud ya fada yana mikewa sai tsohuwar tace gashi ko yanzu ya iya yaji saboda korafina ba kuma zan fasa ba idan baiyi abinda nake son yayi ba.
Ya dago kai yana fadin me kike ci na baka na zuba hjy kwana zan fitar da mata kowa ya huta ina shike nan.
Shike nan kuwa kaga an wuce wurin haba ko kai fa mutum kamar me jin warin mata a tare dashi.
Barshi hjy rainawa mutane yake son yi wanan karin ko ba zan saurara mashi ba don naga wasa ya dauki zancen nan.
Mami ai na fada maki kwanan zan fitar kowama ya huta sai mami take fadin yar gidan wanene yarinyar da zaka fitar din ?
Mami ai ko yar waye zaki gani idan Allah ya kaimu ranan dinan ki sai naba kowa mamaki a gidan nan sosai.
Mami ai kin san sai yar gwauna ko wani seneter don irin su yaya Jackson sai diyan manya a kasan nan ai Aisha ta fada tana kallon shi tana dariya.
Shima murmushi yayiwa zancen Aisha din yace kedai bari zan yi surprise din kowa idan na tashi sai hjy tace kada dai kaiwa mutane zaben tumun dare garin ruwa idon kan nan.
Ni makoho ne aka fada maki ai kece mai bani shawara ki bari ki gani idan ban zabo da kyau ba sai ki fadi hakan.
Wayan shi da yai kara ya dauka yana duba kafin ya mike ya bar wurin yana wani magana kamar yare sai hjy ke fadin.
Itace ta kiraka kake gudu kar muji me kuke fada dama ka zauna da wanan yaren naku baji muke ba mu.
Daga inda nake ina dan murmushi wani tunane yazo min nake fadin a raina zanso nima inga wanan zabin na yaya jafar yadda yarinyar zata kasance.
Nasan badai kyau da kudi ba kan kamar yadda yake da kyau din nan ga ilimi ga wayewa dole wace zai aura din itama ta kasance kamar ai.
Ni daya ke faman tunane har naji abincin ma ya fita a raina ina tuna sukan sunji dadin su uwa kudi uba kudi haka.
Suma gasu kudi wai ina mutanen nan zasu da wanan dukiya hakane idan da nice su ai ba zan nemi wani kudi ba zan zauna in hutane kwai inta jin dadi na a gida.
Zeey zoki kwashe wanan kayan abincin nan wurin nan ki dawo ki kai hjy daki tayi sallah ta dan huta.
Firgigit na dago kai tare da fadin to mami ina kokarin mikewa a inda nake zaune din.
Sai dana gyara komai mami na zaune gurin tana waya da yayan ta da muka baro dazun garin su.
Hjy muje in kaiki dakin azahar yayi tun dazun na fada a cikin ladabi ina kokarin daukan kayan ta gyale da ledan maganin ta dake gefenta aje.
To yar nan har na fara gyangyadi ko a wurin ba tare dana sani ba tana mikewa tare da kokatin tattaro gyalen ta dake gefe.
A hankali muke tafiya zuwa dakin har muka kai dakin yayi dan dumi sai kamshi ke tashi a cikin sa ledan na aje a gefen gadon kafin in nufi kofan ban dakin in bude mata shi.
A, a kagani ba nan yayi min gara in zauna dake da in zauna da wanan mara moriyar Aisha wace ko kara ba zata iya kawar wa kanta ba balle wani.
Bayan mun idar da sallah dukkan mu a nan kasan muka kwanta nabawa hjy filo tayi matashin kai dashi niko ko filon ban samu matashi dashi ba sai barci.
Ban falka ba sai da hjy ta tashini don inyi sallah la,asar nasan yamma yayi saboda dadin barcin da nayi.
Na idar na mike zuwa dakin mami bata dakin yasa na samu daman kara gyara dakin da yake ba wani datti a ciki dakin
A falo mamice da yaya mamud suke magana haka yasa na juyo zan koma dakin mu indan gyara don ko ba komai da zan wa dakin ban dakin yana bukatan wanki koda yaushe.
Na wanke na fito ina daukan filon data kwanta a kasa take fadin yar nan idan kin rage sai ki kaini falo in zauna don yamma tayi yanzu.
Na amsa da to hjy muje mami ma tana falon zaune tare da yaya mamud .
Wai ni iyalin shi mamud din suna inane don banji duriyan su ba tun dazun ina a nan gidan suke zaune ne suma.
Suna Abuja an barsu a can da zamu dawo kaduna yar ta kifen tana nan dai da halin ta har yanzu bata canza zani ba ko ?
Dan dariya mai sauti nayi ba tare da nayi magana ba don ban san abinda zance da ita ba.
Falin muka fito tafiyan minti daya daga dakin mu zuwa falin saida muka biyar muna lalabawa kafin mukai saman kujeran ta zauna a hankali.
Mami na fadin kun lalabo kun fitone hjy take fadin yar nannta lalabo dani ina dan jin dadin hakan yarnan akwai kirki sosai.
Allah yasa kiga aurenta hjy amin ta juya tana fadin kada ki tsaya dogon bokon nan na zamanun nan dake batawa mutum lokaci sai a dauki lokaci yaro na zubar da irin sa duk wata.
Yaran nan da kun gane ai da ku aurar da su don har sun wuce munzali aure a yanzu .
Hjy kin san ai aure dan lokaci idan lokacin sa yayi koda shiri ko ba shiri sai ayishi a lokacin.

Zaune yake saman farar kujeran roba a gurden din gidan mai dauke da dogayen itatuwan da ba wani zugun ganye suke dashi ba sai dai tarin tsayi a gasu.
Babu wani abinda yakeyi duk da sytem din shi dake gaban shi a bude ya kasa aiwatar da komai sai faman tune a ranshi.
Yakai hannu a hankali ya rufe sytem din ya dafe kan shi dashi yana ci gaba da tunanen shi ya rasa yaya zaiyi ne da wanan hukuncin da yake kokarin yakewa a ranshi.
Allah ya gani bawai yana son yarinyar da mami ke son hadasu bane zai dai amincene don farin cikin mahaifiyar shi kawai.
Don yadda mami dasu hjy suke nuna mai muhinmancin yin hakan gareshi saidai shi Allah ya gani bawai ya shiryawa aure a wanan shekarun nasa bane.
Anya kuwa idan yayi gangancin yin aure a yanzu ba zai jawa kanshi matsala bane ga hakan.
Kai ya girgiza shi kadai tare da fadin dole yai juriya da fin karfin zuciyar shi don ya samu su rabu lafiya da mahaifiyar su.
Muryan Rufaida dake fadin ki tabbatar da kin wanke kayan nan tas wallahi kada inga jirwaye a jikin su banza kawai mun zuba ke nan dake a gidan nan.
Ke gaki kin samu wuri zaki mike kafan ki kiji dadi ko to wanki har na tufafina duk ke zaki dinga wankin su a gidan nan daga wanan ranan.
Nima ga nawa Nazira ta fada shegiya munafuka mumuke zamuyi maki a gidan nan ba tare da mami ta san da hakan ba ta jefo min unders din ta a fuska.
A daidai lokacin daya karaso wurin don jin zagin da suke min din yayi yawa a lokacin.
Yana tsaye hannun shi duka biyu zube cikin aljihun wandon shi kallon kayan yayi yayi saurin kawar da idon shi ga kayan.
Ya dago yana kallona su kuma sai dan kame kame sukeyi suna fadin sannu da hutawa yaya J ke daga daga nan ki shige ciki ya fada yana kallona.
Da sauri na bar wiein kayan na koma ciki dama wurin su mama kande nake zaune suka sameni suka ban wanan sikin wankin.
Nan nabar masu kayan nasu na shige ina share hawaye babu mami a falin sai hjy dake zaune ita kadai ta kurawa tv ido tana sauraren malam daurawa dake wa,azi a tashan sunna tv.
Na zauna take fadin yar nan akwai kura kuren da mukasha tabkawa a rayuwa sosai a baya wanda sai yanzu kake jin bayanai akan abubuwan da bamu sani ba a can baya.
Jin tana magana ban bata amsa ba yasata dago kai tana fadin kinga kamar da can baya ai bamu sancewa ga lokacin da mutum ya dace yayi , , , ,
Ido ta kura mi don hawayen data ga ina sharewa a lokacin salati ta saka hankali tashe tana fadin .
Waya tabaki me akai maki yar nan ki fada min wanda ya musguna maki yanzu don nasan ranki aka bata haka.
Muryan mami ne ke fadin hjy lafiya wa aka batawa rai zeey lafiya me ya faru yanzun fa kika bar falin nan da raha da hjy .
Mami ba komai ba komai kamat yaya ta fada tana kallona tana zama saman kujera takon kafab shine yana shigowa daga kofan baya yake fadin.
Mami kiwa yaran nan iyaka da yarinyar nan abin is too much sun mayar da ita boya a gidan nan .
Mami idan baki iya masu magana su daina don Allah ki mayar da yarinyar nan gaban iyayyenta haka cin fuskan yayi yawa.
Ya kwashe komai da yaji yana fadawa mami rai bace yana gama fadi ya juya ya fita hjy ma tana masa magana bai tsaya sauraren ta ba ya fita don bai cikin dasin rai a lokacin.




ZAINAB IDRIS MAKAWA








🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅




2️⃣1️⃣




ZAINAB IDRIS
MAKAWA




YAR UWA FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA TARE DA IMANI A ZUKATAN MU AMIN DON ALLAH KADA KI FITAR KARKI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA KI TUNA DA AKWAI RANAN HISSABI YANA NAN TAFE.


Ki biya ki karanta a cikin salama yar uwa kan dari uku kada a tsayar dake ranan da kowa tashi ke fitar dashi sai abinda ka shuka.
Yau tun safe Lantana da haibaici ta tashi a gidan don kawai Abban mu ya kwana a dakin innar mu kuma taga Abba ya fito ban daki da asuban farko.
Saboda ta hana idon ta barci duk ranan da Abba ya shiga wurin innan mu haka take kwana leken tagar dakin ta don ganin halin da suke ciki.
Wanan dalili ke sa Abba ko zai shiga dakin sai yaji wa,azi da nasiha abokan shi ko wani na kusa dashi akan yadda yake wofintar da innan mu har yan waje suka gane hakan.
Hakan ba abin mamaki bane sanin ko wacece uwar lantana a garin dan zaman kanta takeyi tana sana,ar tuwo tuwo.
Haka kuma take mu,amula da maza bata boye halinta har mutanen gari suka ki auren yarta data taso shine Asabe kakar mu taje ta kwasowa Abban mu ita.
Don kswai a lokacin suna dan dasawa da mahaifiyar ta har suka hada wanan alakan cewa idan Abban mu yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login