Showing 123001 words to 126000 words out of 191310 words
Chapter 42 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
?
Idan don maganan dayiwa yaron nan ne kiyi hakkuri wallahi ba nayi haka bane don in raba tsakanin ku.
Nayi hakan don kawai a samu kwanciyan hankali ga wanan zancen dayaki ci yaki cinyewa tsakanin shi da mahaifiyar shi.
Da kyat na iya motsa bakina na furta hjy ba wanan zancen ne damuwa na ba iyayyena da suka fita zancena a nan sune damuwana a yanzu.
A, a yar nan don wanan ai ba zai sa ki rame har ki lalace haka ba lokaci guda wallahi anyi farko anyi karshe insha Allahu ba zan kara maganan nan ba a gidan nan irin haka a kanku shima din na kula da fushi yake dani a kwanakin nan.
Aisha ce ta shigo dakin ta samemu muna wanan maganan duk da shigowan ta baisa hjy ta daina fadin abinda take fadi ba a lokacin.
A daidai lokacin da hjy ke fadin Allah ya baku hakkuri kuskure nayi na aikata hakan .
Aisha data fahinci maganan tsohuwar inda ya dosa Aisha taja wani irin tsuki tana fadin wanan zancen har yanzu nina rasa me yasa ya J ya nace akan wanan zeey din haka wallahi mami tace bata son zancen nan amma shi duk yabi yana kokarin dagawa mutane hankali akai.
Da sauri naji hjy tace a, a yar nan kada in kara jin kin fadi irin haka so ba a yi mashi irin haka abune shi mai cin zuciya rabu da namiji kan abinda yake so.
Idan an mashi hakan ba,a kyauta mashi ba don yaron nan bai taba nuna yana son wata ba haka kamar yadda ya nuna a yanzu.
Daga shi har yar nan ai yanzu an zama daya dan yar nan yanzu tankar iyami ce ai ta haifi abinta bata da maraba da wace ta haifa a cikin ta tunda iyayyenta sun bata amanan rikonta a hannun ta.
Da sauri Aisha ta dago tana fadin ba zasu taba zama daya ba kan da yaya jafar hjy ta yaya ma za a hadusu wai ?
Wani kallo hjy ta watsa mata lokaci guda kafin tace ni ba ruwa da zancen nan yanzu daga fadin gaskiya ya J ya tashi makeni gidan nan.
Dole ya makeki don kalamin ki baida dadi yar nan don yarinyar nan tana da hakkuri da mutuncine ko wanan maganan da kike fada yanzu haka ke kinga ya dace da ki fadi hakan a gabanta.
Tsam ta mike ba tare datayi wani magana ba ta fice daga dakin hjy ta bita da harara tana fadin sakariya mara wayau idan Allah yayi saiku hana mugani.
Indai biyayya gun nagaba nada dadi mu zuba gani nida uwarku data raina zancena a yanzu tunda ban isa in fada mata daidai ba a gidanta yanzu tana ganin ita ta ishi kanta ke nan yanzu.
Ta juya inda nake bayan fitan Aisha dakin tana fadin ke kuma ki barsu da dansu wa yan nan zuciyar su ya kyankyashe da wullakanta dan Adam.
Amma saboda shi har zaki wani shige daki kina hawaye haka don baki danayi yanzu sai tunanen shi.
Ki matsa ki yada kanki wurin wa yan nan mutanen da suke raina arzikin tallaka a rayuwan su.
Take jikina ya kara sanyi nace nifa hjy na fada maki ba wanan zancen kika samu inawa kuka ba dazun.
Don waye kike kuka idan bashi bane din idan fadan danayi ne bazan kara shiga harkunku ba a gidan nan.
A sanyaye na marairaice ina fadin kiyi hakkuri hjy insha Allahu ba zan kara ba tace shike nan ai.
Nidai shawaran da zan baki shine wallahi ki natsu ki bar saka wanan zancen a ranki ki kara kama kanki da wanan zancen.
Kinga tunda aka fara haka ko da Allah yayi kunyi wanan auren bazaku samu jittuwa da sarakuwar ki ba a hakan tunda har ta iya rufe idanun ta ta nuna hakan yanzu.
Don hakane yasa nace mai ya fita wanan zancen don abindana hango maku din keda shi nan gaba.
Amma badon bana son ku a tare ba ko wani abu can kawai dai abin ne da uwar taku keyi akwai cin fuska a cikin sa yanzu.
Abi komai a sannu sannu iyayye ku su amince da wanan zancen don ina gudin abinda kaje ya dawo daga baya.
Hjy kiyi hakkuri wallahi ba a kansa nake kuka ba nan na labarta mata abinda nake yawan tunane game da iyayyena a raina.
Saida hjy ta gama saurarena kaf take fadin koma dai meye ba zasu taba mantawa dake ba a rayuwan su mussanman ma mahaifiyar ki dole tana can a cikin rashin ki tare dasu a yanzu.
Haka ta kalleni a cikin tausayi tana fadin ki saki jikin ki ki kara kwantar da hankalinki ki nunawa iyami danta ke baya gaban ki a yanzu.
Nace hjy ni komai ya wuce a wurina tun farko ban taba nasa wani alaka a tsakanin mu ba bayan na yan uwantaka.
Can cikin dare ina barci nake jin wayana na varvirating a saitin kunnena duk da nasan babu mai kirana sai shi yanzun kuma ya daina kirana din tunkan ai wanan tsakanin su da hjy.
Har kiran ya kare ban dagaba sai ma kokarin danne wayan da nake gudun kada hjy taji kiran.
Kira uku na daga a dan rikice don nasan ba zai daina kira ba idan ba na daga wayan ba a lokacin.
Murya kasa kasa na amsa da sallama don kada hjy ta jini jin muryan shi take na rikice gaba daya na rasa a wani duniyan nake.
Wani irin tsoro da fargaban jin muryan shi suka ziyarci zuciyana wanda nake ganin kamar amsa wayan babban laifine nake aikatawa a lokacin.
Wani irin ajiyan zuciya naji ya saka yayin da yake ji a bangareshi kamar susa nake mai a kwakwalwan shi don rikicewa.
Ran sarauniyarta ya dade kin wuni lafiya ya rigiman hjy da tsufan ta ban san lokacin da dan murmushi ya subbuce min ba a lokacin.
Yace nasan kina nan kina fama da rudu irun nata a kullun sai kara firgita min ke da takeyi.
Aiko hjy ta wuce hakan a wurinta don da tana da iko da kai da ta faranta maka rai fiye da kowa a duniyan nan.
Na sani amma yanzu itama din sun fara in mata ai nake gani kan hakan .
Da sauri nace yaya ka daina irin zancen nan don maganan hjy shine gaskiya a garemu don Allah yaya ka barni da wanan zancen.
Ka tuna ni kamar marainiya nake a cikin ku kune gatana a yanzu na rokeka idan kai sanadin dana bata da mami zan shi, , , ,
Amma so ance hana ganin laifi ko nayi shiru yace don haka kada kiga laifina a wanan bangaren .
A raina nace tabbas akwai sauran rikici a tsakanin mu gidan nan yanzu don a gaskiya ba zan taba yarda da hakan ba a gareni don mami dai ba zata taba yarda da hakan ba a tsakanin mu tunda ni banda gata a wurinta.
Yace ina son inji kin shirya zaki zauna dani komai ritsi komai wahala ni kuma nayi maki alkwarin inganta rayuwan ki dana yan uwan ki da iyayyen ki tun daga ranan da bakin ki ya bude da kin yarda dani ko ba tare da yardan mami din ba.
Wanan maganan yafi karfin fahintana ka rufamin asiri a rayuwana koda zan soka yaya badan kudin ka ko wani abu zan soka ba zan soka ne tsakani da Allah kamar yadda nima kuka rikeni a cikin ku amana.
Koda kuwa yin hakan yana da wani illa a gareni nan gaba zan daure in ga nayi abinda zan sakawa mami a rayuwana.
To idan kuma mamin naki bata yarda ba kan wani dalili nata na daban zaki iya jure wanan daman da kika samu daga taimakon iyayyen ki da yan uwan ki ya tafi ga wata.
Nace idan yin hakan zai kawo fahinta a tsakanin mu da mami a shirye nake da mata biyayya ko wani lokaci.
Amma dai kin yarda har a zuciyar ki niba mai cutar dake bane zainab ya fada a cikin wani yanayi mai ban tausayi.
Yaci gaba da fadin ki yarda dani kanwata ke kadai zuciyana ta amince dake zainab kece zuciyana take hasko min a yuwana kece rufin asirina kada ki yarda ki barni zainab komai ritsin mami a garemu na maki alkawarin rikeki a mana a rayuwana koda kuwa duk duniya zasu juya maki baya akaina.
Nayi maki alkawarin rikeki amana har karshen rayuwan mu nidai muradina shine ki amince min zainab yardan ki kawai nake bukata a yanzu.
Nayi maki alkawarin rikeki amana harga Allah zainab ba zaki taba dana sani a kaina ba matukar kika yarda da amsa min da eh yaya na amin ce.
Ki taimakeni ki taimaki rayuwana kada mami ta zantar da hukuncin da zata dawo tana nadama a kaina daga baya akanshi.
Yadda yake magana a cikin wani irin yanayi kamar roko a gareni yasa tausayin shi ya rufe min zuciya ban san lokacin dana bude baki don dakatar dashi nace.
Na yarda yaya indai hakan shine rufin asirin ka da mami dama yan uwan ka na yarda da wanan koda kuwa hakan zai zama kadara rayuwana mutukar hakan zai zama rufin asirin ku a duniyan nan.
Yace Alhamdullahi zainab na gode tunda kika fahince kamar yadda hjy ta fahinceni ga hakan yanzu kema din kin fahinceni.
Zainab kece rufin asirina ke kadai ce wace na yarda da ita a rayuwana da zaki iya zama dani a irin yanayi na ko yaushe ba zabin mami da take soyi a kaina ba yanzu.
Fatana inje ga iyayyen ki yanzu su amince dani kamar yadda kema kika fahinceni kika yarda dani .
Na samu duk wani fari ciki da nike so a fanin rayuwan duniya ke kadai kika rage min a yanzu in mallaka .
Idan har mun daidaita a tsakanin mu muka shirya zama da fahintar rayuwan mu to tabbas bani da matsala a duniyan nan fatana yanzu mu samu kiyamar mu.
Idona na lumshe don jin abinda ya fada ina kiyasta maganganun daya fada min a zuciyana saidai na kasa fassara abinda maganan nasa ke nufi a fili.
Katseni yayi da yake fadin to yanzu sai ki shirya tsana da tsangwaman mami a gareki don kinsan itace matsalan mu.
Saidai hakan na dan lokacine ba mai dorewa bane idan mun bar kasan nan munyi nisa da ita komai a sannu zaizo ya lafa.
Mun jima a hakan shike zuba min hiran da ba amsa tun ina amsa mai da eh ko a, a har ya fahinci barci ya kwasheni a lokacin ya sararawa ranshi.
Washe gari koda muka tashi hjy bata nuna min komai ba har na shirya na tafi school sai bayan mun dawone da yamma muna zaune.
Naji hjy ta jefo min tambayan da ya girgizani lokaci gudan don ban zaci taji me muke tataunawa a tsakanin mu a daren jiya din.
Ina fatan kin fara shiri kan abinda koka tarawa kanki kika yarda da hakan da bakin ki ba wani ya fada min ba na jiki naji zancen ku kaf a kunnena duk yadda kukayi dashi.
Kai na sunkuyar kasa a cikin kunya dajin nauyin hjyn data fito min da wanan zancen .
Nayi rantsuwa akan wanan kudirin naku kece da hakkuri jikata a ciki nasan kuma babu wanda ya isa ya wuce kaddaran shi a rayuwa.
Nasan kin yanke wanan shawaran ne ba tare da kinyi nazari a rayuwan ki ba na abinda zaije ya dawo ga auren shi gareki.
Hakan kuma ya samo asaline ga yawan tausayin da raunin irin namu na mata ga da namiji da muke saurin yarda da bukatan su.
Naso ace kin manta da zancen jafar a rayuwan ki saidai a yanzu kadara ta riga fata don kin riga da kin amsa mai bakin alkalami ya riga daya bushe gare ki ko.
Dama ubangiji baya son ayi maishishigi ga al,amarin shi yanzu ni a nawa bangaren zan tayaku da addua insha Allahu ubangiji ya kade mana tsotsayin dake cikin wanan al,amarin naku amin.
Duk yadda naso hjy ta wayar min dakai kan wanan zancen hjy takiyin hakan fafir dole na hakkura na kyaleta da gutun sharhin da tayi min din.
A bakin hjy nake jin sunyi tafiya da ya mamud ko mami bata sanda zancen tafiyan tasu ba sai bayan tafiyan su ne tana neman ya mamud matar shi ke fada mashi sunyi dan balaguro da dan uwan shi zuwa wani business wajajen kaduna.
Kansu tsaye sukaiwa garin mu tsinke su isa misalin karfe daya da wani abuna rana a gidan dagacin garin mu sukaiwa kansu masauki.
Bayan gaisawa da gabatar da kansu gareshi dako waye mahaifin su take dagaci ya gane daga inda suke.
Bayan fahintar juna take suka gabatar mai da abinda ke tafe dasu ba bata lokaci take ya gane kowa ake nufi mai gari yadan musguda yana gyara zaman shi tare da fadin.
Kardai wanan yarinyar da uwarta ta kawo kara nan gurin mu kakarta da mahaifinta sunkaita birni aikatau ba tare da sanin wurin wanda aka kaita ba taka maimai.
Ya mamud ya tare da fadin a gidan mu take aiki a hannun mahaifiyar mu hjy maryam lerai take zaune tare damu.
Yanzun ma tafe muke da zancen auren yarinyar kanina gashi shike son auren ta sai kanin mahaifin mu gashi zaune tare da wan mahaifiyar mu Alh bello samu,naka.
Munzo da zancen neman auren yarku ne wa dan mu kuma dan danuwana kamar yadda addini ya kindaya muna da al,adan malam bahashe.
Maigari ya na,am tare da yabawa kamalan su da kuma yabawa ga iyayyen su ya nemi da sy bashi lokaci a nemo iyayyena da suka haifeni don a sanar dasu halin da ake ciki a kaina.
Ba bata lokaci aka aika neman mahaifina dake bakin aikin shi a lokacin jin maigari ke neman shi don zuwan wasu baki da ba a san meke tafe dasuba a lokacin.
Hakan yasa Abba ya nemi da yaje gida ya sauya tufafin aikin shi dake jikin shi da farko don zuwa amsa kiran maigari da bakin shi saidai gaban shi na faduwa don baisan abinda zaije ya sama ba a can fadan lokacin.
Tunda Abba ya tunkari fadan ya hango tarin motocin dake wajen gaban shi ya shiga faduwa don baisan dame sukazo gareshi ba .
Shida ba birni yake shiga ba kuma ya san wani ba ta yaya wa yan nan bakin zasu danganta dashi.
Bayan ya iso sun gaisa a ciki mutunci dagacin garin mu ya gabatar mai da abinda suke tafe dashi a lokacin.
Ikon Allah Abba yace lokacin da aka nuna mai ya jafar din da yake zaune ya hakince a gefe daya bai wa kowa magana ga cikar kamalanshi da zati kawai shida dan uwanshi daya gama cika wurin.
Bayan bayane ne Abba yake fadin yana da magabata ga maigari sai su taru suyi magana abindaya dace yana fadan hakan ya fita daga zauren maigari yace bazaiyi magana ba kasancewar yarinyar yar fari ce a gurin shi.
Ba a dauki lokaci ba yan uwan mahaifina suka gabata zauren maigari take aka tsayar da maganan aure kawun su wan mahaifiyarsune ya zo da wani zance da cewa mai zai hana tunda gasu ga jama, a a daura auren ga baki daya inyaso daga baya duk wani al,adan aure ya biyo baya.
Take akai na,am da zancen shi abu na kudi haka suka zube kudi a zauren maigari aka yi yekuwa take gurin ya cika aka daura aure akan sadaki dubu dari don maigari da sauran iyayyena sunce dags hakan ba zasuso akara kwandala akaiba.
Da mamaki a ransu da kawu ya bude bayan motar shi aka fitar dasu alawa da sauran abubuwa da duk ake bukata a wurun daurin aure.
Karfe hudu na yamma an gama komai kowa ya watse ya nufi inda ya fito suma dai a ranan suka juya suka koma kaduna sai cikin dare suka shigo don jirgin sai karfe bakwai na marance yabar garin kaduna.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
3️⃣7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA INA MAKI FATAN ALHERI A KULLUN UBANGIJI ALLAH YA TSARE YA KARE YAIWA ZURI,A ALBARKA AMIN, , , ,
Ina bukatan addu,an ku gareni yar uwa badon halina ba sai domin Allah da annbinsa gareni Allah ya bada ikon yi lafiya Amin nagode ga wace ta samu lokaci tayi min dama wace Allah baiba dama ba taji tanasa hakan Allah ya kara haskaka muna al,amuran mu amin.
Tunda ya dawo gidan bai fita ko ina ba yana dakin shi har wayewan gari mami bata sakashi a idon ta ba.
A daren ranan ne kuma akai hira dashi a talabijin din NTA na kasa wanda mami tana zaune har da hjy kawai sukaga an haskoki shi a matsayin bakon da za ai hira dashi a ranan.
Mamakine ya