Showing 147001 words to 150000 words out of 191310 words

Chapter 50 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

fada yana maida hankali a wurin haraban gida tare da bin motan mamud dake shigowa gidan da kallo yana mamakin dawowan shi gida a wanan lokaci.
A hankali ya bar wurin tagan zuwa cikin sakin bacin shi har lokacin yana mai jin kunan rai a tare dashi don baisan amsam da zai ba mami ba a yanzu tunda ta riga da ta kamashi red hannded a shaye ko.
Ruwa ya shiga ya watsa a jikin shi duk sa safe saida ya watsa ruwan don jikin shi da yai mai nauyi a lokacin.
Yanzu kuma zafin da yake ji ta ko ina a jikin shi yasa shi ya nufi bathroom kai tsaye tare da sakewa kanshi zuwa jikin shi ruwa gaba daya don yaji sanyi.

Karfe hudun yamma mun gama duk wani shiri zuwa unguwan da innan tace muje mu gidan wani baffan ta dake can karshen layin su.
Sea tsawale nake tafiya don idon mutane dake yawo a kanmu a duk inda muka wuce dan gungun mutane a zaune.
Gidan irin ginan kauyen mune akwai zaure har biyu kafin ka kai kanka cikin gida gidane mai dauke da matan aure guda uku ko wace daga ciki an kewaye mata part din ta da dan kishefa guntun katanga da bazata iya ganin sasshen yar uwata ba sai idan ta shiga daga ciki.
Nasan gidan don yana daga cikin gidajen da muka bude ido dasu tunda mukai wayau muna kai masu abincin sallah da yawon sallah kamar yadda al,adan bahaushe yake a karkara.
Sashen uwargidan muka nufa tana ciki da taranta ta amsa muns muka shigo tun a waje muka fara gaida ita da yaran don zaman uwaye suke a gare mu tunda inna diyace a wurin su.
Matar da fara,a take fadin a, a lale marhabi ga amaryan birni a gidan nan yaushe garin inji maki bako ?
Kafin in bada amsa halima kanwata ta cabe da jiya suka zo gobe ko jibi zata koma idan anzo daukan ta.
Ke kan fafi ba, a tambayeki ba sa,adatu takai mata dan duka a aika suna kokarin rikicewa da fitina a tsakar gidan mutane lokaci guda.
Tsawa na daka masu tare da masu fadan haka da sukeyi matar baffan ina na fadin indai wa yan nan ne ai mun saba da halinsu ko yaushe suna gidan nan tare damu ai.
Zama nayi saman tabarban da dayan yarta ke kokarin shimfida muna lokacin da muke maganan muka kara tusa sabom gaisuwa tare da tambayana yaya can ya nabaro su.
Sai mukaji dauri aure kawai daga sama haka kokaiwa malam ashe kin gama karbe mai dan kudin sadakan shi kin tafi birni kinyi auren ki a can kin bar mallam a soro ko ?
Da murmushi nayi tace ai ba a mamaki sa ikon Allah don wanan auren naki Allah kadai yasan manufan hakan gareku ubangiji yasa alheri ne hakan ya kawar da duk wani sheri daga gare ku .
Wanda ke sakin suka amsa da amin ni dai a zuciyana na amsa ban iya amsawa a fili ba don kunya da kawaici irin na yayan hausawan asali.
Tsaraban da inna ta debo masu muka zo masu dashi nayiwa halima signal da ido ta mika mata tare da mata bayani kamar yadda inna tayi muna bayanin a gida.
Ta amsa da murna tare da fadin barin kaiwa malam ya gani kafin ya fita wurin daliban shi yasan kunzo don idan ya fita baku samu ganin shiba sai bayan magariba zai shego gidan kuma.
Ta mike tare da daukan su kayan shayi da sabulen da nazo masu dashi ta nufi turakan malam din dake zaune saman buzun rago mai launin fari da baki a shimfide a kasa.
Ga kwanon hura a gefen shi da kofin silver maidan girma na ruwa ya amsa sallaman umma hari matar shi lokaci guda.
Bai daina shan furan ba saida ta kare mai bayanin tsab ya dauki kofin ruwan dake gefen shi ya kora kadan kafin yace sun iso ashe tun dazun su nake dan dako ban fita ba dama.
Ki masu iso su karaso ya fada a cikin yanayin da malam bahaushe kanyi magana da matarshi a cikin gadara da isa .
Har takai kofa yake fadin ji mana da sauri ta dawo baya don jin mai zai fada kafin yace na yanke shawara kecev zaki bi wanan yarinyar kamar yadda uwarta tazo ta bukata ai mata gada don ba wani abinda yahanasu zata nema muddin ina da karfin sa in kasa yimata shi kamar yadda zanwa dan cikina abu babu jin kyashi ko wani abu haka itama yahanasu din .
Na sani malam inna habbi ta fada tana gyara tsayin ta don maganan yazo mata a bazata kuma bata da halin da zata musa hakan ga maigidan nasu.
Da sanyi jiki ta fita daga dakin kafinta kawo wurin mu babu wani alaman damuwa a tare da ita alokacin sai fara,a dake fuskanta tana fadin mu isa mu yake jira a sashen shi dama ashe.
Nan muka barta ta aika karamar su watau amaryan malam tazo ta raba abinda muka kawo masu din na tsaraba.
Yana zaune a yadda matar tasa ta barshi muka shigo muka gaisa ya dan jamu da ba,a kafin ya dago yana sallaman su sa,adatu da su dan fita daga waje ya gama magana dani.
Ba bata lokaci suka mike zuwa wajen mutanen gidan inda suke zaune kafin ya dago yace min amarya watau kin koma birni kin mana wayau ko ?
A cikin dan kunya nake fadin ba gani na biyo ku kauyen ba malam tunda nan na saba dashi ni yadan yi murmushi yana tono wani abu a cikin kayan shi kafin yace.
Dazun uwarku tazo min nan hankali a tashe tana fada min wani magana wanda nina dauke shi kamar zancen matane kawai.
Don a iya bincike na tun dazun din ni alherin hakan nagani ta ko ina dan akasin shi baida yawa sai dai abinda ba,a rasa ba kawai wani lokaci na zama tare.
Don haka yanzu dai karbi wanan ki fara sha ya miko min wani ruwan rubutu a wani tsohon goran yought daya dan dushe kalan farin shi.
Dole hakana na karba na kafa kai kamar yadda yace insha da bissimillah in raga in shafe kaina har zuwa wuya sa fuska da sauran ruwan.
Yayin da nake faman yi shi kuma yana kokarin yan tone tone acikin kayan shi yana nema wani abu, har lokacin dana aje mai goran magani a gefen shi.
Kin sha kenan ya fada ba tare daya jiyo Inda nake zaune ba, na amsa da eh nasha malam nagode na fada a sanyayye.
Kai haha dai wanan aiyiwa kaine ne hidima mukaiwa banza don a zauna lafiya balle namu jinin mu fatan mu dai ladabi da biyayya ga miji shine abin bukatan mu.
Karbi wanan ya miko min wani abu kamar bawan icce yana fadin ki saka a baki ki dinga taunawa a hankali koda a wayane ki fadi bukatan ki gareshi yau kiga aiki da cikawan wanan.
Na baki wanan din ne ba do komai ba sai irin bayanin sa uwarki tazo mi dashi koda yayi wana auren ne da nufin ya cutar dake Allah ba zai taba bashi ikon hakan ba a kanki wanan kuma dan bawan iccen da kike gani a hannun ki aiki shi gareki yafi akirga ki dai saka a baki kamar yadda nace dake yanzu ya kara bada da sauri na dan balle na jefa a bakina sauran na bude yar jakkana na kada a ciki.
Addu,oi masu ma,ana ya ban tare da min nasiha akan zaman aure da rike duk wa yanda na sama a gidan da zuciya daya duk wanda yace zai bini da sheri abinsa zai koma mai zuwa safe zaibawa yaron shi wani rubutun akawo min na sha.
A nan yake min bayanin tafiya da matar shi tare da hikimar shi nayi hakan wanda shi yasan dacewan zuwa da ita din da zamuyi da irin ranan da zatai min a can din idan mun tafi baidai fito fili ya fada min komai ba ya barshi a dunkule hakana.
Munyi sallama dashi da matan gidan da muka samu su fito dukkan su waje ana girkin abincin dare gwanin ban shawa dasu kansu hade ake komai a gidan.
Yamma lis muka shigo gidan mu don dan biye biyen da muka yan gidajen yan uwa da kawayena kafin mu shigo gidan .
Sallama mukeyi ga lantana a tsakar gidan mu kamar ba musulma ba ta kyalemu bayan sai data juyo ta kallemu kafin ta hakademu gefe guda tana jan tsuki taci gaba da abinda takeyi a wurin.
Muryan innan mune da taji sallaman mu daga dakin ta tafito tana fadin kundawo ke nan yanzu nake fada daku a raina don me zaku bari ai magariba kuna waje.
Marigaba fa matattaram sheri ne ko sa,an ka ake son a samu a daidai wanan lokacin akanci galaban mutum ai mai sheri.
Muna ta sauri wallahi inna nasan bakya son ai fita a wanan lokacin na fada ina kokarin cire hijjab din dana saka a jikina da zan fita.



ZAINAB IDRIS MAKAWA








🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅


4️⃣4️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA


YAR UWA FATAN ALHERI A GAREKU KO YAUSHE ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMAN UBANGIJIN MU AMIN YA ALLAH, , , ,
YAR UWA KADA KI MANTA LITTAFIN NAN NA KUDI DON ALLAH KADA MU SHIGA HAKKIN JUNA DARI UKU NE KACAL ZAKI BADA , , ,



Kofa aka turo tare sa sallama a lokaci daya wanda hakan yasa ta mayar da hankalinta ga wanda ke shigowa dan karamin falon a lokacin wanda ba kowa ke zuwa falon ba sai lokaci lokacin don takardun aikin ta masu mahianci da take adanawa a falon nata.
Mami lafiya naga kira yafi a kirga a wayana ban san da shigansu ba sai yanzu na duba mami ta dago kai a cikin wani irin yanayi mai ban tausayi ta kalli dan farin nata dake tsaye daga kofa a cikin damuwa ga yadda ya samu uwar nasu alokacin.
Kara rikicewa yayi lokaci guda kai tsaye ya karasa shiga dan falon tare da samun wuri ya kai zaune a gefen ta.
Mami wani abu ne kuma ya faru ko kuma jikin ne don office din ki na fara zuwa yauma akace min baki samu fitowa ba.
A hankali takai hannu ta zare glass din dake idon ta yanayin da fararen kwayan idonta da suke ciki na bacin rai ya baiyana a sarari har dan na iya ganin yanayin nata.
Jikin shi yai sanyi sosai lokaci guda yasan ba karamin abune ke jefa mahaifiyar tasu ga tashin hankali irin haka ba ga sanin da yai mata na jajirttatan mace a duniya.
Dan gyara zama yayi ya fuskance ta sosai da kyau don jin me zata fada mai a lokacin kafin ta dago kai tace dashi.
Mamud for long ka san da Jafar yana shaye shaye dama ?
Maganan tazo mai a bazata saida yadan razana don yasan ta kwabewa kanin nasa ke nan yau tsakanin shi da mahaifiyar su din tunda har ta sanda hakan gareshi.
Mami yasha wan, , , , hannu ta sake daga mai tare da dago kai ta kalleshi tana fadin ai tambayan ka nayi kawai ka ban amsa in sani.
Ajiyan zuciya ya dam sauke kafin yace gaskiya mami ba zance na san lokacin ba saidai tun kan dai ya tafi Hong Kong nasan da yana dan taba abubuwa kadan ina kuma kokarin tsawata mai ko a lokacin.
Sheshekan kukan data sake ne a lokaci daya ya kara tayar mai da hankalin shi sosai har ya mike ya isa gareta da sauri yana fadin.
Haba mami kuka kuma at dis stage da jafar yake a kanshi aini ina ganin wanan bai kai abin kuka ba tukun illa a tsaye a fahinci waye jafar a yanzu ?
Da sauri ta dakatar da kukan da takeyi din don jin abinda dan nata ya sake fada mata kan dan nata da take gani shine hasken rayuwan da kowa nasu nan gaba.
Wanan dalilin yasa take kokari ganin ginashi a kasan nan tun tana raye don ko bayan ta ya kasance suna da bangon dafawa kamar jigon su.
Shine hikima da kokarin mami na nacewa da auren shi da yar gidan mamman bello mai ritaya tsoho wanda ke daya daga cikin dattijan kasan nan dake fada aji a arewa.
Sai dai shi dan baisan manufarta kan hakan ba duk da ya hango hasken a zancen ta tun farko saidai shi sam baida ra,ayin hakan a rayuwan shi.
Yasa ya kaucewa wanan hadin da mami din ke sonyi mai da ko wace yarinya da bashi yaji zai iya zama da itaba a rayuwan shi don kawai wani siri nasa na daban can da bai damu da kowama ya sani ba a yanzu .
Muddin dai din ya samu daidai da yadda yake son macen ta kasance a rayuwan shi nan din gaba.
Mamud me kake son fada min a yanzu mami ta fada a cikin wani sabon tashin hankali a fuskan ta kuma wanda yafi na farko hadewa.
Mami ba wani abu bane dubaga yadda jafar ke samun cigaba yanzu a kullun idan anyi duba ga yadda rayuwa yanzu ya koma ga mutane.
Mumunan faduwan gaba ya kara zowa mami din hankali tashe ta furta hakane mamud nayi babban sakaci da damana na uwa a gareku da bana bibiyan bayan al,amuran ku akoda yaushe.

Haka kawai daga kwancen yaji ranshi na raya mai yakira layin wayana a lokacin don jin yadda na samu gida da yan uwana.
Kiran farko har zai katse yaji an dauki wayan ana fadin bata nan tana waje muryan karamar yarinya da bata kai mace sosai ba ke fadi a wayana.
Ke wacece ke maganan ua fada yana dan murmushin da bai tashi yinshi a lokacin na sai yajo tace ni, nice halima kanwar ta.
Au halima ya fada kamar ya santa a fili dama , kina lafiya ?, ta amsa da lafita kalau , ina yayan naki ta tafi ya tambaya .
Bata fitaba tana nan tana gyarawa innan mu wurine yanzu aka gama fada da inna da lantana saboda wurin girji dan murmushi ya sauke don jin abinda yarinyar ta fada.
Kafin yace fada kuma tace eh kullun lantana sai taja innan mu fada tace a raba wuri yana sauraren ta a daidai lokacin yaji wani murya na salati ana fadin yanzu wayan yayan tamu kike jagula halima?
Ba jagula nake ba an kirata ne na daga ta fada daga a dan shagwabe amma ke din nan yana ji zasu kaure da fadan su da suka saba yi ko yaushe.
Samun kamshi yayi da rashin kashe wayan yana saurare duk abinda ke faruwa har dawowana dakin da mukai magana akan abindaya faru yana jin komai bai kashe ko ya damu da kudinshi da a Ke jayewa ba a lokacin.
Basu fada min komai ba tunda na dawo dakin sai da nayi shirin kwanciya barci ne waya ya dauki sabon ringiing a dan daburce na daga wayan, murya kasa kasa ina amsa mai sallaman shi .
Don nagane shi duk da ban tubuta mai komai a wurin sunan shi ba har yanzu muryan shice take fadin ke idan ba,a kiraki ba ba zaki taba kiran mutum ba ko ?
Ganin har innan mu na dakin zaune yasa na dan saci kallon inda take a dan kashe murya nake fadin kayi hakkuri na mantane ban kira ba.
What ya fada da dan karfi har saida na dan razana da hakan na samu da kyat cikin rashin damuwa na sake fadin na mantane bankira ba.
Ji nayi ya sake wani wawan tsuki a wayan tare da fadin ke kina da hankali kuwa ?
Sai kuma ba bata lokaci yaci gaba da fadi kai tsaye ba tare daya saurari mai zan fadaba wanda dai bai wuce kalman hakkuri ba gareshi a lokacin
Ke ki saurareni da kyau kiji may zan fada maki don gobe zamu fara deal din mu na abindana fada maki zai faru tsakanina dake na taimakon junan mu a tare.
Don haka goben nan akwai wanda zaizo garin ku da safe daga kaduna zasu diba fili a saya a ginawa mahaifiyar ki wurin da zata zauna tare dasu halimatu fada ya kare daga yau a zauna lafiya.
A cikin mamaki na dago kai na kalli inda inna take zaune tare da sauran yan dakin namu dake zaune a lokacin kafin in mayar da hankali a wurin wayan ina kallo a cikon mamakin ji abinda ya fada din.
A Ina ma yasan wata halima can na fada a raina muryan shi naji yana fadin akan karamin abu za a dinga batawa inna rai yadda naji tana fadi dazun.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login