Showing 93001 words to 96000 words out of 191310 words

Chapter 32 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

tarewa yaran nan fada a kan gaskiyata da zai tafi nema mata ai sai ya nemi shawarata yaji abinda na yanke a kanta.
Fada muna yanzu ai gashi zaune me kika yanke a kan yar nan a yanzu tunda an hutar dake baki ga hakan ba.
Iyami bansan yaushe hali ki ya sauya ya zama na mutanen zamanin nan wajen , , ,
Hjy ba nufina ke nan ba bandai jin dadin yadda yaran nan suke min abu gaba gadi haka kamar banda daraja a gunsu kamata yayi yazo ya fada min kafin ya samo mata din.
Sai kawai yazo yanzu yana fada min magana haka kai tsaye wai mondaya zata fara tafiya wani makarantar ma ka samo mata din.
Mami inda yaran nan suke zuwa a nan na sama mata itama sai su dinga zuwa tare duk da ita a secondary section zata zauna.
What har nawa za a dinga kashewa a kanta ke nan ina kosu yaran nan kana min korafin yayi yawa da farko saidana haneka.
Mami indai zatayi kararun ai karuwan kowa ne nan gaba don haka kiyi hakkuri nayi kuskure ya fada yana dukkar da kanshi kasa alaman ban hakkuri a gareta.
Allah ya kyau hjy ta fada tare da dafani tana fadin yar nan nayi maki murna ubangiji yasa a shiga da kafan dama nace.
Yaya na gode Allah ya karawa arziki albarka yace ba komai ki dai dage da karatu sunce idan sun gwada ki kinyi nasara zasu iya barin ki inda kike a can kaduna.
Allah yasa hjy ta fada tana tattara takardun dake gaban ta alaman zata bar falon ke nan nayi saurin mikewa ina karban kayan daga hannun ta.
Sai naji tana fadin wa zai dinga sauke su a school din kai ko driver zai kaiku ya amsa da fadin.
Dama ai nike saukesu kafin in shiga office yanzun ma nidin dai ne zan dinga sauke su idan zan fita .
Ka nema masu driver daga yanzu da zai dinga sauke su kai ka wuce office din ka kaji abindana fada ta juya wurin hjy tana fadin hjy zan shiga in karasa aiki a daki.
Ni dai na aje kayan na fito daga dakin don babu wani abinda zan mata a lokacin don haka na dawo falon na samu hjy da yaya mamud suna hira Aisha ta shige dakinta ko lokacin.
Har kasa nakai na kara mai godiya yacs Jafar ne ya saka in sama maki nan don haka shi zaki godewa idan ya dawo.
Sai ki mai da hankali ki samu abinda kikaje mema banda wasa ko wani hali na banza don Allah.
Nagode yaya na kara fada kaina yana kasa nake fadin hakan don gabana na faduwa tun lkkacin daya ambaci sunan ya Jafar din.
Suna ta hiran su da hjy ni kuma ina faman tunanen gargadin hjy a raina a wani bangare kuma ina Allah Allah in ga na fara zuwa makaranta ranan monday din.
Rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya hausa suka fada don yau gani a class tare da diya manyan mutane don an gwadani na ketare da kyat don su ba wani gata da zaka nuna masu su yarda su kaika gaba saidai idan kokarin kane ya kaika.
Na mayar da hankalina sosai ga karatuna banyi kawa ko aboki ba kamar yadda naga wasu sunayi a school din koda yaushe ni kadai zaka sama a class din ina bitar takarduna da akai mana darasi.
Ranan kwatsan mun dawo daga school tun a haraban gidan idona yayi tozali da bodyguard din shi suna tsatsaye waje suna mazurai da idanu don motan mu daya danno kai gidan.
Gabana ya shiga faduwa haka na daure na shiga cikin part din mu da sanda nayi arziki babu kowa a falon sai tv dake aiki a falon shi kadai babu mai kallo.
Da sauri na shige dakin mu inda na samu hjy zaune ta idar da sallah la,asar a gurin tana zaune.
A gurguje na tube uniform din jikina na fada bandaki ban fito ba saidana shirya a cikin wani dogon riga duk kayan da Aisha ta ban ne nake sakawa a jikinao.
Na fito na o da sallah nacewa hjy zan leka kitchen in fito daga can na zauna abina ina taya su mama kande aiki har muka karasa na dawo don yin sallah lokacin har mami ta dawo tana dakin ta .
Tunda na tun karo wuein kamshin turaren shi ya daki hancina na tsaya na dan saurara ko yana dakin in koma kitchen in zauna har ya fita.
Naji banji wani hayaniya a dakin ba na shiga hjy ne zaune ita kade tana ganina take fadin wai ina kika shiga haka daga barin je in dawo naji shiru sai yanzu.
Har yaron nan ya dawo daga balaguron da yayi yana tambayan ki bai dade da fita daga dakin nan ba.
Wa ke nan na tambaya kamar ban fahince ta ba tace wanan bayahuden mana jafari ai ya dawo tun dazun da ranan nan wai wata kasa yaje kallon ball kawai don barnan kudi.
Shiru nayi don ban san me zan fada ba sai kuma hakan yaiwa hjy zafi take fadin anya yar nan kinko damu da yaron nan kamar yadda ya damu dake.
Don shi da zuwan shi ke ya fara tambayana na fada mai kindan fita sai gashi shiru shiru baki leko ba dakin nan sai yanzu daya fita.
Ko uwar taku tayi nasara a kanki ne tun yanzu nace hjy dan Allah ki daina zancen shi dani kada mami taji ta riga da tayi min kashedi a kanshi tun a kaduna hjy.
Ita iyami din hjy ta fada nace hjy kada kiyi mata magana ko dan karatun nan da yanzu nakeyi kada in rasa sa,ata ta wanan dalilin.
Wai maryama kanta daya kuwa gaba daya yarinyar nan ta rikice min lokaci guda na kasa gane inda ta dosa kan zancen nan.
Haka mukai ta shan bambam dashi ban yarda mun hadu ko sau daya ba a gidan tundaya dawo garin.
Ran ba makaranta ina zaune inawa kaina kitso muna hira da hjy ya fado dakin namu daga sallaman shi ya kutso kai ciki.
Ba daman in gudu in shige koda bathroom ns don ya riga daya ganni ko dole na daure na gaida shi tare damai an dawo lafiya.
Shima yadda ya amsa min naji dadin hakan don ba yabo ba fallasa gareni sai na mike zan bar masu dakin don dai kawai in kaucewa warning din mami gareni.
Ki zauna fita zanyi na leko hjy ya fada daga inda yake tsaye yana magana da hjy gashi ya kara haske sosao yayi wani kyau dashi bakin gashin kanshi yayi lub kwace a kanshi sai sheki yakeyi ga wani saje daya bari a fuska tasa wanda bai saba bari shi a fuska ba.
Yana gama magana ya sa kai ya fita ya bar dakin gabana sai faduwa yakeyi min don abinda idona ya gane min din duk da ban kalleshi sosai ba ma ke nan.
Tun daga wanan rana ban yarda mun kara haduwa dashi ba a gidan don ina ganin shima bai faye zama a gidan ba sosai sai jefi jefi.
Ranan zan fito daki ke nan don hjy na falo mami tafita gurin aiki bata dawo ba ina ganin shi na ruga da gudu na koma daki a zatona ko bai ganni ba ne.
Saida ya dan dade a zaune kafin ya mike ya nufi dakin namu hjy dai tana zaune tana kallon shi tare da tausayi mu a ranta.
Ya tsaya daga bakin kofa dakin bai karasa shigowa dakin ba sai hannun daman shi dayayi amfani dashi wurin rike labulen dakin dashi.
Wa kike gudu haka ya fada a cikin muryan nan nasa mai fida sauti mai dadin saurara kunnuwa suka jiyo min hakan.
A razane na juyo ina kallon shi yana tsaye a kofan yadda yake a wurin wani irin tsoro da damuwane suka ziyarci zuciya sosai take jikina ya fara kyarna ta yadda har ya fahinci hakan.
Hannun ya sauke daya tokare kofa dashi yana gyara suit din dayake sagale a hannun nasa karya fadi.
Takowa naga ya fara yi zuwa inda nake
haka yasa gana ya tsananta da faduwa sosai a haka ya iso inda nake rakube ga bango ginan dakin.
Wani abu naji yana taso min wanda yasa na duntse idona a hankali kafin ya kara tako ya cin min a gurin.
Jin kamshin turaren jikin shi gab dani yasa na bude idona na dube shi kadan babu sauran tako a tsakanin mu ko daya a yadda muke tsaye a dakin.
Kokarin ja nayi baya sai dai babu inda zan daga don gaba daya ya tare wurin ya tokare hannayen shi a ginan dakin.
Shiru ya ratsa dakin ba wanda yai magana a cikkn mu kamar babu kowa a dakin lokacin.
Inan tsakiyan hannayen shi har lokacin idanuwa na a rutse kamar naga dodo a gabana.
Ga ba hanyar da zanbi in gudu daga wajen don ya hana hakan gareni ya kankame ko wane gefe da zan iya guduwa mashi.




ZAINAB IDRIS MAKAWA










🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅




2️⃣8️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA


LITTAFIN KUDINE DON TURA KUDI ZAKI TURO GA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU NE KACAL KATIN WAYA KI TURA GA WANAN LAYIN 08036959257

YAR UWA DON ALLAH KI DAURE KINA BIYAN HAKKIN MUTANE DON ABIN BAN YAFE BA KALMACE MAI NAUYI GA MUSULMI NAGODE.




Har lokacin idanuwana suna a rufe ga numfashinsa ina jin saukan su a kunnuwana idon na kara budewa don jin shirun da yai yawa na dauka nike haukana a lokacin shi baya ko wurin.
Yana nan tsaye a yadda yaken haka yasa na soma kokarin sunkuyawa ta kasan hannun shi in samu in wuce don tserar da rayuwata ga mami dashi.
Ji nayi ya kamoni ya kankame ni a jikin shi tare da mamaye ni cikin wasu irin abubuwan da ban taba tsintar kaina a cikin ba ko a mafalki ban san da wanan nau,in abinba.
Haka kuma ban taba sanin ana wanan abin ba na dauka sai kafiran turawa da nake ganin haka a film danazo gidan mami.
Suma din kuma idan sunayi kawar da ido nakeyi koma na tashi na bar wurin ga baki daya.
Can kasan makogorna na iya furta innalillahi don Allah ya jafar ka bari kada kayi min sanadin da mami zata koreni gidan nan.
Bai kula da abinda nake fadi din ba yaci gaba da abinda yake min kamar ma zancena ya kara mashi kaimi ne .
Babu inda baya karkarawa a jikinsa don abinda yake min din nikan na sadakar sai hawayen da ke zubomin kamar an sake famfo na barwa Allah lamarin sa duk abinda Allah ya kaddara min mai kyaune.
Muryan shi naji a kunne kamar mai rada yana fadin mami kike tsoro yasa har kika fara guduna kina boyewa ?
Idan mami din ta sakaki ki min hakan ko ta hana ki aure ni kamar yadda na bukata ai ba zata hanani wanan bako ?
Abinda mami taji ke nan a karshe wurin da take tsaye ta mutu a tsaye don mamakin ganin halin data same mu a ciki a dakin.
Da sauri mami ta juya kafin ko wanin mu ya ankara mu farga tana gidan a lokacin ta nufi dakin ta da sauri duk maganan da hajiya ke mata a falon bata jita ba.
Karan sakin kofan da mami tayi ne ya farga damu don dai kawai tsoron dake yawa a zuciyana ne daya rufemin ido ban farga da ita ba tun shigowan ta dakin.
Yanzu kan sheshekan kuka na fara mai don na kula in dai ba mami ba hjy tsohuwa ce ta rutsamu a halin da muke ciki.
Ya jafar don girman Allah don ya rasulillahi ka, , , , , shhh yace tare da fufe min baki da hannun sa na kasa karasa abinda nake nufin fadi karshe.
I boldly care da duk wanda zai shigo ya same mu a haka dake dakin nan idan su basu san soyayya yada yake ba wanan ni bai taba damuna tunda sun hana min abinda nake so.
Naji yaya ba zaka taba damuwa ba don kai nan gidan kune bayan hakan kuma kai na miji ne dama mace itace da kunya ai.
Idan mami ne ta bar wurin nan na tabar da yau ban kwana a gidan nan don ta riga da tayi warning dina tun kan muzo garin nan a kanka.
Babu inda zaki tafi matukar ina raye a gidan nan doIn ko kin tafi dawowa zakiyi ita mami tasan halina idan ke baki sani ba.
Ban taba cewa ina son abu har in sashi a raina ban in rasa samu wanan abin don haka ba zan soma shi a kanki ba.
Naji amma don Allah ka barni in bar gidan nan yanzu tun mami bataji wanan maganan ba yau ta kasheni gidan nan.
Don girman Allah ka daga, daga nan in fice na fada cikin wani irin kuka daya zo min mai karfi.
Maimakon ya daga daga wurin saima naji yana kokarin kara matseni a jikin shi.
Kayi ma Allah kaimun alfama na hadaka da girman iyayyen ka ka daina rike ni haka kana hadani da fushin ubangijin mu.
Ka rabu dani ya jafar ka kyale rayuwana hakana ya huta da wanan ukuban daka sakani a cikin sa yanzu.
Ka taimakeni ka taimaki rayuwana da kake shirin rusa min yau karatuna shike nan na rasa shi tunda mami kauye zata mayat dani ina gap da gamawa.
Nima ki taimake ni zainab don ke kadai zan aura a kasan nan in zauna lafiya dake bani na sawa kaina son ki ba Allah ne ya zaba min ke don hakkurin ki da tarbiyan ki.
Abu daya nake so dake shine ki daina cewa zaki bar gidan nan ko karatun ki zai tsaya ba wanda zai faru daga insha Allahu.
A razane na dago kai na kalle shi kafin in mayar da kan kasa don kwarji da nauyin da yai min ga kallon shi.
Ya daga min gira yana fadin nasan mami zata yarda da bukata na idan na kafe a kanki a cikin sauki.
Don farin cikin ta shine nawa itama nawa shine nata bata taba hanani abu nayi shi ba a duniyan sai wanan karon kinga ko zatayi min adalci a nan.
So da sannu mami zata fahinta ta yarde mana muyi aure in dauki mu tafi can inda zaki karatu sai kince kin gaji da karatu a rayuwan ki.
Wani irin takaicin sa da tsanar sa yake tokare min zuciya ga tausayin kaina danakeji nida kaina kamar in dora hannu aka in ta kurma mai ihun a dakin sai anzo an ceceni.
Sai da ya fahinci ya gama hada min zafi akaina don kansa ya janye min daga banga bangan dayi da farko ya tare ko ina da zan iya sulalewa in gudu daga tsayin dayayi a gaba.
Kamar jira nake ya nuna min kofa in gudu aiko yana nunawa na sheka da gudu ina kuka mukai karo da hjy a kofa da tazo shiga kamar.
Duk da nayi murnan ganin ta amma naji haushin da sai yanzu ta zo dakin duk dadewa da mukayi a tsaye tare dashi zuwan ta yai min kama da zuwan yan sandan indiya da sai an gama cin gari suke isowa.
Fadawa nayi a jikin ta ina kuka take ta rude a wurin tana fadin a rikice maikai mata jafari na fadama kabi yarinyar nan a sannu akwai kurciya a tare da ita yanzu sai ka lalabata tukunna.
Ask her idan nai mata wani abin just magana nayi mata kan guduna da takeyi kawai.
Ba dole ta gujeka ba kaida uwar ka kun saka yar mutane a gaba haka wanan hattaran yai wa yar nan yawa a gidan nan.
Ai saika tashi kaje don uwar taku ta dawo har ta leko nan baka sani ba kana nan kana gyara kanka a wurin mace.
Hjy kefa kikace sai na jata a hankali zata fahinceni na fara hakan kuma laifine yanzu hjy ?
Laifine kan indai zaka dinga sakata kuka haka ko wani lokaci murmushi ya sake mai laushi yana kada kai tare da fadin well i know what to do next barin leka mami ya fada yana mikewa har lokacin ina a jikin hjy ina dan sheshekan kuka.
Yana fita daga dakin na dago kai ina fadin shike nan hjy yau zamana ya kare karatun da nakewa murna ya tafi daga gareno don mami korata zatayi yau gidan nan.
Saboda kawai kun kebe dashi a nan zata kore ki hauka tayi kome daga haka sai kora kawai.
Hjy mami tayi warning dina tun a kaduna kada in yarda in tsaya da danta don ta riga da tayi mai mata ko.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login