Showing 144001 words to 147000 words out of 191310 words
Chapter 49 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
mungode ma dadin mu da gobe saurin zuwa wallahi.
Yanzu ai sai muga ankai mutum makka shine zamuyiwa mutum ai murna ko a sauya mai gida kinga an rufe baki zagin diya mata a gidan nan ga baki daya.
Har sukayi suka gama ina lafe a dakin inna ban samu abindana fada ba sai faman tunane nake a kasan zuciyana.
A yanzu zancen ya jafar ya fara tasiri a zuciya don gaskiya innan mu tana so hutun da yake kira masu a yanzu.
Ba inna kadai ba har yan uwana da Abban mu shi kanshi yana bukatan kulawan daya dace a yanzu.
Kafin innan mu ta karasa girkin ta har barci ya daukeni a gurin saida akai kiran sallah a zahar kafin sa,adatu ta tayar dani daga barcin da ya dab daukeni.
Sai lokacin na fito waje tun bayan shiga dakin daga wurin rakiyan hjy da muka tafi tun lokacin ban fita wajen ba ina dakin mahaifiyar a ciki damuwa .
Nazo gida ban huta ba a can kuma ba zancen hutu ko kwanciyan hankali a gareni fara ma nan din na samu na lafe a dakin innan mu din.
Bamu samu natsuwa da inna ba sai dare baya kafa ya dauke ne muka zauna zaman hira da inna din.
Ban boye mata komai ba yadda komai ya faru a tsakani na da mami na labarta matashi a cikin daren nan ko zan samu sa,ida ga abinda nake ji a raina.
Ikon Allah Inna ta fada tana ajiyan zuciya tare da fadin wata sabuwa cakwakiyar kenan ke shirin tunkaro mu ashe.
Yanzu ita hjy da kanta take kyamatar ki da danta don kina yar tallakawa ko don wani mugun halin naki da koka boye min bansan da shi ba ?
Da sauri na dago ido duk da babu wadattacen haske a dakin lokacin inna taga kallon razanar da nayi mata alokacin .
Inna ki yarda dani da tarbiyan da kuka dorani tu farko ban kara wani hali ga wanda kika sanni dashi da farko ba ban yarda duniya ta rudeni ba inna don nasan kudi daine iyayyena komao dadewa wurin ku zan dawo zaman can din na dan lokacine.
Kafin in kara inna ta tare da fadin kimar ki da kamalanki ne ne basu kai ta hada iri da ke ba kamar yadda mafi yawan masu hannu da shuni suke da wanan akidar bawai ke dince bata so ba a zahiri a yadda na fahinci zancen.
Inna bata sona yanzu sam zama kawai nake a gidan dan hjy da danta daya jamin duk wannan abin a yanzu.
Inna har fa sata mami da yar ta suka dora min a gidan sai da shi dan nata ya biya kudin yakuma sakatar dani duk wani aiki da nake a gidan da sunan biya haka na zaune a cikin su babu walwala ko sakewa komai akan hattara da tsamgwama nakeyin shi gidan na karasa fadi a cikin kuka.
Subbahanallahi wanan wani irin rayuwa muke shirin fuskanta karfin mu ba daya ba balle na nuna jayyaya ko nace zan kwatar maki hakkin ki garesu.
Bazanyi izzigili acikin sha,anin aure ba don aure abune mai rai da Allah ya hallita kamar rayuwa idan kaddara sai anyi shi idan kuma zama ya kare ko ana so sai an rabu a tsakani.
Shine dalilin da yasa akeson musulmi ya yadda da kaddaran ubangiji maikyau ko marakyau ka yarda daga Allah komai yake.
Kuka na sakawa inna don gareta kadai na dogara da zata tsaya ta kashe wanan auren don ita kadaice nake hango gatan mu a gareta da tausayawa don Abban mu yanzu sai a slow tun shigan lantana rayuwan shi.
Da mamaki inna ke kallon yar nata a cikin tausayi da kulawa take fadin menene ne a ciki aure ne bautan ubangiji kowace mace da yadda akasin nata yake zo mata.
Idan ma wani mugun haline gareshi har yake boyewa na roki Allah a sandiyar ki ubangiji ya sauwaka mai ko menene a rayuwan shi.
Idan kuma da zuciya daya ya aureki ubangiji ya kara mashi sonki da kaunar ki a rayuwan zaman ku tare da zuri,a masu albarka.
Bazan taba ja da ikon Allah ba don haka kema nake gargadi ki da ki yadda da kaddaran ki a yadda tazo maki.
Allah yasan hikimar daya shimfida a nan ya tsameki daga cikin mu ya kaiki can cikin su kika zauna tare dasu har hakan ya faru yanzu.
To a barwa Allah sanin sa a hakan illa iyaka gobe zan turaki can gurin kawuna Inda addu,oin da zai baki sai ya taimaka muna dashi kafin nan nizan fara zuwa naimai bayanin komai insha Allahu.
Dan sheshekan kuka nakeyi kafin inna tayi shiru tana saurarena ba abida nake tunawa sai irin tsana da kiyayyana da yanzun nake hangowa a idon mami din ko yaushe.
Sai zuwa can naji inna tace yoke ai ya kamata ki hankalta tun daga yanzu ki sancewa ubangiji mai sonki ne yar nan baki da wani zabi dayafi kita godewa ubangijimu .
Dazun nan kika shigo gidan kin dai ga abinda ya faru a gidan nan shi kadai ya isheki ishara a rayuwa duk wani izzigilanci da ji da kai na lantana bai hana ta karbi abinda kika kawo a karkashin ki ba.
Ko wanan ai wani babban baiwa ne da cigaba a wuri Allah wanda yake zaton ka da komawa baya yau a wayi gari yaci ta karkashin ka.
Don haka hakkuri zakiyi kaddarar kice a hakan haka ubangiji ya tsara maki baki isa ki kaucewa hakan ba.
Don yanzu idan nayi fushi nace zan kwata maki hakkin ki da karfi da yaji na dauki mataki sai mu taru mu nunawa ubangiji ke nan bai isa garemu ba.
Haka dai inna tayi ta rarashina har barci ya dauke ni ban sani ba tun ina dan bata amsa har taji nayi shiru hakan yasa ta gane barci ya daukeni ne ta shiga nata tunanen a nan don abubuwan da take hangowa bata dai yarda ta nuna min hakan bane kawai.
Tasan ina ciki wani mawuyacin hali mai wuyan sha,ani da wanan baiwar Allah da Allah ya hada rayuwana da ita don mutum ya nuna bai kaunan ka a cikin ahalin shi abune mai wuyan sha,ani don ita kanta zaman abinda take fuskanta ke nan in badon ta kwabe tsakanin lantana da Asabe ba aka gansu a rana.
Don haka dole itama ta jajirce ta dinga yiwa yarta adduan fatan alheri ga halinda ta riski kanta a cikin shi duk da tsohuwan bata boye mata komai da take hasashe ba kan wanan auren nawa.
Don haka take son inna ta kara kwantar min da hankalina na samu tsuwa ingano mai hakan da yayi, yake nufi akaina dashi din.
Dole sai a cikin hikima da basiri inna zata iya fahintar dani manufan hakan a yanzu don hakane kawai zan samu natsuwa akan zancen.
Washegari tunda ba idar da sallah barci na koma duk daba gajiya a jikina saidai rashin barcin da bamu samuyi da wuri ba nida inna.
Can ciki barcin wani hayaniya ya kara tayar dani don muryan lantanace har kofan dakin mu tana magana kamar a cikin dakin take a lokacin.
Da mamaki na mike kome ya faru suke wanan fitina haka da sassafen nan a cikin maganan na dan tsunci zancen daya hada fadan wai ashe lantana tace bata yarda da rabon da inna tayi a jiya wanda asalima ba inna bace ta raba kayan sa,adatuce ta diban masu komai ta aika dashi.
A hankali nake gyara rigan barcin dake jikina a lokacin tare da fadin inna don Allah kuyi hakkuri meya kawo wanan zancen yanzu kuma.
Daga gefe dayan kanwata ke fadin wai shikafa aka aika mata dashi shine tace yayi maya kadan ko jiya dai ta karbi abinda aka kai matane.
Shine tazo yanzu take wanan fadan da innar mu wai sai an raba daidai ko a kara mata Abba kuma ya daure mata ginda a hakan wai a kara din.
Karbo roban ki kara mata din Allah halima wanan fitina ya kare hakana baza a karaba tayi abinda zatayi din sa,adatu ta fada a hasale.
Sa,adatu dan Allah ki bari a bata koda baku bata karewa zaiyi don ba zaku tabbata dashi ba ai har abada nafada tare da mikewa na nufi kofan dakin da lantana take tsaye.
Abin mamaki ba lantana kadai bane akofan har abban mu yana tsaye a bayan ta tare da dan yaron su rungume a jikin shi da ganinsa a ckin damuwa yake sun kwana suna fitina kila a dakin.
Buhu dayan na mika mata iyakata kofa dashi tana ganin haka tace yanzu naji magana kan dama wanda bai fita ya nemo ba yafi me nema rowa ai.
Tana kokarin jan dayan buhun da muka kai mata kofa zata tafi dana baho da aka zuba nace halima dauki na bahon ki kawai kaka ta kara.
Daya da rabi zamu tsira dashifa yayan mu kanwata Amina ta fada cikin dan marairaice murya nace ki godewa Allah da wanda kuka samu Amina.
Kinsan wanda zaku samu gobe ai,shi alheri takine barta Allah zai kawo muna wani wanda yafi wanan din data dauka.
Nayi mamakin ganin tunda safe ashe girki inna ta hada a gidan lafiyayye da zamu karya dashi da kayan miyan daya hadasu fada da lantana wanda Abba ya kawo muna da hjy.
Kowa na gidan saida ta zuba mai daga Asabe kakarmu har lantana naji tace a kaiwa dan lantana abincin ma,anade tayiwa dan lantana kara.
Wa yan nan dabi,un na inna sukan ban mamaki zakaga an mata abu saudayawa da zaran ta mayar da marta jan abu daya ya waddatar da ita ke nan bazata sake bi kan abinba kuma.
Tana gamawa wanka ta shiga a gurguje ta shirya tare da fadin zata dan fita unguwa mukai mata sai ta dawo wurin muka zauna zaman hira da yan uwana ranan sa,adatu batayi sana,a ba sai labarin abinda daya faru bana gidan suke ban.
Wanda hakan yasa na kara jina wasai kamar babu abinda ke damuna a rayuwa neme kuncin da nake ciki na rasa ga baki daya sai fari cikin daya mamaye zuciyana.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4️⃣3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
BARKAN MU DA YAU YAR UWA UBANGIJI ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMINSA AMIN, , , , ,
Kofa a rufe yake koda ta murda don haka ta tsaya kwankwasa kofan don a bude maya daga ciki.
A hankali yake bin kofan da kallo kafin yaji an tsananta buga kofan yazo ya bude yana tsaye mutum din shi sak saye da jallabiya baka a jikin shi sai farin jikin shi daya karawa jallabiyan kyau a lokacin a jikin shi.
Yana buda kofan sukai arba da mami dake tsaye a cikin daure fuska da dakewa baya yaja ya matsa mata ta karasa shiga cikin dakin.
Mami lafiya da safen nan ya fada yana msi bin bayanta zuwa wuri kujeran data nufa don ta zauna har lokacin tana mai bin falon da kallon abinda ta gani jiya yana dawo mata a ranta sabo fil.
Saida ta zauna dakyau suna fuskantar juna dashi dole irin kallon da take mai yasa ya dan dukar da kanshi kasa don nauyi da kunyanta da yaji lokaci guda duk da baiyi tunane tasan halin data riske shi a ciki jiya ba.
Sake dago kanshi yayi sau karo na barkatai yana dan kallon mahaifiyar tasu yana dukar da kai da idanuwan shi da suka fada a cikin yan kwanakin nan kamar wanda yayi cutar wata daya dashi.
Saidai wanan karo ya kasa jimirin dukar da kan nasa gareta don irin idin data zuba mai tana kallon shi wanda ya kasa fassara ko kallon meye hakan.
Wai mami lafiya na ganki a haka hannu mami din ta daga mashi kafin ta sauke wani irin zuciya da sai daya sake dago kai.
Wani ajiyan zuciya mami ta sauke kafin tace friend magana nazo muyi a matsayi na uwarka kuma abokiyar shawaran ka a kullun.
Jin hakan yasa ya gyara zama ya mayar da hankalinshi gareta sosai din jin abinda zata fada mai a lokacin.
Wani ajiyan zuciya mami ta kara saukewa kafin tace Jafar yaushe kafara shaye shaye a rayuwan ka ban sani ba ?
Tare da mika hannu gare shi tana fadin bani abinda kasha jiya a dakin nan na shigo har na fita baka a cikin hankalin ka.
Ba tare da fargaba ba ko tsoron data tsamaci zai baiyana a fuskan shi ya dago kai yana fadin ba wani abu mai wahala ai nasha ba mami kawai dai don hankalina ya dawo daidaine nasha.
A ciki tsoro da fargaban gami da tashin hankalin, abinda ya fada mami ta dago kai tana kallon shi a firgice tace kasan abinda kake fada kuwa ?
Kwayoyin dake a ciki hijjab dinta ne data kwashe a jiyan ta fitar tare da watsa mashi su a gaban shi sama table yayin da idanuwan ta suka kada sukai jawur a lokaci guda fiye da yadda ta shigo dakin da farko tana fadin a cikin wani murya dake nuna gab take da fashewa da kuka a lokacin tana fadin.
Why Jafar why da zaka jefa kanka a drug additct saboda wanan yarinyar kake kokarin bata rayuwan ka kome ?
Mami yarinya ?
Wace yarinya ke nan kike magana da har zata iya sakani wani abinda ba a sanni dashi ba dafarko kada a zargi kowa indan na aikara wani abinda bashi ba wanda ya isa ya sakani yi abinda ban tashi yi ba kai tsaye.
Ya karasa fada yana kallon mahaifiyar nasa ido da ido babu wani nauyi ko kunya a yanayi shi ranan.
Damm mami taji gabanta ya fadi don kallon da dan ke mata tare da bata amsa haka kai tsaye ba tare da jin nauyin komai a gareta ba.
Wasu irin hawaye ne suka ziyarci fuskanta a lokaci guda tare da fadi a cikin rauni Jafar haka ka koma ban sani yaushe zuciyarka da rayuwan ka shika fara wanan harkan ina raye ?
Mami ya fada a cikin wani murya mai nuna samuwa kafin yace kiyi hakkuri don Allah amma ni bansan na aikata wani abinda har zai sakaki hawaye haka ba a yanzu.
Mami kan duk inda tashin hankali yakai hankalin mami ya wuce nan ga tashi ita kadai tasan irin halin da take jin kanta a lokacin.
Shima kanshi halinda mahaifiyar tasu take ciki a lokacin ba zai iya jure ganin hakan ba gareta karfi hali kawai yake dakewa a lokacin.
Mikewa yaga mami din tayi wace a tunanen ta har zuwa lokacin abinda yasha di a jiya bai sakeshi ba.
Mami ta nufi kofa hankali tashe ya bita da kallon mamaki ba tare da ya iya furta mata komai ba a lokacin har ta fice daga part din nasa.
Komawa yayi ya zauna saman kujeran daya mike tsaye gareshi da farko tare da dafe kanshi zuwa sama suman shi da hannun shi daya yana mai shafan gashin kanshi zuwa baya a hankali kafin ya furzo iska daga bakin shi ya mike zubur daga zaunen tare da fadin Oh shit .
Don tuna ko meya faru dashi jiya din bayan security din shi ya fada mai zuwan su mami din gidan sa nacan daya ajemu da hjy.
Direct wurin window din glass din dake falo ya nufa wanda zaka iya hango haraban gidan mami din ga baki daya, daga inda mutum yake tsaye daga cikin part din nasa.
Glass din ya zuge tare da shakan iskan dake shigowa ta tagan alokacin yana mai lumshe idanuwan shi a hankali.
Allah ya gani baiso hakan ba a yanzu baiso ace mami ta fara fahintar rayuwan shi na boye ba wanda daga shi sai mahaliccin sa yasa da yana wanan halin da a boye.
Shikan shi bazai ce yasan lokacin da rayuwan ta fara mai hakan ba saida kawai ya tsunci kanshi dumu dumu ne a cikin harkan da ba addinin shi ya yardan mai yayi ba.
Muna a cikin wani lokaci mai wuyan fassara a yanzu da dole sai iyayye da yan uwa an dage dayiwa yara addua da saka ido tare da nasiha ko yaushe.
Baka zama talent a banza yanzu ko wani kuru a duniya sai ka karkata idan ba Allah ya tsare kaba da kaifi adduoin iyayye dake bin bawa.
Kusan hakan ne ya faru da Jafar din don shi kanshi ba zai iya cewa ga taka maiman lokacin daya fara wanan harkan ba a rayuwan shi.
Iyaka abinda ya sani shine shidai ko a yanzu yana iya kokarin shi wurin ganin ya gyara harkalan shi a kullun sai dai abin yaci tura har yanzu.
Yau gashi har mami ta fara riskanshi ga yanayin da bai dace ace ta sameshi a ciki ba, Allah kadai yasan a yadda ta riskeshi din a jiyan ya