Showing 156001 words to 159000 words out of 191310 words

Chapter 53 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

kin taimaki kanki.
Yana fadin hakan ya juya ya wuce ya barni tsaye da mamaki a wurin don na kasa fahintar inda zancen shi ya dosa a lokacin.
Gashi ba wai wata kawa ko abokiyar hira ke gareni ba a lokacin da zan kaiwa shawara na har mu gane me hakan ke nufi da zancen shi a kaina.
Ance idan bawa yana son walwale al,amari shiafi yawa haka yafi zuwa mai a daidai tsakiyan sallah don sai shedan yaso ya shagal dakai daga barin sallah ya hasko ma abinda ya shige ma duhu a lokacin.
Nima kusan hakan ne ya faru dani a daidai sallah la,asar danazo yi don yanayin damuwan dana shiga yasa na tayar da sallah a vikk kuncin zuciya.
Tiryan tiryan abinda yake nufi kr zuwa min a rai na har da wanda ban san zankai ga tunane ba saida na fahinci komai a lokacin.
Sheda kenen yaso ya ribanceni ta hanyat bata min sallah a lokacin na farga da hakan da sauri na mayar da hankalina a gurin ibadana.
Bayan na idar ina zaune wani shu,umin murmushi mai hade da sautin dariya yazo mi lokaci guda .
Hannu na daga tare da yiwa Allah godiya akan haska mi hanyar dayi a lokaci daya.
Sai muryan maizube ke fadin lafiya dai yar nan daga idar da sallah kin soma dariya haka kamar an maki bushara da aljanna.
Karfe shidda saura kiran shi yazo min na sameshi na falon shi duk sa bansan wurin ba haka nayi kokarin mikewa zuwa amsa kiran nasa.
Yana zaune a cikin shiri shi sai kamshi ke tashi ko ina a falon na shigo da sallama a bakina ba dauka ya karba hakan ba don ba lale bane ya amaa din.
Banyi gigin hawa kujera dake falon ba a lokacin don haka naja nakai kasa zaune dan nesa daga inda yake hankalin shi yana gun abinda yake a system din shi yayin da falon yai shiru na dan lokaci kamar babu kowa a wurin.
Kafin yadago kai yana fadi a uzurce OK kinzo ko tare da dan lumshe ido ya sauke su akaina a hankali kamar yana nazarina a lokacin.
Yau zan tafi kamar yadda kikaji na fada dazun wa mama don haka komai na kula sa gidan a yanzu zai dawo karkashi ikon ki a garin nan.
Duk wani kokari idan kinga dama ta yadda ba wanda zai fahinci meke tsakanina dake a wanan zama namu yanzu.
Yanzu wasan mu zai fara don a bayana abubuwa zasu faru da dama na sani saidai idan kin iya tsirar da kanki abin zaizo mako da sauki ko yaushe.
Da sauri na sake dago kai na dan kalleshi inda yake zaune din yace yes daga ni sai ke muka san irin zaman da zamuyi a tsakanin mu a yanzu.
Barazan mami ko wani dan uwana kada ki yarda ya kaiki ga furta masu komai dake tsakani mu ki tsaya kaida fata a matsayin matana kike a gidan nan barazan wani ko wata ba zai fitar daken ko ya tsoratar dake ba garesu.
Kaina gyada a hankali don ganin yana maganan ya tsureni da idanuwa shi idona suka dab ciciko da hawayen nadama .
Don tabbas na jefa kaina a tsaka mai wuya duka bangare biyun da nasa dana mahaifiyar su din dama wanda ka taso daga baya.
A hankali ya lumshe idsnuwan shi tabbas tausayin yarinyar ya kamashi don yasa ya jefa yar mutane a wani hali .
Wanda rashin wayau da ilimi ya kaita ga yarda da bukatan shi a kanta ba tare da nazari komai a game dashi ba kuma.
Yace kada kiji komai ba zasu iya illanta min ke ba dan kina a cikj matakan tsarona ta ko ina muddi dai kin iya kanki da bakin ki ko yaushe.
Ba tare dana iya furta mai komai ba na sunkuyar da kaina kasa hawaye na ci gaba da zuba min a hankali.
Shigowan yaron shi da shima na gansa a cikin shirin shi da alaman tare zasu tafi ke na tafiyan.
Ganin yadda nake zaune ina hawaye ya da kalle ni ba tsamani ko zato naji yana fadin lafiya take wanan kukan haka ko an mata wani abin ne kuma ?
Bai bashi amsa ba sai mikewa da yayi tsaye yana gyara kayan jki shi tare da fadin zamuyi sallama da ita ka bamu wuri ya fada mai ba tare da kallon inda yake ba yana daukan kaya.
Haka ya fita daga daki ranshi bace yana dan satan kallona a inda nake kamar mai tuhumana a lokacin.
Murya shi naji a daidai inda nake tsugune ina hawaye yana fadin zainab al,amarin mai girmane ba zaki gane ba a yanzu sai nan gaba zaku gane manufana.
Sai dai ya yanzu ke din kanwa ce a gareni zanso ki rikeni tankar kece Aisha na da muka fito ciki daya da ita wurin kulla da amanata da komai nawa.
Idan ki mun hakan na maki alkawari har abinda baki zata ba a rayuwan ki bikatana kawai ki nuna ma duniyake din matatave ta suna kuma yar uwata a badali.
Kin min alkari hakan ya fada tare da dan tsugunowa saiti inda nake makure ina kuka kafin in magana aka turo kofan tare da fadin kasan fa jirgin mu takwas zai daga kana nan tun dazun.
Kabar falo nan na fadama ya dan fada a hasale tare da nuna mai kofan a ciki zafin rai da sauri ya juya ya fice shima bai tsaya din ba ya mike tare da fadin ga key din daki nan zamu dinga waya duk abinda kike so zaki iya fada min idan na kiraki mu zamu tafi.






ZAINAB IDRIS MAKAWA










🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅



4️⃣7️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA




JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA ALLAHUMA AMIN, , ,




Duk yada naso na boye damuwana a lokacin nayi iya kokari wurin boye hakan saidai hakan bai samu ba don saida maizube ta fahinci hakan a tare dani .
Sai gashi ta koma lalashina wai a zaton ta saboda tafiyan ya jafar dinnne nake haka idanuwa da suka hau saboda kukan nadama danayi a lokacine.
Ba komai yasani wanan kukan ba sai fahintar inda na jefa rayuwata dan kawai tausayi da biyayya ga ya jafar din da yake zaton don deal din shine na yarda dashi da bukatan shi gareni.
Saidai kuma a yanzu kalaman shi sun fara jefani rudani don ban san a matayin da nake a garshi ba da wanan tunanen ya barni a gidan suka daga zuwa inda yake aiki.
Ranan kan mami tayi fushi sosai Allah ya taimaka a gaban hjyn taya kira yana sheda mata zancen tafiyan shi inda ta haushi da sababi saidai ta makara ga hakan don yana shiga jirgine ya kirata.
A zaton mami din tare dani ya wuce don idonta ya rufe a wurin har take ikirarin da sai dole ya dawo dani kasan nan inma don hakan ne ya guje mata din.
Aikin ma gaba daya zai bar can ne ya dawo nan kasan kusa da ita inda take iya ganin komai da yakeyi din a gabanta.
Saidai mami bata san da ta makaro ga hakan ba gareshi don a yanzu kan ba zata iya taro dan nata ba kai tsaye yadda take so din tayi.
Wai ke iyami yaushe kika koma hakane hjy ta fada a hasale daga gefenta ta dora da fadin zaki raba auren da Allah ya nufa sai anyi a tsakanin su ne ko me ?
Ta dago don fadin abinda ke a ranta hjy ta katse ta da fadin yadda kike zaton zaki iya yiwa danki baki ko ki tilasta shi ya saki yarinyar nan.
Ki tuna nima hakan ina da hakkin da zan tursasa ki a kanshi dan ni dince dai na haife ki ai .
Hjy yarinyar nan bawai sonta yake ba ko wani abu shima dole da akwai abinda yake nufi da yin hakan a zuciyar shi tunda bawai sone ya hadasu ba ai.
Iyami bana sonki da shiga tsakanin yaran nan wallahi wararana kunyan hakan zakiji da kin daure kinba yaran nan goyon baya a yadda yakeson abinsa .
Da Komai da zaiyi ai dole ya fada maki ko ya sanar dake amma zuciyar ki yana rudin ki kin hana kanki sakat da nasu haka .
Karfi da yaji kin hana yaron nan ya zauna ya huta a zuciyar shi balle kiji sirin zuciyar shi kinsan irin illan da kike jawa kanki ga yin hakan da kikeyi kuwa.
To idan ma har baki sani ba gara ki san abinda kikeyi ki bar yaran nan hakana idan ko kinki kin tsaya kina jayayya da ubangiji ne .
Sai Allah ya dauke ki a zauna lafiya ayi kuma bada ke din ba kinga sanadin hakan sai sauran diyan naki su zauna a marayu ke nan ba uwa ba uba garesu kuma.
Ina kema idan har talaucin yarinyar nan ne damuwan ki a haka uvan yaran nan ya aureki baki da komai a tare dake ilimin ma a gidan sa duka kika same shi ai.
Jikin mami yai sanyi ga abinda hjy ta fada dan tabbas kawar da ita din ba komai bane a gurin ubangiji ai.
Ganin tayi shiru hjy taci gaba da mata nasiha sossi inda take fadin ki kyakeshi da abinsa inma har akwai abinda yake nufi da hakan ai lokaci zai fadi hakan ga kowa.
Jalal da yanzu ya zama dan gaban goshin ta yana zaune a gefe yace mami gaskiya hjy ta fada ya j ai ba yaro bane yanzu.
Yana da right din da zai zabawa kansa abinda duk ya dace dashi kuma ai kinji hjy ta fada kila daddy mu ya biyo a wurin zabe shima.
Ran kwashi takai mai saida ya dafe wurin don zaifi tare da fadin aini na bar wanan zancen yanzu tunda na gane gaba daya kuna goyon bayan sa a yanzu kan hakan tunda yanuna maku yana da kudi da zai iya yin komai.
Ni kuma wallahi bana rsoro ko shakkar sa idan da ya biyo ta hanyar arziki dani zai iya hakkura dashi a hakan yaje yayi abinda yake so din ai duniyace dai ko , ?
Baki zaki masa ya kara lalacewa ko mai idan ma kin masa din dake dashi duniya zata zaga ai hjy ta kare magana a cikin zafin rai.
Har suka dawo abuja mami bata kara tayar da zancen komai akan da nata ba ko ni do tana zaton tare muka tafi dashi hakan yasa fushinta ya kara karuwa a zuciyar ta saidai batayi zancen da kowa ba kuma.

Sannu a hankali muka fara sakewa da wanan matar da ta gabatar muna da sunan ta da anty Fadila kamar yadda muke kiranta dashi.
Don da safe zata shigo har dakin da muke su gaisa da maizube ta dan ja halimatu da fira tun bamu sakewa har muka fara sakewa da ita a yinin farko da mukayi tare a gidan.
Sai ya kasance duk abinda zatayi zata kirani muyishi a tare da ita a cikkn sakewa da kulawa kamar uwar da ke koyar da yarta wani ilimi na duniya a yanzu.
A cikin hikima da basira take koyar dani zaman duniya da tako aka komai da rashin saka ido ga wani ko wani abinda bai shafeni ba can zamu zauna tana da bamu labari da zai dauke muna hankali ga komai.
Sai gashi mun dan sake da ita har ina iya tambayan ta abinda ya dan shige min duhu wani lokaci tayi min bayani akan komai .
Tun Saturday ta kaimu saloon aka wanke min kai akai kitso shiga school monday driver ya kaimu school don fara shirin jerabawa.
A school di muka hade da yaran ya mamud wanda a wuri su ne mami ta samu labarin ina kasan bai tafi dani ba ashe .
Tayi mamaki matuka don jin hakan koda ta tura ai mata bincike sai ta gane ina zama da fadila ce inda ta zaci ko wani alakane a tsakanin mu bata danta bane ya hada mu.
Inda ta gano ko waye Fadilan da kuma aikinta saidai ta kasa fahintar komai ta kawo ido ta saka a hakan don nasihan da hjyn ta tayi mata a kanmu.
Wanda nasan Allah ne ya dorani a kan mami din ta basar da zancen binciken komai a kaina har na samu daman fara jerabawa hankali kwance.
Yanzu kan ina waya da innar mu tun zuwan mu sabanin da cab da dif idan mun tafi har take fafa muna ginan da akayi a gefen gidan mu itace ashe aka ginawa gidan da zata zauna a ciki.
Inda sa,adatu take labaranta muna abinda ya faru bayan angama aikin ginan dayasa a ginawa innan mu sai lantana ta fara bala,i akan bata yarda da hakan ba dole sai Abban mu ya san yadda za a yi itama ta shiga ko a gina mata nata sashen da zata shiga.
Wani wan mahaifin mu kuma makwabcin mu ya fito yana fadin baki isa ba lantana don arzikin yartane ya kaita ga hakan don babu abinda baki fada akan tafiyan wanan yarinyar birni.
Yanzu da tafiyan ya kai ga alheri gare ta zaki fito kice ke baki yarda da hakan ba dole sai mijin ku ya dauki mataki a kan hakan wani irin mataki kike son ya dauka kan haka din a yanzu ?
Ko so kike yace ba zata shiga ginan da arzikin haihuwan ta ya jawo mata ba ta dalilin diyar ta data haifa .
Yanzu sai kije can ke mai haihuwan diya maza ki jira su girma kema su gina maki naki ai don Allah ba ai mashi ganganci ga hukumcin sa.
Idona ya kawo ruwa lokaci guda da take muna wanan bayanin ban karasa sauraren abinda take fada ba na kashe wayan .
Zama nayi cike da nazarin wanan abinda ya faru da innan mu din wanda a sanadiyan na da abindana jefa kaina a cikin sa wanda bansan ko me hakan ke nufi ba har yakai innan mu din ta fara samun saukin rayuwa a tare da ita.
Don haka ya zama min dole in jure duk wani kalubalin rayuwan gidan dan mami dana mami din a yanzu tunda har na gano hakan zai iya haifarwa mahaifiyata da yan uwana da zaman lafiya a rayuwan ta.
Karatuna nake sosai kuma ina fahintar hakan don bamu tare da wani mstsalan komai a tare damu a gidan zaman kadaicine kuma wanan Fadila din tana iya kokarin ta wurin ganin bamu shiga damuwa da komai a gidan.
A haka har Allah ya taimaka na gama zana waec dina muka zauna jiran zana neco din mu wanda a lokacin ne na samu dan natsuwa sosai tare da maizube da halimatu da yanzu itama take zuwa makaranta tare dani.
Na mayar da hankali sosai wurin koyon girki tare da anty fadila da sauran abubuwan da take koya min na zaman duniya a cikin hikima da basira .
Zakace ya da kanwa muke da ita a yadda nakan bata girma da kuma daraja sai hakan ya kara sawa matar sona a ranta sosai.
Don a yanzu mun sake da juna zata fada min kai tsaye idan nayi wani abinda ba daidai ko bai dace nayi shi ba a take zata tsawata min kan hakan a karshe kuma in bata hakkuri.
Sai ya kasance a dan watannin da mukayi da ita wani irin sabo da shakuwane ya shiga tsakani mu sosai har yakai ranan take tambayana labarina ?
Sai kawai na danyi murmushi ba tare dana furta komai ba a hakan muka bar zancen ba tare dana fada mata komai ba.
Da yake ita din mace wayayyiya a cikin hikima irin nasu nasu na manyan mata take dan tambayana wasu abubuwan a cikin hikima har take samun amsa daga gareni.
Take kuma sakani a hanya yadda zan kula da komai da zaizo min a bazata daga ko wani bangare.
Yau ban tun safe ban leka falon ba ina daki kwance na tashi sa ciwon mara wanda kan dameni duk karshen wata.
Har daki anty Fadila ta kawo min magani nasha wanda hakan ya sakani barci bayan nasha magani sai bayan karde hudu na samu fitowa falo na zauna.
Bandade da zama a falon ba halima ta shigo dauke da ledan corn a hannunta tana ci ta samu wuri a gefena takai zaune.
Na dago kai na kalleta ina mamakin ta a raina ban kaiga karshen mamakin ba ta jefo min tambaya tana fadin wai anty sai yaushe zamu tafi gaida hjyn ki sa kike aiki a gidan ta.
Gabana ya fadi don jin abinda ta fada saida na tattaro dauriya a raina kafin ince da ita kin santane ko wani abin kike son yi a gidan nata ?
Kai ta gyada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login