Showing 15001 words to 18000 words out of 86718 words
*SADAUKARWA GA:*
_ASY KHALEELí ˝í˛_
*TUKWICI NE GARE KU:*
_YA HAJJAH CEí ˝í¸ť_
_BILLYN ABDULí ˝í¸_
*SHAFI NA 14-15*
_This chappy goes to you *MISS HAFSY* favorite co-writer and a dearest friend of
mine_í ˝í¸ťí źíźšâ¤
nanahafsat.wordpress.com
Saurin d'aga kansa Dr Khaleel yai, yana duban Inna Bilkisu. Jaddada kai yai alamun yayi naâam
da zancen, Murmushi ya fad'adâa akan fuskar sa yace,
âWannan abu yayi Inna..Wallahi yayi, dama na jima ina son hadâa Saifullahi da wata acikin
yaran nan, sai dai duba da su d'in duk yara ne duka- duka sha biyar suke, kuma ko gama
makaranta basu yi ba.â
âHaka ne.. Amma ai ana aurar wa ko k'asa da hakan, sai dai yanzun ba kamar lokacin mu bane
tunda inaga Islam ce ma kawai tayi shekaru goma sha biyar ko?â
âEh haka ne Inna, ashe akwai tazarar shekara dâaya tsakanin su da Hafsat, ita Hidaya ce dai
suke saâanni da Islam.â
âEh..To amma fa ba cewa nayi lallai ba, ba kuma cewa nayi dole ba, kuyi shawara da d'an uwan
naka yadda kuka ga ya dace sai ayi hakan.â
âHaba Inna, ai wannan kyakkyawar shawara kika bayar kinga dama fa aiki yake yi, duk saâannin
sa sunyi aure, kuma shine dai-dai da Nusrah, saboda kinga ta gama komai na karatu, rantsar
da su kawai xaâai watan gobe su zama lauyoyi..â
âMasha Allahu, Allah ya sanya albarka a abinda aka karanta. Munyi waya da wannan yaron, (Ya
Bala) yace shima yau zai shigo Habujan, amma ban sanar masa ba tukun sai yazo sai ayi
komai a gama ko?â
âKwarai kuwa Inna.. Hakan yayi wallahi sosai, Allah ya k'ara miki lapiya da nisan kwana mai
amfani, Allah ya jikan Malam (mahaifin su) yasa aljannatul firdaus makoma ce agare shi.â
âAmeen ya Allah.. Allah yayi muku albarkaâ
âAmeen Inna..Bari naje ciki na gaya musu a yiwa Ya Bala girki kafin ya k'araso.â
âEh hakan yayi. A gaida suâ
âZa suji Insha Allahu, yau mazajen naki basu shigo miki bane Inna?â
âNi nace abarsu garin ya d'an rufa tukun na, sai akawo min su, kaga yanzu da d'an sanyi yau.â
âEh haka ne kam.. Toh bari naje Inna sai na dawo.â
âYawwa d'an tsaya..â
Gani yai ya tsaya daga tafiyar daya soma yi ya dawo ya tsugunna cike da girmamawa yace.
âMaganar su Karimatu ne, dan Allah nasan kana adalci sosai a tsakanin su, kar ka gajiya da
hakan, ka cigaba . Allah yayi maka albarka.â Kansa a k'asa cike da girmamawa yace,
âInsha Allahu Inna..Na gode kâwaraiâ
Mikewa yai ya fita bayan ya mata sallama, ko bata fito ta fad'a ba, sarai yasan kishi ne ya rufe
idanun su jiya suka zo suka yi masa sharri. Murmushi kawai yayi yana cewa,
âMata.. Kai Allah ya shirya mana zuriâaâ
Sashen Helwa ya fara shiga don anan yake, ita kadai ce sai maâaikatan ta don 'yan biyun ta ma
kullum a sashen Haj Aysa suke wuni, sai dai bacci ya dawo dasu. Wani lokacin ma acan suke
baccin.
Sun d'an taba hira nan yake sanar mata zuwan Ya Bala. Kitchen ta shiga bayan fitar sa don yin
abincin tarbar yayan mijin nasu. Daga nan ya nufi sashen Haj Aysa, ya jima yana d'auke da 'yan
biyun sa, gefe kuma su Arfat sai d'ane k'afafunsa suke yi, Islam dake kusa dashi ta zumburo
baki,
âDaddy...â
âNaâam Mamanaâ
âDaddy yanzu kafison su Areef. Sam baka sona kaman daâ Ta kâarasa fad'a tana shagwabe
fuska.
Murmushi yai yana riko hannun ta da yake a kusa dashi take, cikin muryar lallashi yace,
âHaba nina isa?! Mamana ai kece gaba da komai, kawai dai kinga su ne âyan fari a maza amma
kuma ai kece 'yar auta a mata ko?â âDaga kai tayi tana murna.
Sai da ya jima sosai anan har Haj Aysa ta fito daga wanka ya sanar mata zuwan Ya Balan, kafin
ya shiga wajen Haj Karimatu tana zaune tana aikin taunar cingam (chewing gum) dan ya zamar
mata alâada.
Gefen ta kuma Hafsat ce tana kwance rigingine sai shekâar bacci take.Tashin ta yayi yace ta
koma d'aki ta kwanta hadâe da jaddada mata karta sake kwanciya a rigingine ba kyau, duk
abunnan da yake haj Karimatu danna waya take, sai daya mike zai tafi ne ya dubeta yana
fadâin,
âSai faman danna waya kike, Wai ni ban gaya miki cewar hasken waya na cutar da ido ba ko
kuwa?â
âAlhaji wani littafin hausa nake karantawa wallahi, ba kaji dad'in sa baâ
Jaddada kai yayi yana mamakin wannan k'arfin halin nata,
âToh Ya Bala dai yana nan tafe, anytime from now, zaâa d'akko shi a airport..â
âToh.. Allah ya kawo shi Lapiyaâ
âAmeen!â Kawai yace, yai ficewar sa sashen Yafendo.
Tana zaune itada Nusrah sai rusgar kuka suke yi, shi abinma dariya yaso ya bashi wallahi, abu
ya k'ici ya k'i cinyewa, zama yai kusa da Nusrah, gaishe shi sukai dukkan su, ciki harda Hidaya
data fito daga kitchen da indomie a hannunta,
âDaddy ga indomie..â
Kallon ta yayi ita da indomien, murmushi yai yana kadâa kai,
âNagode Hidaya amman na koshi, indomie sai ku âyan indomie generationâ
Daria Hidaya ta kyal-kyale da ita tana zuba lomar indomie a baka,
âDaddy kenan, Allah indomie na da dad'i amma kai baka soâ
âZaki koya munci ne?â
âEh Daddy..â Ta fad'a tana dawowa kusa dashi da plate a hannun ta,
âHaa bakin ka to daddyâ Murmushi yayi kafin yace,
âAâa ba yau ba fa sai wani lokacin. Yanzu kije d'aki zamu yi magana dasu Umman kiâ (Yafendo
da Nusrah).
Amsa mishi tayi da toh, kafin ta haye sama abun ta. Juyawa yai yana fuskantarsu baki dâaya.
Ajiyar zucia ya sauke mai nauyi, hakan yasanya su juyawa su maida kallon su gare shi.
âNusrah..â
âNaâam Daddy.!â
âKisani shifa komai na duniya muqaddari ne daga Allah, Wallahi bamu da tsumi ko dabara ta
canza yadda komai yake tafiya a rayuwa face Allah ya yadda da hakan, Ina ilimin ki ya tafi?
Common and Islamic law kika yi, Duk Ina tarin tauheedin da ku kai yabar kanki? wallahi tunda
kikaga haka Allah ne zai musanya miki da mafificin alkhairi, ita rayuwa baka isa ka tsarawa
kanka yadda kake so ba, komai kud'in ka, ko mai k'arfin mulkin ka, kai kowacce irin sarauta ce
gare ka wallahi sai Allah ya yi ikon sa akan ka, saboda haka ki kwantar da hankalin ki, Insha
Allahu rabbi alkhairi ne wannan abu daya faru, dama can shi d'in ba mijin ki bane, kisa hakan a
ranki, ki cire damuwa kina jina ko kuwa da iska nake maganar?â
Saurin kadâa kai tayi,
âAbba duk naji, na kuma gode Insha Allahu zan sanyawa zuciata hakâuri.â
âMasha Allahu.. Ni kuma na miki alqawarin wata babbar kyauta nan ba da jimawa ba, zan cika
maki ita da yardar Allah..â
Murmushi tayi cike da murna tace,
âDaddy Nagode, Allah ya saka da alkhairiâ
âYawwa..â Ya fad'a yana maida duban sa ga Yafendo data rafka uban tagumi ta dulmiya duniyar
tunani,
âAminah(Asalin sunan ta kenan)â
âNaâam Alhaji.â
Rausayar da kai yayi, hakan ya sanya Nusrah saurin tashi ta basu waje, kalamai masu dad'i
yake yi mata, had'e da qarfafa mata gwiwa akan ribar hakâuri, ya jima kafin ya tashi yana fad'in,
âYawwa, Yaya Bala zai zo yau a kowa ne lokaci zaku iya tsammatar saâ
âAllah ya kawo shi lapia..â
''Ameen.'' kawai yace yasa kai ya fice.
Wurin matan Yaya Bala yaje suka gaggaysa, duk sun caba ado suna jiran mijin nasu ya shigo,
shi abinma dariya ya bashi ganin yadda sukai ado kamar wad'anda zasu zabâen kyau. Ya jima
suna hira kafin ya koma sashen sa yana nazarin (research) wasu litattafai.
***
Karfe 4 dai-dai Yaya Bala yana parlorn Dr Khaleel, an shirya masa abinci kamar wani
restaurant, ya d'anci ba laifi, nan Inna Bilkisu da ke gefe ta shiga sanar masa da komai akan
Nusrah kuma kwarai yayi naâam da xancen domin fuskar sa ta nuna hakan,
Shafa sankâon kansa yai, cike da murmushi yace,
âInna wallahi wannan zance yayi min dad'i ba kadâan ba, shi yasa yau na tashi duk zuciya ta
tana dadâi, ashe abunda xai faru kenan, to ni Ina ganin me zai hana kawai a hadâe ayi gaba
dâaya da nasu Mudasser da Muâutaseer, don suma sunzo sun sameni da maganar yaran da
suke nema, wasu yara ne anan Abujan, ita yarinyar da Muâutaseer ma yake nema yace k'awar
su Marwa ce, Toh Kamaludden ma dama ina shawarar hadâasu da Aysha 'yar Hansaâu, Toh
kuma ga maganar Saifullahi ma daddad'a tazo. Toh zan yiwa Nuradden magana ma kan lalle ya
tsayar da wadda yake so, shi kuma Shamsudden tunda naga mata basa gaban sa, Ina ganin a
hadâasu kawai da Shemaâu, duk muâaurar dasu mu huta Inna, Kinga nan gaba da an tashi nan
da wasu shekaru sai na su Islam, su ukun suma sai a hadâe ai nasu ko kuwa ya kuke gani?â
Hansaâu dake gefe sai gudâa take tana rangadâawa jin wannan daddadâan labarin,
âAbu zai yi dadâi, idan yaran zasu bada had'in kaiâ
Cewar Hansaâu cike da farin ciki, don dama a kauyen 'yar gaya 'yan uwan mahaifin su
Shemaâun sai gulma suke yi suna yada maganar yara sun zama gandâama-gandâama amma
taki ta aurar dasu, bayan ga saâoinsu nan sun tara âyaâya, dan tsabar iskanci ta kwashe su sun
koma legas sun iskance gaba dâaya.
âMu fa muka haife su ba su suka haife mu ba, aure tamkar anyi angama ne da yardar Allah
babu mai kawo cikas a cikin su, kuma watan gobe farko ko tsakiyar sa Insha Allahu xaâai bikin,
kowannen su ya tare a gidan sa, Alhamdulillah tunda kowa yana nan ba sai ance a jira wane
ba.â
âAllahumma Ameen! Allah ya sanya albarka, ya bamu saâa a cikin wannan lamarin.â
Cewar Inna Bilkisu wadda faraâa gaba dâaya ta cika mata fuska. Su hudâu ne dama a parlorn,
daga Ya Bala, Dr Khaleel, Hansaâu sai Inna Bilkisu. Tsaida shawara sukai kan anjima zaâa yi
General meeting don a shaidawa kowa abinda aka yanke....
_Munada biki jamaâa..í ˝í˛í źíżżí žíľ°â¤ anko na kece raini zaâa fitarí ží´_
_WRITTEN BY THE ELOQUENT WRITER;MISS XOXO_í žíˇí źíżź
[1/3, 10:53 PM] Miss Xoxo: *_SAIFUL_ISLAM...í ˝í˛*_
*_NA*_
_*ŠNANA HAFSAAT*_
*_(MISS XOXO)*_
ÂŽ *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_Home of experts and perfects writers)_
*_SADAUKARWA GA:*_
_ASY KHALEELí ˝í˛_
*_TUKWICI NE GARE KU:*_
_YA HAJJAH CEí ˝í¸ť_
_BILLYN ABDULí ˝í¸_
*_SHAFI NA GOMA SHA SHIDA(16)*_
_Wannan shafin na kune âyan *SAIFUL_ISLAMí ˝í˛FANS GROUP* Ina son ku, kuna âkaramin
âkwarin gwiwar rubutu, Musanman *Aunty Bilkí ˝í¸, Juwairiyya Ummee*_da *Mamuxee Sule and
Ummuh Islam*_ _kai da duk âdauka cin ku, Fatan Alkhairi gare ku hazikâan makarantaí ˝íší źíżž
jazakum Allahu khairaní ží´â¤í ˝í˛__
_nanahafsat.wordpress.com_
Bayan sallar ishaâi rankatakaf âdin yan gidan kowa ya hallara, jikoki kawai aka cire, sai su Arfat
da ba wani gane kan zancen zasuyi ba, duk suna sashen Haj Aysa, wajen Yakolo, Safa ce
kawai wadda bata nan itada mijin ta Mubassher. Amma dukda hakan anayin live video call
dasu, tamkar dai suna wajen.
Adduâa aka fara, gaba dâaya banda su Dr Khaleel babu wanda yasan akan mai taron zai
gudana, duk âdauka suke labarin fasa auren Nusrah zaâa bayar, Shiysa kowanne su bai wani
bada full attention ba,
Da maganar fasa bikin Nusrah aka fara, sannan aka fara lissafo marassa aure agidan. Tuni jikin
su Shamie baby ya dâau rawa, dan akwai wani Alhaji mai tumbi ga shegen muni a legas da ya
kafe kan lalle ita yake so, ita kuma bata son shi, amma ya nace sai ya aure ta, don baba ma (Ya
Bala) har fada yai mata, Kan lalle ta dinga saurarar sa, shi mijinka bakasan wanene shi ba,
babu kyau wulaqanta mutane, jikin ta sai rawa yake yi, Shikenan ita kam tata ta bushe, duk tulin
shekarun data âdauka tana dakon soyayyar Shamsudden (Dan Ya Bala)a ranta yanzu shikenan
ta tashi a banza kenan? Ai batasan sanda zancen zucin yafito fili ba, cikin zunduma uban ihu
tace,
âWayyo shikenan ni Shamie Baby, tawa ta âkare, Alhaji Tulu(wai dan yanada uban tumbi) ka
cuce ni, Innalillahi waâinna ilaihir rajiâun na kadâeâ
Duk sai kallo ya koma kanta, Islam ta gimtse dariar data taho mata, Nan Saifullahi ya juya yana
kallon ta, hadâa ido sukai ya zabga mata harara, Ya Bala dake gefe ya dubi Shemaâu yana
murmushi, shi duk ya gano abunda yasa ta zauce haka, duk dan akan âAlhaji Lawwali Mai Nera
neâ, danne dariar sa yai yana zare mata idanu,
âLapia Shemaâu?â
Saurin rufe baki tayi, ganin katobâarar da tayi, murya na rawa tace,
âBa komai Baba, da zucia ta nake.â
Daria falon ya âdauka dashi, banda Nusrah da Saifullahi wanda gaba dâaya kowanne da abunda
zuciar sa take sakayo masa,
âToh ki cewa zuciar taki, ta baki nutsuwa tayi hakâuri, mu âkarasa, sai ku cigaba da ganawa idan
muka gama ko?â
Cewar Dr Khaleel don akwai shi da barakwanci, dukkansu ma haka suke har Ya Bala. Kada kai
Shemaâu tayi tana kukan zuci. Ciki harda tsinewa Alhaji Tulu da takeyi.
Gyaren murya Ya Bala yayi, duban su yake dukka ahalin nasu. Yasan Kowanne da abunda
zuciar sa ke ayyana masa, âdan sosa hanci yayi yana kurbar ruwa, yafara da basmala kafin
yace,
âSai abu na biyu, wanda ni da mahaifiyar mu da âyan uwana muka yanke, wanda duk duniya
indai ba Allah ne yayi hakan baxai faru ba, to babu mahalukin daya isa ya sa a fasa wallahi, da
farko dai. Kai Mudasser da Muâutaseer su waye kukace kunaso anema muku auren su?â
Suka kalli juna, cike da kunya Mudasser yace,
âBaba ni wata âkanwar wadda muke aiki a company din kace, wannan staff din naka yâar nijar?
To kanwar ta nake nema âRamaâ tana can nijar, amma idan tazo hutu muna hadu wa,â
Kadâa kai Ya Bala yayi, alamun ya gamsu, Muâutaseer yace,
âBaba ni kuma, âkawar su Marwa ce, wata yarinya âMiss Hafsyâ tana karantar agricultureâ
âMadallah..Duk zaâa nemo muku auren su da yardar Allah, amma sai na fara bincike, a yau
âdinnan ba sai wani lokacin ba.â
âMungode Babaâ suka hada baki suna fadar haka.
Ruwa Ya Bala ya sake kwankwada, yana duban Kamaludden, da cikin sa ya hautsine ganin irin
kallon da Baban ke masa. Gyaran murya ya sakeyi yana nuna Kamaludden da yatsa,
âKai kuma kamalu, ga âkanwar ka nan na hadaku aure da ita, daga yau ku fara fuskantar junaâ
Duk yan matan parlorn sukai tsuru-tsuru, musanman su Hidaya. Murya na rawa Kamaluddeen
yake cewa,
âBa..Baba wa kake nufi wai?â
âWa kuwa? bayan kai da Aysha gata nan kusa da kai,â
Sanyi Aysa taji aranta, amma bata nuna ba, Shemaâu wani kuka ne taji ya taso mata, take, ta
dinga jero adduâoi harda tashiga bandaki.
âShikenan Baba..Na karba Allah ya sa albarkaâ cewar Kamaludden, bawai dan yana son hakan
ba, kawai dai sai dan bin zabâin iyayeâ
âAllah ya muku albarka..â
âAmeenâaisha tafada tana wani sussunne kai, da alama yâar banzar ta fara kunyar Ya Bala,
wayaga uban miji hehe.
âKai kuma Shamsuddenâ cewar Ya Bala, sai kuma ya tsaya yana saka wayar sa a silent ganin
irin âkarar da masu kira suka ishesa.
A razane Shamsudden ya dago yana kallon Ya Bala, sai kuma ya mayar âkasa yana kukan zuci,
ganin da girman su ana sadakar dasu, a auren dole.
âYawwa Shamsudden, Kai kuma na hadâaka aure da Shemaâu..â
Babu kunya Shemaâu tayi sujjadar godia ga Allah, tana riko kafar Ya Bala, sumbatu take tayi,
daâdi kasheta,
âBaba,Nagode! Allah ya saka da alkhairi.â Cewar Shemaâu.
Daria aka kwashe da ita, Banda wanda aka hadâa auren dole, su waâenann kukan zuci suke.
âShikenan Baba, Godia muke.â
Shamsudden ya fadâa ko ajikin sa, domin ya âkudiri niyyar anayin biki ba da jimawa ba, zai âkara
wani auren son ransa, tunda ita Shemaâun zabâin iyayen sa ce.
âAmeen.Allah ya muku albarka.. Sai abu na âkâarshe, Nusrah!â
Dago kai tayi a razane tana kallon Ya Bala, ba ita kadai ba du yan parlorn kallon sa suke yi,
musanman Yafendo da ta gwalalo idanuwa tana jiran jin wanne hukunci zaâa yanke akan tata
âyar. Dakyar ta iya furta,
âNaâam Uncle Bâ
âYâar albarka kenan, Kiyi hakâuri da âkaddarar data faru akan ki, kan auran ki da Aliyu, Kuma ki
sani ba xamu tabâa miki zabâin da ba nagari ba, kamar yadda âyan uwanki kowannen su ya
yadda kada ki bamu kunya, bayan baki isa ko wani naki ya hana ba ma..â
Shiru yai yana duban yan parlorn, Sosai yake hadâe ransa don yasan yanzu xaâa kwashi
ruguntsumi. A hankali Nusrah ta furta,
âToh..Uncle Bâ
âYawwa! kai saifullahi ,na hadâa auren ka da Nusrah, sai ku fara fuskantar juna,â
A razane Saifullah ya dâaga kai yana kallon mahaifin sa, sosai ko a mafarki bai taba xaton haka
xata faru ba, yarinyar da ya tsana, ya rena âkirarta, wata sadâoâdo da ita, domin shi mutum ne
mai muguwar shaâawa, kuma yafison dirarriyar mace, komai yaji ishasshe, Islam ce tafadâo
masa arai, yasan ba sonta yake ba, amma tabbas yana shaâawar yarinyar, koâina cikakke ne a
jikin ta, komai nata yayi mai. Ya juya yana kallon Islam, kansa ya sauka akan âkirjin ta da yake
mugun tafiya dashi. Dakyar ya iya janye kansa yana saukar dashi âkasa.
âKo bakuji bane,