Showing 45001 words to 48000 words out of 86718 words

Chapter 16 - SAIFUL-ISLAM Book Complete by miss xoxo (2).pdf

06 Jul 2025

2082

Bala ba, domin cutawa zai tayi. Wasu textbooks ya ‘dauka dama dansu yazo. A
tare suka fita, driver yajashi zuwa airport, ita kuma ta tukasu zuwa Kano itada Sidiya. Sam ko a
mafarki Karimatu bata kawo komai ba. Haka suka shiga kano, a hanya ta tsaya ta siyi biredi na
dari uku da lemon ‘bawo na dari biyu wai zata kaiwa Hajia, siyayyar ‘dari biyar dai cif acikin
dubu ‘dari da aka bata. Suna ta hira suka ‘karasa cikin unguwar yakasai.

Ranta taji gaba d’aya ya baci. Sam batason unguwar su yanzu, ballantana gidan su. Wani yaro
ne rike da mangwaro a hannunsa yana sha, ruwan sai zirara yake a rigar sa, bako wando
ajikinsa, majina sai yar tsere suke a fuskar sa. Kyakkyawan rankwashi Karimatu ta bashi akai
kafin tace,
“Tafi gida, ‘dan kan uba, kai yaran unguwar nan ‘kaxamai ne wallahi”

Sidiya dake gefe tayi daria,

“Yaya ‘dan zulfa’u ne fa (‘kanwar Karimatu da auren ta ya mutu).

Ashar Karimatu ta lailayo tana duban sa, rike haba tayi, cikin mamaki tace.

“Wallahi kuwa ga nason bakin nan irin na ubansa haladu mai kayan koli.”

Sidiya dai darawa take tayi, a Haka suka shiga cikin gidan. Gaban Karimatu sai faduwa yakeyi,
domin ta tsani gidan nasu, dan ‘kukut dashi ga shegen ‘doyin masai data cika, take barazanar
‘burmawa. Duk sai ‘kaurin icen da mahaifiyar su ke alalar siyarwa. Gefe ta zauna tana rufe
hancinta. Kallo d’aya hajian tayi musu tana ‘dauke kanta, domin Karimatu idan ba aikin asirin
tane ya kawo taba, bata zuwa ganin gidah, ko kuwa mai xai faru sai dai ayi ba ita. Shiysa a
dangi ake cewa batason shiga harkar dangi saboda ba masu kudi bane. Tana zaune ‘kannenta
suka fara zuwa suna gaidata, wasu tafadi sunan su, wasu ta amsa da kai kawai. Sai data mulaa
ta huta don kanta sannan ta mike tana nufar hanyar kitchen, a tsaye yadda take ba rissinawa

bare girmamawa tace,

“Hajia ina yini?”

“Da ban wuni ba kya ganni Ina alala?”

“To fah.. Alhaji yana gaida ki.”

“Nagode masa, yaron kirki”

Biredin da lemon ‘bawon takai gaban hajiar tana wani tabe baki,

“Hajia ga tsarabar Bauchi.”

Bin ledar Hajia tayi da kallo,biredi mai yanka-yanka (slice bread) guda d’aya sai lemon da baifi
kwaya goma ba. Murmushi kawai Hajian tayi, tana gyara xaman kular da take juye alalar, zind’e
Karimatu tayi, kafin ta koma ‘dakin da take sauka ta zauna a kan wata yarkacacciyar tabarma,
cikin ‘daga murya tace,
“Alawiyya..”

Da azama Alawiyyan ta ‘karaso dakin tana haki, Don tasan irin rashin mutuncin Yayar tasu,
kowa bata bari ba, domin kwanaki da tazo, ita suna waje suna hira da saurayin ta, Karimatun ta
lek’a ta bashi ‘dari biyu ya karbo mata awara, ya siyo kyauta ya bata, ta sake cewa ya koma da
dari biyun ya siyo mata balangu a y’ar kasuwa. Tun daga ranar bai ‘kara zuwa ba.
“Aunty gani..”

“Ungo rik’e.. Ki je gidan asabe mai abinci, ki siyomin shinkafa da taliya ta dari uku, da
hakarkarin kaza na ‘dari biyar. Yawwa da lemo mai sanyi guda biyu da ruwan roba. Kiyi sauri
yunwa nakeji.”

Cike da azama Alawiyya ta mike tatafi, tana tafe tana ‘korafi. Gand’amemiyar budurwa da ita,
amma kullum idan Aunty tazo saita uzzurawa rayuwar ta. Tana tafe tana kukan zuci haka ta
‘karasa gidan ta siyo ta kai mata, ba ko godia Karimatu ta karba tashiga narkawa cikin ta. Sai da
tai nak sannan ta mimmike tana hutawa. Nan Sidiya tashiga tana mata sannu,
“Yawwa.. kaiwa Kawu takardar nan, da alama kudi ya tambaye shi, aita zubarmin da kima dai”
cewar Karimatu tana mikawa Sidiya takardar da yace abawa Kawu.

Karba Sidiya tai tana murmushi,

“Bari Yaya, ai wallahi sam banajin dad’in yadda ake zubar miki da mutuncin ki wallahi. Zamu

kamo bakin zaren dai.”

“bar ‘dan nema kawai, mamugunci idan nasa ‘yayan ne ai bazai musu haka ba.”

Ita dai Sidiya saka kai tayi ta fita, bayan ta kunna Karimatu dake ta faman mita tamkar zata
amayo kayan cikin ta, duk ‘yan gidan sun tsakure kowa a tsorace yake da ita. Hajja ce kawai
dai-dai ita, Don sam bata raga mata. Sidiya na kaiwa Kawu ya karba, sai da yaga tatafi sannan
ya bude ya fara karantawa, don dama ya masa bayani a waya da ya je airport. Karantawa yayi
yana jinjina kai kawai. Dama yasan za’ai haka, domin duk wanda baya ganin ‘kimar iyayen sa
bazai ga da kyau ba. Mahaifinta na kan gadon asitbiti ba lapia ya nemi da tazo yaganta, taki
zuwa wai haka kawai ba zata kwashi cuta ba. Sai da yarasu da kwanaki uku sannan tazo. Sai
bayan sallar isha’i yaje gidan, kallo d’aya yai mata ya ‘dauke kansa. Gaysawa sukai da Hajia,
aka kawo masa dadduma ya zauna akai, sai da yaran suka gaggayshe, sannan Karimatu ta
‘dan daga murya tana,

“Ina wuni..”

“Lapia lou.” Ya amsa yana cewa da Hajia,

“Gurin ki fa nazo, zamu ‘danyi magana ne.”

Zaure suka koma suka zauna, Karimatu ta tun tsire da daria tana fadin,

“dole ka sammata ai, sarkin ‘yan kwadayi. Wannan mutumi badan ance ‘kanin uba na bane,
bazan yadda ba.”

Hajia kuwa, Kawu na gama gaya mata yadda akayi tasa hawaye, Allah sarki uwa. Kai Allah ya
shiwa iyayenmu albarka, ya biya musu bukatan su, Allah yasa aljannatul frdaus makoma ce
agare su. Kawu ya shiga bata baki. Dakyar tayi shiru tana goge hawayen dake neman zubo
mata, cikin tausayawa tace,
“Yanzu Amadu abunda Karime tayi ta kyauta kenan? Dubi yadda yaran nan yake mana abun
arziki, gidan nan fa shiya siya mana da haya muke, cinmu shan mu duk ya ‘dauke yana kokarta
mana. Shekaran jia fa ya turawa Dauda kudin makaranta. Amma yarinyar nan sai da tasa
hakurin ta ya ‘kare ya rabu da ita? Shin ko yammata da zawaran gidan nan basu isheta ishara
ba? Mu bakwai duk kanmu d’aya, gata ta takwas ta kashe aure, na shiga uku ni Salamatu”

“Kiyi hak’uri Hajia, wallahi karime halin ta sai ita, mutumin nan yanada mugun hak’uri duk
yadda akai bango ta kaishi, wallahi bakiga hakurin da yake bani ba a waya. Idan kinji abunda
tayiyyi masa zaki mamaki, da wani ne da tuni ya rabu da ita, ta sanyawa uwargidan sa da
amaryar ido ta hanasu xaman lapia, sihiri da sharri kala-kala, ni wallahi duk sai kunya ta
mamayeni.”

Tsaki Hajia tayi tana rakfa uban tagumi. Kafin tace,

“Ita ba’a auren aka aure ta?, ko kuwa nan gidan ni kadai ta tashi taga Ina rayuwa ba tare da
kishiyoyi ba?, Dan Allah yayi ma bamasu zama bane, ko kuwa kaf dangin mu kafadamin banda
Nura waye baida mata fiye da uku?. Ai ga gidan nan gata, kuma wallahi sai dai ta koma gidan
ka, bade nan ba. Bazan zauna suna kaso aure suna takurawa rayuwata ba.”
Girgiza kai Kawu yayi, cikin sauri yace.

“Ba dai gida na ba Hajia, taje can wani wajen tayi zawarcin ta wallahi, duk k’ok’arin da nake
mata bata gani, duk zagin da takemin yana zuwa kunnena, ai ita nan can d’aya sokuwar
batasan abunda ke faruwa ba. Catai bakida lapia, Don ya tambayeni ya jikin ki? Nace toh da
sauki Alhamdulillah.”
“Allah ya shrya.. Allah ya kyauta, tunda rayuwar da ta zabawa kanta kenan sai tazo ta zauna ai,
shashasha, sakarai kawai. Babbar banza, babbar wofi.”

“Kiyi hak’uri Hajia, ta ta ‘kaddarar kenan.”

“Kaddara? Wannan sakaci ne da shirka, ai ga hukuncin nan, ta fara fuskanta tun a dunia.”

Haka dai Kawu ya shiga bata baki. Ya kuma sanya aka kira masa Karimatu, Hajia ta mike
tabasu waje tana goge hawayen ta, ita kadai take kalla taji dadi, Don ita ce kawai mai aure, duk
sauran yaran basuyi aure ba, uku daga ciki kuma zawarawa ne gata taxama cikon ta hudu.
Kawu na sanarwa Karimatu, ta saki wata ‘kara mai razanarwa. Take ta yanke jiki ta sume. Kanta
‘yan gidan suka yi, suna tambayar ba’asi, Kawu ya sheda musu. Sidiya ta sulale tabar gidan,
dama ita y’ar kanwar Hajian ce. Tatafi yada auren Karime ya mutu a unguwa.

*DUTSE*

Zaune Yafendo take tana yanke farce, ba laifi ta’dan kara kiba akan da, domin tayi ciwo sosai,
bayan komawarta dutse. Dr Khaleel ya shiga bakinsa ‘dauke da sallama. Gaisawa sukai , kafin
ta jere masa abinci a dining, serving dinshi tayi tana zaune a kujera mai kallon sa, wayar shi tai
‘kara, ‘dauka yayi yana karawa a kunnen sa,
“Assalamu Alaikum.. oh! Na’am Kawu. Bakomi, ni zan baku hak’uri. Allah ya bata wani daya
fini..”

Nan jii da ganin Yafendo suka ‘dauke, dakyar ta iya furta,

“Alhaji kai da wa kuka rabu?”

“Karimatu”

yafada yana danna lomar abinci a baka. Ji kake ‘s...iiiit’, ‘birrr, ‘bubur.. bot’ Yafendo tashiga
sakin iska ba ‘kak’kautawa, tana sakin tusa tana magiya,

“Alhaji.. Ni dai dan Allah karka rabu dani, wallahi na kintsu yanzu, Allah ba ruwana da kowa...”
‘Birrrr’

Ta ‘karasa maganar tana sakin wata bahaguwar tusa mai shegen ‘doyi, mikewa yayi yana
yakice hannunta data rike nasa, cikin dauriya yace,

“Sakar ni Amina. Da me zanji yanzu? Da shegiyar tusar ki mai doyi ko kuwa hannun ki da ke
dauke da shawarma sauce duk jin shafamin.. ni sake ni dan Allah.. kiyiwa Allah ki cikani, wallahi
bakiji ciki na ba.” Yafada hannunsa toshe da hancinsa,

Dakyar Yafendo ta sake shi tana,

“Alhaji kakka rabu dani ni, dai dan Allah,”

Can ‘k’arshen parlor ya koma yana fifita hancin sa da murfin flask. Dakyar yace,

“Bodara kawai, ki rage shan madara wallahi da kayan kwadayi, ki guji nacin cin starchy food.
Ko kiga likita, Gaskia ba lapia ba, gashi ke ko ajikin ki.”

Tashi tai zata biyoshi biyoshi yai hanzarin dakatar da ita,

“Ki bari ta huce wallahi. Zan mugun sab’a miki idan kikazo nan Amina. Can anjima ki hadomin
coffee ki kawomin.”

Yana gama fada ya shiga ‘daki ya murza key. Ita kuwa safa da marwa tashiga yi a parlorn. Sam
nutsuwarta bata jikin ta, gani take kawai saura nata takaddar sakin. Cikin kidimewa tashiga
kamo addu’oi tana yi, ciki harda ta hawa abun hawa.


.....

_Masu neman SAIFUL_ISLAM daga farko kuje blog dina na nanahafsat.wordpress.com, dan
bana posting a wattpadd.. wattpaddians hiyam sorry zaku iya wantsalawa fans grp na
SAIFUL_ISLAM, don samu daga farko_

https://chat.whatsapp.com/FCICopl029LGkPU2TmA5ov


_HML FIDDAUSI SODANGIMAY ALLAH BLESS UR NEW HOME._

_WRITTEN BY THE ELOQUENT WRITER:MISS XOXO_
[1/3, 10:53 PM] Miss Xoxo: *_SAIFUL_ISLAM...*_


*_NA*_


_*©NANA HAFSAAT*_
*_(MISS XOXO)*_


® *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_Home of experts and perfects writers)_


*_SADAUKARWA GA:*_
_ASY KHALEEL_


*_TUKWICI NE GARE KU:*_
_YA HAJJAH CE_
_BILLYN ABDUL_


*_SHAFI NA 37-39_*

_WANNAN SHAFIN NA KINE, MASOYIYAR ‘KWARAI, NANA HAFSATU NA GODIA DA
YADDA KIKE BIBIYAR LITTATTAFANTA, DA MA ITA KANTA *~Halymah saminu El-jibrin*_
_ THANKS FOR THE HERBAL REMEDY_

_nanahafsat.wordpress.com_

Yafendo ta kasa hak’uri, sai da takira Inna Bilkisu ta zayyane mata komai, tareda ‘doriyar tasa
baki, kan dan Allah kada Dr Khaleel itama ya bata takardar sakin ta, a daren kuwa Inna Bilkisu
ta kira Dr Khaleel tashiga balbaleshi da fad’a, ta inda take shiga batanan take fita ba. Hak’uri ya
shiga bata tareda d’oriyar,
“Inna ba zaki gane bane, wallahi nayi hak’uri sosai da matar nan, taki ji, taki ta shiryu, babu
abunda ya ragu a halayenta saima dad’uwa. Zama da irin su Karimatu inda tamkar annoba ce,

dan bakiji abubuwan da suke fad’a zasu aikata bane itada wannan y’ar uwar tata Sidiya, Kinga
fa har kashedi na mata akanta amma tak’i. Shiysa bazan iya wani hakurin su cutar da baiwar
Allah da ahalin taba, hak’uri na ya kare. Kiyi hak’uri Inna.”

Shiru kawai Inna tayi tana sauraransa, Tabbas duk abunda yafada, Karimatu zata iya aikata fiye
da hakanma, kuma yanke hukuncin dr Khaleel lokaci d’aya , lalle babban abune, dan baya tab’a
zartar da hukunci saida shawarar manyan sa. Cikin dattako tace,

“Shikenan! Allah yasa hakanne yafi alkhairi, Allah ya maka albarka. Ita kuma Allah yasa hakan
ya zamto silar shiryuwarta, Allah ya ‘kara kareku da kariyar sa...”

Haka tashiga yi masa addu’oi da kalamai na kwantar da zucia, har saida ta tabbatar komai ya
wuce, sannan sukai sallama. Fada sosai ya shiga yiwa Yafendo saida ya mata tatas tukun
sannan ya ji sanyi a ransa, dakinsa ya koma ya cigaba da nazarin wani littafi da yakeyi, domin a
satin gaba ne, za’a bashi shedar farfesa. (professorial title).
Karimatu kuwa na a asibiti, da kudin da ta karba na ‘karyar hajia ba lapia, zata bawa malaminta
ladan aiki, dashi aka kaita asibiti, sam takasa motsa ko‘ina na jikin ta, hawaye ne kawai ke
gangara daga fuskar ta. Lokaci d’aya ta ‘kanjame kamar wadda ta shekara tana ciwo. Dakyar
Hajia takira Hafsat da sauran yaran tace suzo mahaifiyar su ba lapia. Da niyyar idan sunzo ta
sanar musu auren tama ya mutu.

*ABUJA*

Shirye-shiryen tafia Nile University suke yi, inda za’a bawa Dr Khaleel matakin Farfesa(prof).
Duk ‘yan uwa na nesa dana kusa sunje Abujan. Kowa ya kintsa cikin shigar sa, suka ‘dunguma
a zungureriyar motar da aka tanada musu, ta kai su Nile. Anyi addu’oi aka fara da abunda taron
zai ‘kunsa, daga nan kuma aka kira Dr Khaleel , da za’a bashi farfesa na ‘bangaren psychology.
Tafi aka fara yi kowa daka ganshi kasan yana cikin farin ciki.

Can gefe kuwa Khaled da Saifullah ne, cikin tawagar mutanen, kallo d’aya zakai wa saifullah
kasan takura masa akai yaje. Sai kumbure fuska yake yi, baturiyar mai magana wato Mrs Brown
ta ‘kara kiran Dr Khaleel tana,

“May I please call on stage, our amiable man of honor, Dr Khaleel Muhammad Tasi’u...”

Cikin isa da takunsa na dattako ya ‘kara stage din, bakin sa ‘dauke da murmushi, sai yanzu
Saifullah ya tabbatar dagaske ‘dan uwan mak’ocinsu ne na legas(Ya Bala) domin suna kama,
sai dai wancan yafi manyanta. A take professors suka yo kansa, kowanne saida yayi bayanin
hazakar Dr Khaleel, kafin a rataya masa professorial gown da hula, da wani yadi dake ‘dauke
da tambarin professor of psychology, da wasu littattafai, tukun sannan akai announcing ‘dinsa
da zama cikakken farfesa, aka kuma fadi matakinsa tun daga kan Bsc, Msc, Misd, Mnia, Phd.
Sannan Professor a yanzu.

Gaskia an gwangwaje, kuma anyi farin ciki, Inna Bilkisu kuwa hawayen farin ciki ne ke reto a
fuskar ta. Wai yau Khaleel ‘dinta ne ke tsaye cikin dubban mutane ana ‘kara masa
girma/matsayi a ilimi. Anyi hotuna sosai, an ci kuma ansha anan, kafin a koma gidah kuma ayi
wata walimar da Haj Aysa ta shirya. Riri kuwa dadi kasheta hango Khaled datayi, bude baki tayi
ganin harda wannan arrogant saifullah din makocinsu dake lagos. Tabe baki tayi tana mamakin
dama yana shiga mutane haka.

Saifullah kuwa jan hannun Khaled yake tayi, yana marai-raice masa su tafi gidah wai time ‘din
karatun sa ne, Khaled ya tuntsire da daria yana kwace hannunsa,

“Wallahi bazan tafi ba, haka kawai me xanje nayi a gida?, kai ungo Key dinma kaja motar kaje
da kanka.”

Yana fada ya zaro mukullin motar ya mika masa, ‘kin karba Saifullah yayi yana wani langabar
da kai, nan Riri da Islam suka doso su suna tahowa, sanye Islam take cikin laffaya, orange
color. Ba kadan ba tayi kyau, gashi laffayar ta kwanta a jikinta, duk coca-cola shape dinta ya
bayyana, Riri kuwa sanye take cikin Kimono ta ‘daura ‘dankwali kalar rigar, sai karairaya jiki take
tunda ta hango Khaled, itacema ta ishi Islam suje wajen su, Don ita batasan yazo bama.
Saifullah kuwa gaba d’aya nazarin Islam yake, mace har mace amma take cewa tanason namiji,
Tarasa wane namijin ma sai Khaled. Tsaki ya saki yana kauda kansa gefe, Ganin Riri, sarai
yasan yarinyar nan a legas batajin magana, saboda unguwar su d’aya, ta tab’a shiga rayuwar
sa ya shek’a mata mari.

“Yaya..”

cewar Islam tana washewa Khaled baki. Murmushi ya saki yana sake binta da kallo, tayi masa
kyau kwarai,

“Mi lady.. Kin fito sak kanuri babe. You look breathtaking..”

Saifullah dake gefe ya saki tsaki, yana,

“Bani car key din, I’m going”

Sarai Khaled ya gano dan yace wa Islam hakane, yarasa mai yasa saifullah ya tsani harkar
mata gaba d’aya. Sai asannan Islam ta hango Saifullah, cikin murmushi tace,

“Ah... Sai., Ya saif!”

Juyawa yai yana kallon ta, idanun sa suka sauka akan ‘dan bakinta dayasha jambaki, cikin
dakewa cikeda basarwa yace,

“Sannu ko..”

Mamaki ya cikata, gyada kai kawai tayi, yayi wucewar sa mota ya figeta a guje. Khaled baiji
dad’in yadda Saifullah yaiwa Islam ba,

“Kin sanshi ne?” Cewar KHaled

“Yeah.. Muna haduwa idan na fita jogging. To anan ya gayamun sunan sa”

“Just., ignore the fool. So ya school sissy?”

“Alhamdulillah Yaya. Ya naku baka tafi ba kuma”

“Eh wallahi, sun hanani visa suna ta renamin hankali, Baba kuma yaki saka baki. So kawai na
hakura, zan bari muyi aure da madam sai mu wuce can gaba d’aya, itama ta fara karatun acan.”

Islam ta bude baki kenan zatai magana, Riri dake gefe takasa hak’uri, cikin kissa tace,

“Yaya.. Ina yini?”

“Ah lapia lou Fareedah. Ya garin?”

“Alhamdulillah,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login