Showing 1 words to 3000 words out of 88489 words

Chapter 1 - SHAGALALLIYA COMPLETE HAUSA NOVELS BY Hadiza D Auta.docx

18 Dec 2025

2049

*SHAGALALLIYA!*

*HADIZA D/AUTA*

*DEDICATE TO HANNAH SUHANA*

*Free book kuma Labarin barkwanci.*

*LAMBA TA FARKO.*

Aguje ta isa dandalin matasan ta tsaya a kansu dafe da ƙirji tana haki, yayin da take so ta yi magana amma ta kasa tsabar gudun da ta sha. Dukansu suka bi ta da kallo cike da mamaki a kan fuskokinsu, suna jiran su ji abin da ya kawo ta, saboda sanin halinta. Musamman Mani da ya kasa ɗauke idanuwansa a kanta, masu ɗauke da ƙatuwar hararar da ƙiris ya rage ya kai mata hannu, saboda bai raba ɗaya biyu a kan cewa wurin sa ta zo. Ganin hakin ya ƙi barin ta ta faɗi zaune daɓas a cikin ƙasa tana rabon ido cikin rarraba magana da haɗiyar yawu ta ce masa,

"Ka..kawu Mani, inji Kandala..wai.. wai ta ce na kira ka asiri rufe ka je ka ci kwaɗon garin kwakin da ta..."

A zabure ya miƙe tsaye yana wurga mata daƙuwa kafin ya riƙe ƙugu cikin fusata ya ce,

"Wai ke wace irin tonanniyar yarinya ce ke? To don ubanki ki je ki ce mata ba na ci na ƙoshi!"



"An gama kwaɗon yanzu yanzun nan! Kuma ai kai ka ce idan an yi a sanar da kai tun kafin ya yi ruwa ya lalac..."

Cikinta ya yi kamar zai kai mata duka, ta yi hanzarin dunƙulewa wuri guda tana ihu, haushi ya saka shi shura talkamansa zuciyarsa cike da takaici ya bar wurin. Saboda tonon sililin da ta yi masa a cikin abokan hirarsa. Hannuwansa zube a cikin aljihunsa ya sha kwana ko waige babu tsabar shaƙiyancin da abokan suke ta yi masa, a kan idan ba ya cin kwaɗon ya kawo musu tun kafin ya lalace. Amma hakan bai hana ta ɗaga murya ta sake cewa ba,

"Ɗumamen da ka ce a rage maka ma yana tukunya!"

Babu shiri wasu daga cikin abokan nasa suka fara dariya, yayin da wani daga cikinsu ya kalle ta a lalace ya ce,

"Ke kam Bintoto an yi watsatsiya! Shi kenan ba za ki iya rufa masa asirin ba, duk da jan kunnen da aka yi miki a kan ki kira shi asiri rufen?"

Ta miƙe tsaye tana turo baki ta shiga kakkaɓe zaninta da ya kwaso ƙasa tana cewa,

"To ai na faɗa masa asiri rufe ko kai ba ka ji me na ce ba?"

Ta ƙare maganar tare da murguɗa baki, zaburar da ya yi da nufin kai mata duka ya sa ta bazama da gudu tana faɗin,

"Allah Ya isana idan ƙato ya dake ni."

Ya bi ta da kalolin zagi tana yi masa gwalo. Sai da ta sha kwanar da za ta sada ta da gida ta zaro dogon kare a cikin karan da ke ƙofar wani gida, sannan ta fara yin mota da shi tana gudu tana faɗin,

"Ziiiiiiiiiih! Ba burki ba burki! Duk wanda na kaɗe yasin babu ruwana!"

Haka take ta zuba gudu da dogon karen tana nanacin babu burki har ta ci karo da wani yaro da ke ɗauke da bokitin awara a kansa, wanda fitowarsa kenan daga gida zuwa wurin talla. Babu aune sai jin ƙarar faɗuwar bokitin tare da tulin awararsa da ke cike fam ko rufuwa ba ya yi. Babu jinkiri awara ta watse gabaɗaya ta baje cikin ƙasa. Yaro ya dafe kai yana tsalle tare da ihun faɗin,

"Wayyo ni awarata! Wallahi na rantse da Allah sai an biya ni awarata!"

Kafin ka ce me mutane sun fara taruwa wurin suna tambayar mafari. Bintoto ta rike ƙugu tana kallon awarar da ke watse cikin ƙasa tana huci tare da zaro ido ta ce,

"Kam buhun uban nan kai! Me kake nufi ne? Lalle ma ni ce zan biya ka awarar? Lalle ma yaro!"

Abin da ya faɗa ya harzuƙa yaron ya yi kanta cikin zafin nama ya ruƙunƙume ta yana ihun faɗin sai ta biya shi awararsa. Ta shiga kokawar ƙwatar kanta cikin fushi tana faɗin,

"Tun farko ba sai da na faɗa maka motar babu burki ba ka ƙi ji? To ai yanzu sai na ga uban da zai sa a biya ka awarar!"

Nan take dambe ya sarƙe a tsakanin Bintoto da mai awara, mutane suka yi dafifi ana ƙoƙarin raba su suna ƙin bari, har sai da wani dattijo ya nemo kare ya fara kai musu duka, sannan suka daina yunƙurin sake yin wani damben. Daga nan aka fara tambayar ba'asin mafarin rikicin, da aka gano Bintoton ce ba ta da gaskiya kai tsaye aka kwashe sauran awarar da ta rage. Saboda tuni yara sun daka mata wawa sun cinye mara ƙasa sai kaɗan aka bari.

Ƙeyarta aka tasa sai gidansu da bokitin awarar, tare da mai awarar da ke gaba yana rantsuwar ko da bala'i sai ta biya shi kuɗin awararsa.

Ɗanɗano.

Daga Alƙalamin D/Auta✍🏻

*SHAGALALLIYA!*

*HADIZA D. AUTA*

*Labarin Barkwanci.*

*LAMBA TA BIYU*

https://chat.whatsapp.com/ICmrsyihZBzLrpXfmM7DyQ

Suna zuwa ƙofar gidan ta yi wuf ta faɗa cikin gidan tana faɗin "Wallahi Kandala ƙarya suke yi mini ba ni ce na zubar da awarar b..."

Mutumin da ya raba su faɗan ya bi bayanta da kallo cike da takaici, sannan ya fara rafka sallama wata bayan wata cikin ɗaga murya. Daga can ciki muryar Kandala ta fara tashi tana nufo soron gidan tana zuba faɗa, don tafiya take yi tana gyara zanin da ke ɗaure ƙugunta har cin tuntuɓe tana faɗin,

"Sai na ga wanda zai saka ni biyan awarar tun da an ce da ku kuɗin banza gare ni! Haka kawai a dinga ɗora wa yarinya jarfa kullum ba za a bar ta ta huta ba sai an ce ga abin da ta aikata? To ahir ɗin ku Wallahi Allah kurwar Bintotona kur take a kanku duk sharar da kuka zuba mata sai na kakkaɓe ta! Don haka gane za ku gan ta don ta Allah ba taku ba billahillazi. Awara kuma sai na ga wanda zai saka ni biyan ta a kaf faɗin garin nan na Maidala! Tun da sharri ake yi mata ta ce ba ta san ta zubar ba."

Ta ƙare maganar tare da kwance ƙullin goronta da ke gefen kallabi ta gutsura, sannan ta mayar da shi a gefen zaninta ta ɗaure shi ta sake sokewa a jikinta. Ta shiga taunar goron tana ƙarewa kowa kallo ɗaya bayan ɗaya alamun ko daidai take da zamanin wanda ya ce cas.

Mutumin da ya jagoranci zuwan baki a sake ya dinga kallon ta kafin ya yi magana cikin tausasa murya ya ce,

"Inna kin ga yaron da ta zubar wa awara, ni zan wuce ne na ga suna rigimar shi ne na raba su. Sannan kin ga bokitin fa gabaɗaya ta zubar masa da kaya, saboda Allah hakan da ta yi kin ga ta kyauta?"

Ya ƙare maganar tare da nuna mata cikin bokitin awarar, in da sauran da ta rage ita ma ta nashe da ƙasa. Kandala ta bi bokitin da kallo a lalace sannan ta yatsina fuska ta ce,

"Ta ina ko zan ga rashin kyautawarta tun da ba a gabana aka yi ba?"

Sannan ta juya gefenta ta riƙo hannun Bintoto da ke raɓe jikinta tana muzurai, ta fito da ita gaban mutumin ta sake cewa,

"Fito tsakiya ki tsaya tsaf ki yi bayanin abin da ya faru, tun da dai ba kashe ki za a yi ba don kin zubar da awara."

Bintoto ta fito gabanta ta tsaya tana muzurai tana hararar yaron sama da ƙasa sannan ta turo baki ta ce,

"Kin san Allah Inna; idan har ni ce na zubar kwarankwatsa dubu ta faɗo a kan Malam Idi. Kuma idan har ni ce na zubar ba sharri suka yi mini ba; wallahi Allah Kandala na yarda aradu ta faɗo miki duk lokacin da aka yi hadari Kandala. Saboda ban ma gan shi ba, amma ya ce ni na zubar masa da awara don yana so a ce ni na yi wannan ta'asar. Kuma fa Innarsa ce ba ya so ta dake shi shi ne ya ce ni ce..sannan ai ke ma kin sani ba zan aikata ba ko Kandala?"

Ta ƙare maganar tana langaɓe kai ta koma alamun tausayi cike da son Kandala ta amince da zancenta. Amma maimakon ta yi nasara a kai sai Mutumin ya tari numfashin Kandalar da cewa,

"Ki faɗi tsakaninki da Allah Bintoto ba ke ce kike tuƙa motar kare kika kaɗe shi ya zubar ba?"

Kowa ya zuba mata ido a lokacin da ta shiga rantse-rantsen ba ita ce ta zubar ba, amma zancenta na ƙarshe da ta dire ya tona gaskiyar ƙaryar da take ƙoƙarin kartawa domin ta wanke kanta. Saboda kallon da ta ga ana yi mata ya sa ta fashe da kuka cikin maganar tana cewa,

"Sai da na ce masa babu birki amma ya tsaya motar ta kaɗe masa awara. Kuma tun da ba ni ba ce ai ya je wurin karen da ya yi aikin sai ya biya sh...Wallahi Kandala shi ne ya ƙi janyew..."

Mugun kallon da ta wurga mata haɗe da dundu a baya ya sa ta fasa ƙara tare da barin wurin da gudu ta yi cikin gida tana zagin mai awarar, tare da jera masa kalolin ba ta yafe ba tun da ya ta sa aka dake ta a banza.

Jikin Kandala yana tsima ta fara kumfar bakin faɗin, "In dai kuɗin awarar da kika zubar ne ko nawa ne zan biya shi tun da ba da tsiya na zo duniya ba. Kuma ko gobe kika zubar zan biya ai Allah ba azzalumin Sarki ba ne ba."

Sanin halinta ya sa Mutumin ya yi tsaye sai da aka ƙididdige awarar da ke cikin bokitin sannan aka haɗa kan kuɗin da wadda ya ce an yi masa lissafi gida tun kafin ya fito. A nan Kandala ta yi tsalle ta dire a kan cewa ba za ta biya shi kuɗin duka ba, sai dai a ware wadda ke cikin bokitin ya je ya wanke tun da shi ma da laifinsa.

Da lallami da ban-baki Kandala ta biya kuɗin awarar tana masifa sannan taron ya watse. Bayan ta gama dungure wa mai awara kai a kan duk ya kuskura ya bari ta sake zubar masa da kaya babu ruwanta.

Ta juya cikin gidan tana balbala faɗa tare da ƙwala wa Bintoton kira a kan ta ɗauko asusunta a fashe ta cire kuɗinta don ba kyauta ta biya mata ba. Bintoto da ke bayi ta sha jinin jikinta ko motsi ta kasa yi. Saboda sanin idan ta fito za ta iya dukan ta, hakan ya sa duk kiran da take yi mata bai sa ta yi motsin kirki ba. Sai da ta ji ta nufo bayin tana faɗa bayan ta gama bincike ta ko'ina cikin gidan ba ta gan ta ba.

Tsul Bintoto ta kama guntuwar katangar tasu ta dira ta bayan gidan daidai lokacin da Kandala ta faɗo bayin.

"Wayyo Allahna!"

Abin da ta faɗa kenan a lokacin da ta faɗi ƙasa ƙugunta ya daki dutse tsabar tsoron ta kama ta. Kandala ta leƙo kanta tana faɗin,

"Fitinanniyar yarinya! Ko ki dawo gida ki kawo asusunki na ɗauki kuɗina; ko kuma na tattara miki kayanki ki koma gidan Ubanki."

Bintoto ta miƙe riƙe da ƙugu ta fara ɗingisa ƙafafuwa tana yi tana waigen Kandala da ke tsaye katangar tana faɗa. Tare da yi mata kashedin kada ta je ko'ina ta dawo gida sai ta biya ta kuɗinta. Amma hakan bai hana ta tsallake gidan ta faɗa wani gida ba.

Kandala ta fito bayin ta shiga neman asusun lungu da saƙon ɗakinta. Saboda ba ta san inda ta ɓoye shi ba, domin duk lokacin da ta saka kuɗinta canza masa wurin ajiya take yi. Cikin sa'a ta ga asusun ta fito da shi tsakar gida tana cigaba da faɗan, kai-tsaye ta fasa shi ta haɗa kan kuɗin sannan ta cire nata ta naɗe mata canjinta a gefen ɗankwali. Zuciyarta cike da tunanin borin da za ta yi a lokacin da ta ga asusun nata a fashe, hakan ya sa ta tanadi dogon kare sannan ta zauna zaman jiran dawowarta.



Ga mai buƙatar group ɗina ga link



Domin samun littafin a kan lokaci kuma babu jira ya biya 1k ya same shi a Telegram. 1230094555 Access Bank Hadiza D Auta Ibrahim. Shaidar biya ta wannan layin: 08022014771.

D. Auta ce✍️

*SHAGALALLIYA!*

*HADIZA D. AUTA*

*DEDICATED TO HANNAH SUHANA*

*LAMBA TA UKU*

https://chat.whatsapp.com/ICmrsyihZBzLrpXfmM7DyQ

Haka Kandala ta yi ta mita har zuwa yamma, inda take ta zuba idon dawowar Bintoton amman shiru kamar an shuka dusa. Dole ta saɓa zaninta ta yafa ta fita zuwa neman ta gida-gida, sai dai duk inda ta je ce mata ake yi ta zo amma ta fita, ko kukma a ce mata ba ta je ba. A jigace ta dawo gida tana sababin faɗa tare da cin alwashin irin dukan da za ta saka kawunta Mani ya yi mata idan har ta yi nasarar kama ta.

Sai dai abin da ba ta sani ba tun lokacin da za ta je wani gidan da ke maƙotaka da su; wasu yara suka shiga gidan da gudu suka sanar da ita ga Kandala nan zuwa, cikin rawar jiki ta miƙe daga wasar ƙasar da suke yi ta yi soron gidan ta ɓoye bayan ƙyaure sannan ta sha jinin jikinta. Kasancewar soron da duhu hakan ya sa har ta wuce ba ta san da ita a saƙon ɓoye ba, sai dai tana ganin Kandalar ta shige gidan da bambamin faɗa ta fito aguje ta yi gida. A miliyan ta faɗa ɗakin Kulu ta shige ƙarƙashin gado tana sauke numfashin wahala.

Leƙo kanta ta yi daga cikin ƙarƙashin gadon tana sauke numfashin kamar ta shiɗe ta ce wa Kulun,

"Don Allah Kulu idan ta zo nema na ki ce ba ki gan ni ba."

Kulu da ke zaune tana ƙullin kukar miyar da take siyarwa; wani kallon raini ta fara yi mata sannan ta samun damar cewa,

"Wallahi ni kam ba za ki saka ni yi wa Inna ƙarya ba, haka kawai ki sa ta zo ta saka ni gaba da faɗa ina zaman zamana lafiya. Don haka sawunki a likkafa ki fito, saboda duk ta tambaye ni wallahi sai na faɗa mata gaskiya ba za ki saka ni yin ƙarya ba."

Bintoto daga can ƙarƙashin gadon ta murguɗa mata baki sannan ta ce,

"Ni ko na rantse da Allah sai na kashe miki ɗiyan kaji duk kika tona mini asiri."

Babu shiri Kulu ta kafe ta da ido a lokacin da take ƙoƙarin ƙulle wata ledar kukar da ke hannunta, kai-tsaye ta ajiye ledar ta fasa ƙullewar cikin masifa ta nufo bakin gadon gadan-gadan don daman cike take da kalolin rashin kunyar da take yi mata, a zafafe ta duƙa ta janyo ta ƙii iya ƙarfinta tana faɗin,

"Fitar mini daga ɗaki marar kunyar banza fitsararriya!"

Bintoto ta ƙara komawa tare manne jikinta riƙe ƙarafunan gadon ta ƙarƙashin gadon tana faɗin,

"Ai na rantse da Allah ba zan taɓa fita ba tun da ba daga gidanku kika zo da ɗakin ba!"

Ita ko Kulu ta nace a kan dole sai ta fitar mata ɗaki ko kuma ta jibge ta, da haka rigima ta kacame a tsakaninsu har Kulu ta ci nasarar fito da ita ta ƙarfin tsiya, saboda ƙarfi ba ɗaya don ta girme ta sosai ƙarfin hali ne kawai ɓarawo da sallama.

Ai ko fitowar Bintoto ke da wuya ta yi cikin Kulu da duka kamar wata mai ƙarfin gaske. Kulu ma ta cire tsoron Kandala ta saki jiki ta dinga jibgar ta iya ƙarfinta tamkar an ba ta umarni. Wuya ta sa Bintoto ta fara ihu tare da kiran sunan Kandala a haukace tana faɗin ta yi sauri ta zo Kulu za ta kashe ta. Amma ganin Kandalar ba ta zo ba kuma ba za ta iya da ita ba; hakan ya sa ta ratumi ƙwaryar kukar Kula ta juye mata kukar duka a jikinta, tun daga fuskarta har tsakiyar ɗakin duka kukar ta barbaɗe, sannan wadda ta ƙulla ita ma ta dinga farfashe ledodin tana zubarwa a tsakar ɗakin tana faɗin,

"Ni za ki daka? B ni kika daka a banza ba! To wallahi na rama ni ma!"

Tsabar baƙinciki da takaici ya sa Kulu tsayuwa riƙe da ƙugu tana kallon ta'adin da take yi mata baki a sake. Cike da mugun jin haushin ɓarnar da ta yi mata bayan asara; Kulu ta bi ta da kallo ranta a matuƙar ɓace ta yi kanta tamkar wata zakanya, cikin matsanancin fushi ta fisgo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login