Showing 3001 words to 6000 words out of 88489 words

Chapter 2 - SHAGALALLIYA COMPLETE HAUSA NOVELS BY Hadiza D Auta.docx

18 Dec 2025

2052

Bintoto sai jin ƙarar rugujewar kwanonin jeren ɗakin Kulu Kandala ta jiyo rifff. Wadda shigowarta gidan ke nan daga yawon neman Bintoton ranta a ɓace tana wassafa irin dukan da za ta yi mata idan ta riƙa ta.

Gabaɗaya kwanonin da aka yi wa Kulu jere da su duk sun zubo musu a jiki, don ko da Kandala ta shigo ɗakin ta tarar da Kulu saman Bintoto a tsakiyar kwananin ta taushe ta tana ta kai mata kalolin duka inda ranta ya yi mata daɗi. Ita ko sai ihun neman ceto take saboda har da kwanonin Kulu take haɗawa wajen hushe haushin ta ga Bintoton.

Babu zato ta ji muryar Kandala a saman kanta tana salati, hakan ya sa ta yi saurin zabura ta ɗaga Bintoton da ke ta kuka iya ƙarfinta tana faman kiran sunan Kandala ta zo za a kashe ta.

A firgice ta miƙe ta yi wurin Kandala tana ihun wayyo Kulu ta karya mata hannu, Kandala kam saboda mamakin irin abin da Kulu ta aikata mata ko motsin kirki kasa yi ta yi, sai da ta ga Bintoto da hannu a sage tana ihu sannan ta dawo natsuwarta. Cikin ruɗewa ta kalli Kulu a masifance ta ce,

"Allah ya toni asirinki munafuka! Ashe daman maganar da Bintoto take faɗa mini kullum a kanki gaskiya ce? To Wallahi bari Mani ya zo kin gama zama cikin gidan nan baƙar almura mara imani... ke tun kafin ya zo ma maza ɗauki mayafinki ki bar mana gida tun da babu kuɗinki cikin ginin shi. Sannan ni Kandala uwar Mani daga yau na haramta miki zama cikinsa ki je na kore ki kuma na sake ki saki uku ringis ƙwarara. Gayyar na ayya gayyar tsiya wadda kakanki har ya bar duniya ko likkafanin da za a saka masa sai da aka bashi sadakarsa tsabar tsiya irin ta zuri'arku. Bayan ficika bai bar wa ubanki gado ba, haka ya bar shi yana watangaririya a cikin gari da riga guda ƙyalau-ƙyalau kullum rai da rai kamar fatar dabbobi."

Kulu ta fashe da kuka tana ba ta haƙuri amma Kandala ta kafe dole sai ta bar gidan, dole ta ja mayafinta ta fice tana kuka iya ƙarfinta. Bayan fitarta gidan Kandala ta dawo da kallon ta ga Bintoto hankali a tashe ta riƙo ta suka fito gidan tana ihu da kuwwar wayyo Kulu ta karya mata hannu.

Ba ta zame da ita ko'ina ba sai gidan mai ɗori, da ƙyar da walahaula aka gyara wa Bintoto hannun don Kulu ta goce ta, sannan suka dawo gida ta shinfiɗa mata tabarma ta kwanta sai nishi take yi tana sharar ƙwallah. Kandala tana mata fifita tare da jera mata sannu tana mita har ta samu ta yi bacci, sannan hankalinta ya kwanta ta dawo jimamin kuɗin da Bintoton ta sa ta kashe a wunin ranar don ta sani ficika ba za ta yi ciwon kai ba a cikin kuɗinta da ke asusu. Saboda har ta sayi wani sabo ta mayar mata da kuɗin kamar yadda ta gan su.

Tana zaune tana tsine wa Kulu a ranta, don daman can bala'in haushin kulun take ji, saboda yadda take cin zalin Bintoton a duk lokacin da ta fakaici idonta.

Sallamar Hari ce ta katse mata zancen zucin da ta ke yi, cikin sauri ta washe baki tana yi mata lale marhaban, saboda ba ƙaramin girmama Harin ake yi ba a cikin garin nasu na Maidala.

Shin wace ce Hari?

1k ne kacal ku mori laratunku babu jira. 1230094555 Access Bank Hadiza D Auta. Shaidar biya ta wannan lambar: 08022014771.

D. Auta ce.✍️

*SHAGALALLIYA*

*HADIZA D. AUTA.*

*LAMBA TA HUƊU.*

Jikin Kandala yana rawa ta miƙe da nufin kawo mata sabuwar tabarma, amman Hari ta nufi wata kujera 'yar tsugunno ta dawo wajen da su Kandalar suke ta ajiye ta zauna, sannan ta ce da Kandala da ke ƙoƙarin shigewa ɗaki da nufin ɗauko tamarma ta ce,

"Ki dawo kawai Inna Kandala ai na samu abin zama."

Kandala ta waigo tana washe baki ta ce,

"Da dai kin bari na kawo miki tabarmar ta fi kujerar daɗin zama, ko ba komoi kya miƙe ƙafa ki sarara ga shi kin kwaso hanya."

Hari tana dariya ta ce, "Babu komai Inna, dawo abin ki ai nan ma ya yi mini, da ma can gaishe ki kawai na zo yi sauri nake yi, saboda ana nema na a can birnin."

Kandala ta dawo tana wasar baki ta ce, "Ai kin kyauta, gara da kika biyo a yi zumunci, ko banza Hausawa sun ce a rabu a gana arziƙi ne."

Hari ta washe baki tana cewa, "Haka ne Inna, ai ya zama dole gare ni na zo gaishe ki ko don ki yi mini addu'ar da kika saba."

Tana gama maganar ta kai kallonta ga Bintoto da ke barci ta sake cewa,

"Bintoto lafiya ko? Na ga tana barci da wannan yammacin haka Inna. Ko dai ciwo ta ji ban da labari? Na ga hannunta da sabon ɗauri.

Kandala ta dawo inda take farko ta zauna, sannan ta ɗauki mafefeci ta ci gaba da yi wa Bintoto fifita sannan ta ce,

"Kin san 'yar taku da rashin jinta Hari, to yau ma garin jan maganarta ne ta jayo matar Mani saura ƙiris ta nakasa ta a banza, don dai Allah bai nufa ba kuma ya ya tsare abin ya tsaya a gocewar hannu, kin gan ta nan; yanzu muka dawo daga wurin mai ɗorin, ta sha kuka kamar babu gobe."

Hari ta ɓata fuska cikin damuwa ta ce, "Ni na rasa wa Bintoto ta gado da wannan rawar kan nata, don kowa ya san daga Habi har Buba babu wanda yake da hayaniya a cikin su, amman ita kullum daga wannan sai wancan?"

Kandala ta goge guntuwar ƙwallarta da ta taru gefen idonta sannan ta ce,

"A kan rashin jinta yau har jikka uku da rabi ta sa na salwantar, ga shi sallah ta ƙarato duk tarin kuɗin da nake yi, ina yi ne kawai a kan ɗinkin da nake so na ɗinka mata ta fito kamar kowa, amman yanzu ta jawo kuɗin sun samu mugun giɓi, ban kuma san har yaushe zan sake tara wasu kuɗin ba."

Hari ta yi shiru na ɗan lokaci tana nazari sannan ta ce,

"Wai Inna ko dai za ki ba da ita na kai ta birni ta yi aikatau? Kin ga idan ta dinga aikin za ta samo muku abin da za ku dinga ɓatarwa ke ma ki huta faɗi-tashin da kike yi. Don a ganina gara aikin ya fi, da wannan yawon ɗaukar maganar da take yi miki a cikin gari."

Kandala ta yi saurin girgiza kai tana faɗin, "Ina! Ina! Daina faɗa Hari, ai ke ma kin san ba zan iya rabuwa da Bintoto ba, saboda ita nake kallo a madadin Habi idan na rasa ta kusa da ni ban san wane irin hali zan shiga ba. Don haka gara ɗaukar maganar da a ta yi mini nisa ba zan iya ba gaskiy...."

Nan take Kandala ta fashe da kuka wiwi har da fyace majina da gunjin kuka. hankalin Hari ya tashi ta fara roƙon ta a kan don Allah ta yi haƙuri ta daina kukan, saboda girman abin bai kai yadda ta ɗauke shi ba. Saboda kukan nata Bintoto ta tashi daga barcin da take yi, ta miƙe zumbur saboda ta manta da tana da wani ciwo a jikinta, ai kuwa sai ga ta da komawa ta kwanta babu shiri tare da fasa wata uwar ƙara tana faɗin,

"Wayyo hannunta!"

Kandala ta ja ta jikinta tana ci gaba da kukanta tamkar wadda aka ce a ranar za a raba su, da ƙyar Hari ta shawo kanta ta daina kukan, sannan ta dinga ba ta baki a kan ta yi haƙuri da maganar da ta yi mata, don da a ce ta san har haka ranta zai ɓaci da tun farko ba ta yi mata ba, cikin sanyin jiki Harin ta ciro kuɗi ta ajiye a gaban Bintoto sannan ta miƙe tana yi musu sallamar tafiya, cikin rashin sukuni suka rabu ko rakiya babu.

Hari ta fita zuciyarta cike da alhinin rabuwa da ƙawarta Habi mahaifiyar Bintoto, wadda suka taso tare tun suna 'yan yara, kafin mutuwa ta yi musu katangar ƙarfen da ta shata layi a tsakaninsu. Sannan Habin ita ce auta a wurin Kandala, kuma ita ce ɗiyar da ta fi so a cikin 'ya'yanta, garin haihuwar Bintoto Allah ya yi mata rasuwa, hakan ya sa ta damƙe Bintoto a hannunta ko ƙuda ba ta so ya taɓa ta.

Sannan kuma ta ɗauki son duniya ta ɗora a Bintoto, don ko shayar da ita da ƙyar ta bari 'yarta Jimmala ta shayar da ita, wadda ta zamo yaya ga mahaifiyar Bintoton, ana yaye ta ta karɓe ta ta dawo hannunta, tun daga lokacin hidimarta ta koma kanta, don a yadda take ji ko ubanta bai isa da ita ba ganin yadda take da matsayi a wurin ta. Dole ya zuba mata ido ya bar ta da ita, tsakaninsa da su ranar da ta ga damar kai masa ita ta ya gan ta, tun tana ƙarama har girmanta ya kawo kai.

Fitar Hari ya bai wa Kandala damar ƙyalla ido ta hango 'yan dubu-dubu da Harin ta ajiye mata a kan gefen tabarma, babu shiri ta share hawayenta ta kai wa kuɗin wawura, Bintoto ma ta yi saurin damƙe kuɗin da hannunta mai lafiya, saboda sanin idan suka shiga hannun Kandala babu rabonta. Ai kuwa Kandala ba ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ƙoƙarin ɓanɓare kuɗin a hannunta tana cije baki tana faɗin,

"Ai wallahi yau ƙwandala ba za ki ci a cikin kuɗin nan ba, tun da har kika jawo na yi asarar ƙudina a banza a wofi garin rashin mutuncin da kika saba."

Bintoto ta damƙe kuɗin iya ƙarfinta ita ma Kandala ba ta daina son ƙwace kuɗin ba, ganin ba za ta iya ɓanɓare kuɗin ba ta soka mata haƙorinta na gaba, wanda ya bindiro waje ko ta rufe bakin shi ba zai yiwu ya rufe ruf ba, babu shiri Bintoto ta saki kuɗin tana yarfa hannu tare da faɗin,

"Wayyo Kandala! Yanzu a kan kuɗi za ki huda mini hannu da haƙorinki mai wuƙa??"

Kandala tana haɗa kan kuɗin cikin sauri ta ce,

,"Ko mashi haƙorin nawa ya koma ba zan ji shayin soka miki shi ba a kan kuɗin nan, ballantana haƙorin da ko ko kaifi bai da shi amma kin kira shi da sunan wuƙa. To ba wuƙa ba ne zarto ne don malfar ubanki."

Bintoto tana ci gaba da yarfa hannun ta ɓata fuska ta ce,

"Ai da a ce zamanin yaƙi muke yanzu da wallahi ko shi zai yi jahadi wajen kashe miyagun arna, don tsaf zai iya komawa takobi ya kai sara ba tare da an tantance ba."

Wata muguwar dariya Kandala ta fashe da ita tare da buɗa gefen zanenta ta ƙulle ƙudin ta tsuke tsukut, sannan ta soke zanenta a jiki ta ɗauki mafefecin ta ci gaba da yi mata fifitar tana faɗin,

"Yanzu dai duk abin da za ki ce ki faɗa daidai kike. Ni dai kuɗi na haɗe musu kai na soke a jikina, idan kin isa ki tashi ki ƙwata mu gani."

Bintoto za ta yi magana kenan sai ga Kulu ta yi sallama ta shigo gidan, jiki a sanyaye ta nufo su gabanta yana faɗuwa, tana zuwa ta duƙa tana share hawayen ta ce,

"Inna, don Allah ki yi haƙuri wallahi ba da son raina na daki Bintoto ba. Tsautsayi ne da sharrin shaiɗan."

Kandala ta watsa mata wata muguwar harara sannan ta ce,

"Ai kuma tun da na riga da na sake ki to ki sani kin saku yarinya, abin da ya rage kawai ki kwashi tsommakaran haukarki ki koma gidanku, aure ya riga ya ƙare babu fashin barin gidan, ke da Mani haita-haita tun da kika dakar mini Bintoto. Don ko Mani ne ya yi mata abin da kika yi mata sai ya san ya aikata, ballantana ke 'yar karan kaɗa miya, ki zauna gidan naku ki ji idan da daɗi. Daga wannan karon Mani ya gama zama da ke, wallahi kin ji na rantse a kan Bintoto ban ƙi na tayar da garin nan ba."

Akafta😛

Na kuɗi ne. 1k kacal ku garzaya Telegram ku more karatunku babu jira. 1230094555 Access Bank Hadiza D Auta Ibrahim. Shaidar biya ta wannan layin: 08022014771.

D/AUTA ce✍🏻

*SHAGALALLIYA*

*HADIZA D. AUTA*

*LAMBA TA BIYAR*

Kulu ta sake fashewa da kuka tana yi wa Kandala magiya a kan ta yi haƙuri ba za ta sake ba, amma hakan bai sa ta karya mata zuciya ba, ba illa ɗaga kai da ta yi sama tana kumbura hanci alamun magiyarta ko a jikinta. Ana cikin hakan sai ga Mani ya shigo ransa a ɓace saboda ya samu labarin Kandala ta kori kulun, takaici ya saka shi zuwa har gidansu ya roƙi iyayenta ta dawo ɗakinta. Saboda ya tabbatar musu shi bai saki matarsa ba, kuma yana son zama da ita.

Wannan dalilin ya sa ya ƙi biyo ta ya ce ta fara zuwa, ko da ya shigo gidan kallo ɗaya ya yi musu ya kawar da kai, don bai bi ta kansu ba ya nufi ɗakin Kulun kansa tsaye, Kandala ta bi shi da kallo cike da mamaki sannan ta ƙwala masa kira tana cewa,

"Ban gane ba Mani! Wai an yi yamma da kare, shin kana nufin ba za ka zo ka duba Bintoto a kan aika-aikar da matarka ta yi mata ba ne ko me kake nufi?"

Ba tare da ya juyo ba yana haɗe rai ya ce,

"Allah ya ba ta lafiya! Amma ni ban saki Kulu ba kada ta sake fita ko'ina ban amince b..."

Yana maganar ya shige ɗaki, Kandala ta riƙe baki tana juya zancensa a ranta, sannan ta ajiye mafefecin da ke hannunta ta miƙe jikinta yana rawa ta bi shi har ɗakin Kulun, labule ta ɗage ranta a ɓace ta ce masa,

"Kana nufin haushi na ka ji don na kori matarka?"

Mani bai ce da ita ƙanzil ba, hakan ya sa ta sake magana a harzuƙe, "To ai tun da ka ce ba ka sake ta ba to ta dawo ta zauna, amman ka sani babu hannuna babu ƙafata da lamarinku balllantana wani abu da zai shafe ku dukanku kai da ita! Kuma wallahil'azimi a kan Bintoto zan iya bar muku gidan nan sai ku cinye shi kai da ita! Tun da ka nuna ka fi son ta a kan ɗiyar ƙanwarka uwa ɗaya uba, kuma wadda ka saki nono ta kama."

Tana gama faɗar hakan ranta a ɓace ta saki labulen ta bar wurin, kai-tsaye ƙofarta ta nufa duk da magiyar da Kulun take yi ba ta kula ba, sai ma buta da ta ɗauka ta yi bayi saboda kiraye-kirayen sallar magaribar da aka fara yi a lokacin.

Amma har ta fito bayin ta gama arwalar ta shige ɗaki bakin Kulu bai yi shiru da ban haƙurin ba. Sai da ta fara sallah ita ma ta je ta yi arwallar ta yi nata ɗakin sum-sum. Bintoto da ke kwance tana bin su da kallo ta bi ta da harara tare da murguɗa baki bayan ta yi ƙwafa a ranta ta ce,

'Munafuka! Ai ko haka aka bar ki kin sha wuya bak'ar muguwa, sai shegen baƙin ƙarfi tamkar wata zakanya, idan ban da Allah ya kawo Kandala da shi kenan sai ta ga na mutu za ta kyale ni...ai kuma wallahi sai kin sani don a kan kajinki zan huce haushina...ke duka ma sai na kashe su a gidan nan, ko kuma na yi ta jefa shegu a cikin masai suna mutuwa kowa ma ya huta.'

Gama zancen zucinta ke da wuya ta miƙe ta nufi wajen akurkin kajin Kulu ta jawo ɗiya biyu suna tsuwwa tsui-tsui, amma a haka ta je bayinsu cikin sauri ta jefa su masai, sannan ta rufe masan da murfi ta fito cike da jin daɗin ta yi ramuwar gayya.

Daren ranar suka yi kwanan takaici kowa da ƙuncin da ke damun shi, don Mani da dare sai da ya zo yana ta bai wa Kandala haƙuri amma ta ƙi kula shi, dole ya ƙyale ta ya koma wurin Kulu yana ƙara lurar da ita a kan yadda za ta zauna da Kandala da shalelenta ko don su samu zaman lafiya da su a huta da halinsu.

Haka rayuwa ta ci gaba da shurawa zaman lafiyar gidan ya yi ƙaranci, saboda kullum da sabon rikicin da Bintoto za ta jawo har ta sa a yi gagarumin faɗa a kansa.

Ana cikin hakan ne watarana ta ɗauki tallar goron da take yi idan ta ga dama, don sana'ar Kandala kenan siyar da goro da nono da man shanu, sai dai mafi akasari an fi zuwa gida a saye ba a cika fita zuwa tallar ba. Amma ranar da Bintoto ta yi sha'awar tallar don kanta tana ɗauka ta tafi yawon da ta saba yi da sunan tallar.



Hakan ta faru a ranar, Kandala ta lissafa mata goron a tire

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login