Showing 9001 words to 12000 words out of 88489 words
Chapter 4 - SHAGALALLIYA COMPLETE HAUSA NOVELS BY Hadiza D Auta.docx
ma sai na sake kashe mata wasu, kuma haka zan yi ta yi har sai sun mutu duka mun huta, tun da ita ba za ta iya ɗaure su ba."
Kandala cikin sanyin jiki ta ce
"Ke ko ki daina kashe su, amma ni na ce duk suka sake ci miki abinci ki ɗauki kare ki yi musu dukan tsiya."
Bintoto ta fashe da wata arniyar dariya sannan ta ce, "To kuma idan suka mace fa bayan kuma kin ce na daina kashewa?"
Kandala za ta yi magana kenan ta jiyo muryar Mani a soro zai shigo gidan, ta yi saurin tashi jikinta yana rawa ta faɗa ɗaki har da cin tuntuɓe saura ƙiris ta faɗi tsabar sauri. Bintoto ta yi tsalle ta faɗi kwance tana dariyar ƙeta har lokacin da Mani ya shigo zai wuce, cikin ɗaga murya da tsokana ta ce da shi,
"Kawu Mani ga Kandala can cikin ɗaki tana neman ka."
1230094555 Access Bank Hadiza D Auta Ibrahim. Don ƙarin bayani a taɓo wannan lambar: 08022014771.
Akafta😊
D. AUTA CE✍🏻
*SHAGALALLIYA*
*HADIZA D. AUTA*
*LAMBA BAKWAI.*
Sai da Mani ya bi ta da harara har da ƙwafa sannan ya nufi ƙofar ɗakin Kandala, wadda ke cikin ɗaki tana ƙoƙarin yi wa kuɗin mugun ɓoyo. Da sauri ta fito bayan ta adana ta tsaya bakin ƙofar ɗakin tana faɗin,
"Lafiya na gan ka a nan?"
"Bintoto ta ce kina nema n..."
"Kul...Kulu ce take neman ka tun ɗazu, ka yi tafi ka ji wataƙila kazar da ta dafa take son ba ka."
Mani ya yi tsaye yana ƙumshe dariya, saboda ya gama gano akwai abin da take ɓoyewa wanda ba ta son ya gani, cikin dariya ya fara ƙoƙarin kutsa kansa da niyyar shiga ɗakin yana cewa,
"Akwai fura a ɗakin nan na sha?"
Kandala ta tare ƙofar tana faɗin,
"Je wurin matarka yanzu ta gama dama ta da zafinta."
Mani ya juya yana dariya ya ce,
"Bari dai na je na dawo Inna, wallahi yau aljihuna ƙaf nake ko kuɗin sayen dawar da za a yi tuwo babu a gidan nan."
Kandala ta bi shi da harara sannan ta ce, "Aikin kenan ba ni-ba ni kullum kai ba ka iya wani motsin arziƙi sai na zillo da dogon wuyan a ba ka a ba ka. Sarkin maroƙan duniya ma dole ya shafa maka lafiya a wajen son banza. Wallahi dai ka san ciwon kanka tun kafin lokaci ya ƙure maka, saboda watarana ake wa gudu idan ƙasa ta shafe idona. Don haka tun yanzu ka yi ta kuka tun da kai ba ka san yadda ake juya kwabo ya koma sisi ba."
Dariya kawai Mani ya dinga yi yana sosa kai, ba tare da ya juyo ba ya nufi ɗakin Kulu don ya saba da gorinta a duk lokacin da ya nemi wani abu daga hannunta. Kuma a haka yake shanye duk abin da za ta faɗa masa matuƙar za ta ba shi abin da ya nema. Saboda zuciyarsa a mace take da kallon abin da take da shi da abin da ta samu, shi ya sa yake zaman kashe wando a majalisin hira cikin abokansa masu zaman banza, ba su da aiki sai yi da mutane wane ya samu kaza wane kaza ya rasa.
Kandala ta gama faɗanta da Mani ta juyo kan Bintoto da ke ta ƙumshe dariya, don ta san ta gama tsokano fushin Kandala dole ta kama kanta ko kuma ta saka ta ɗaki ta rufe sai ta yi kuka ta gama jigata sannan ta fito da ita, don da wuya ta dake ta gudun ta illata ta, saboda ba ta iya dukan yaro ba idan ranta ya ɓace sai ta ji masa rauni take jin sanyi.
Cikin ƙufula ta ce mata,
"Idan ma ɓakin surutunki ya jawo ya karbi kuɗin to kin yi wa kanki asarar ɗinkin sallah, kina ji kina gani kowa zai fito da sababbi kayan sallah ban da ke, tun da ke ba a rufin asiri da ke sai kin tona mutane, to ki je ki ce ya zo ga kuɗin ya ƙwata tun da uban wani ya nema mini su! Wallahi ki kiyaye ni ko a cikin kwanan nan na mayar da ke gidan ubanki na huta da halinki."
Tana gama faɗar hakan ta janyo ɗakinta ta rufe da kwaɗo ta fice gidan, Bintoto ta bi ta da wani kallo tana zunɓurar baki wai ita ta ji haushin an zagi Babanta. Ta haɗa kai da gwiwa tana ta mui-mui da baki tana gungunin faɗar duk abin da ya zo bakinta da harare-harare. Daga nan ta ɓingire tana ta barci saboda garin kwakin da ta sha ya saka ta jin daɗin yanayin har da minshari, sai dai ko'ina barcin nata bai je ba ta ji kaji a saman jikinta suna tsuwa.
"Tsui! Tsui! Tsui."
A firgice ta farka tare da kaiwa uwar kajin da ke kusa da ita wani uban duka, a bisa tsautsayi kazar ta zille ita ta naushi ƙasa. Babu shiri ta fasa ƙara saboda hannun da Kulu ta ji mata ciwo ne, Mani da ke fitowa daga ɗakin Kulun ya nufo ta cikin sauri yana tambayar,
"Lafiya? Me aka yi miki kuma yanzu?"
Bintoto ta miƙe tsaye tana kuka riƙe da hannu ta fice gidan ko kallon shi ba ta tsaya yi ba, haushi ya saka shi kai kallonsa ga ƙofar ɗakin Kandala, ganin shi a rufe ya fice yana 'yar dariya don ya san a kansa ta rufe ɗakin ta fice, don ma kada ya fito ya same ta idan ya yi mata magiya ta ba shi kuɗin da ya nema.
Minti goma sha biyar da fitar Bintoto sai ga muryar Kandala tana ta surfa ruwan bala'i da tsine-tsine, tana shiga ba ta zame ko'ina ba sai wurin kara, ta ciro wani ƙaton karen dawa mai bala'in ƙwari ta bi 'yan kajin Kulu da gudu tana duka. Kulu da ke ɗaki ta fito saboda jin kukan kajinta, ganin Kandala da gudu tana dukan kajin ya sa ta sha jinin jikinta, don ta gama gano sun jawo mata wata sabuwar fitinar da take gudu. A ckin rashin sa'a Kandala ta bi uwar kajin da gudu tana duka, sai ga ta da cin tuntuɓe da ƙatuwar tukunyar ƙarfen Kulu, wadda ke cike taf da ƙasari babu zato ta faɗi tim a ƙasa Sannan ƙasarin duka ya fantsama jikinta ya yi mata wanka. Kandala ta fasa wata arniyar ƙara dafe da ƙugunta tana faɗin,
"Wayyo ni Allah wayyo ni kaina! Ke kam Allah ya tsine miki Kulu daga ke har 'yan kajinki, wallahi yau-yau sai sun bar gidan nan ko kuma ke ki bar shi tun da ba gidan Isuhu mai mola ba ne!"
Kulu ta fito daga inda ta rakuɓe ƙirjinta yana bugawa, ganin irin faɗuwar da Kandala ta yi mai haɗe da mugun walle, cikin rawar jiki ta isa wurin tana ƙoƙarin ɗaga ta sama da niyyar taimaka mata ta miƙe, amma babu kunya Kandala ta saka ƙafa ta kai mata harbi a gefen fuskarta, babu zato Kulu ta faɗi daɓas saboda tsabar tsoron Kandalar ya shige ta ganin abubuwan da ke ta faruwa duk a sanadinta.
Da rarrafe Kandala ta miƙe da ƙyar tana faɗin wayyo, dafe da ƙugunta tana jan ƙafafu da jan numfashi ta koma faɗin,
"Dole na koma wurin Ɗantani mai gyaran karaya ni ma ya duba mini ƙuguna, wallahi Mani ka ci amanata da ka auro Kulu ka kawo mana ita a cikin gidan nan! Ke kam Kulu Allah ya wadaranki ya tsine miki albarkar dare da ta safiya. Wallahi na faɗa da babbar murya Kulu ban yafe miki ba! Saboda kin zamo mana fitina ke da tsinannun kajinki, marasa mutunci da rashin imani, kuma 'yan ƙasan wutar jahannama da ta hawiya!"
To fa! A taushi ƙugun Kandala kafin ta kasa tafiya mu shiga uku😂
1230094555 Access Bank Hadiza D. Auta Ibrahim. Shaidar biya ta wannan lambar; 08022014771.
*SHAGALALLIYA!*
*HADIZA D. AUTA*
*LAMBA TAKWAS.*
A haka ta fice gidan tana ɗangishi tare da ƙara tsine wa Kulu da kajin nata. Kulu kam duk da take cikin tsoron abin da zai je ya dawo hakan bai hana ta fito da dariyar da take faman ƙumshewa ba. Musamman idan ta tuno da irin faɗuwar da Kandala ta yi mai haɗe da walle, sannan da kalar harbin da ta kai mata da ƙafa har ta faɗi kamar wata 'yar wresteling. Tuno abin da ke gabanta ya sa ta ta samo buhu cikin sauri ta dinga kama ɗiyan kajin tana sakawa, sannan ta kamo uwarsu ta damƙe a hannu da sassarfa ta fice gidan zuwa gidansu. Da nufin koma can sa zama don ita ma ta gaji da fitina tana so ta huta, saboda masifar da suke jawo mata koyaushe rigima ta tashi cikin gidan a kansu ne ake yi.
Ko da Kandala da Bintoto suka dawo gidan ba ta dawo ba, don da tsaya bayar da labarin fitintinun da kajin suke ja mata. Bintoto ɗauke da hannu Kandala dafe da ƙugu, a haka suka nemi wurin zama kowa da kalar zogin da yake ji .
Zamansu ke da wuya Kulu ta dawo gidan kai-tsaye wajensu ta nufo da nufin yi masu sannu, sannan ta ba da haƙuri duk da ta san ba lalle ne Kangala ta yafe mata ba kamar yadda ta furta. Hakan ya sa tun kafin ta ƙarasa inda suke Bintoto ta fasa wata uwar ƙara tana cewa,
"Kandala ki hana ta zuwa wurin nan wallahi ba na son ganin ta!"
Kandala ta yi saurin kallon Kulu da jar harara tana faɗin, "Kul kada ki ƙaraso wajen nan! Baƙar azzaluma! Ki tafi kawai mun bar ki da Allah, idan muka je lahira a yi mana hisabi da ke a gaban bainar jama'u!"
Kulu ta marairece fuska tana faɗin,
"Don Allah Inna ku yi haƙuri, yanzu haka ma na kwashe kajin gabaɗaya na kai su gidanmu, saboda ni ma ba da son raina suke yin abin da suke yi b.."
Kandala ta buga wani uban tsakin da ya saka Kulu dire maganarta babu shiri, saboda ganin yadda take jujjuya baki tana mayar da shi gefe kafin ta ce,
"Ke dai kawai ki ce watan mutuwarsu ne ya kama, don ko tantama babu yunwa ce za ta yi ajalinsu a gidan naku, tun da ko su masu gidan neman abin da za su ci suke yi, ballantana a samu na bai wa tsinannun kajin."
Cike da bala'in jin haushin Kandala a kan cin zarafin da take yi wa gidansu koyaushe babu alkunya, Kulu ta miƙe tana ɓata fuska cikin gunguni ta ce,
"Ai duk tsiyarmu ba za mu rasa geron da za a watsa musu ba."
Tana maganar tana tafiya Kandala ta bi ta da ƙatuwar harara tana cewa,
"Dawo ki ci gaba da zagin nawa da kika saba tabbatacciya! Ai daman can ina sane da kalolin zagin da kike shigewa ɗaki kina yi mini, to billahillazi muddin kika ci namana a bayan idona kaf zuri'arku sai Allah ya ci banten ubanku! Tun daga kan Ɗan'azumi har zuwa kan Isuhu mola mai hular gado."
Takaicin cin mutuncin da Kandala take yi wa kakanta da Babanta, ya sa ta isa ɗakinta da gudu tana kuka. Bintoto ta fashe da dariya iya ƙarfinta tana faɗin,
"Ai wallahi da ma kin yi kukan jini kin huta, idan jinin ya tsiyaye ki mutu ki bar mana gidan mu wataya mu kaɗai yadda muke so, shikenan mun mun rabu da gaibu!"
Kandala ta buge mata ƙeyar kai cikin sauri ta zuƙe jikinta tana ci gaba da dariyarta, Kandala cikin haɗe fuska ta ce mata,
"Idan ba ki daina tsokanar ta ba kika jawo ta dake ki babu ruwana don ma ki sani tun yanzu. Ni ba na goyon bayan rashin gaskiya, don haka ki bar mu mu ji da iftila'in da ta jaza mana kafin ita ma tsinuwar Allah ta hau kanta."
Sai da Bintoto ta turo baki sannan ta ce, "To Wallahi ni ko ranar da kika ga ta kayar da ni don ban shirya wa damben ba ne, amma yanzu ko da ciwon hannun nan nawa zan iya tumurmushe ta, na yi ta jibgar ta idan ta sake taɓa ni."
Kandala tana kallon ta tana juye baki gefe ta maka mata tana faɗin, "Kurin banza! Ranar ma da ta so kashe ki ai da lafiyarki amma kika saki baki ta dake ki a banza, ballantana yanzu da kika zama musaka hannu yana shirin shanyewa."
Haushin maganganun Kandala ta sa Bintoto ta rungume hannunta mai lafiya ta soke kanta cikin hannun tana gunguni, tare dasharar ƙwalla. Fahimtar ta yi fushi Kandala ta ko ma jan ta zuwa jikinta duk da zamewar da take yi, cikin sigar rarrashi ta shafo kanta tana cewa,
"Ke fa ba ki san wasa ba, to ni wasa ce nake yi miki, ai na san ko ranar don ba ki shirya ba ne shi ya sa ta lungude ki son ranta, amma tabbas da kin shirya da ta sha baƙin mamaki a kan irin ƙarfinki na zaki wanda kike kashe mutane da shi a cikin mafark.... ai kin tuna shi ko?"
A nan Bintoto ta ɗago kai tana washe baki saboda tuno mugun faɗan da ta yi da wasu mutane a cikin mafarki duk ta kashe su. Hakan ya sa ta zabura daga zaunen tana kallon Kandala ta ce,
"Wallahi fa har da wuƙaƙe na yi faɗan Kandala, kuma na yi ta soke mutane ina kashe su suna faɗuwa ƙasa suna mutuwa. To kamar haka nan zan yi wa Kulu a cikin mafarkin ko da safiya za ta yi sai dai a gan ta matacciya."
Kandala ta gimtse dariyarta tana cewa, "To wai su mutanen da kike kashewa a cikin mafarkim Musulmai ne ko Kafurai?"
Bintoto ta yi saurin faɗin, "Ohon musu! Ni dai ko su waye na yi ta kashe su yasin babu abin da ya dame ni tun da suka zo kama ni. Na san su ma idan suka samu sa'a kashe ni za su yi."
Kandala tana dariya ta ce, "Gara dai mu ji idan kafurai ne, saboda muddin aka ce Musulmai ne da kaina zan kai ki kotun Musulunci a yanke miki hukunci irin na masu kisan kai a cikin mafarki, tun kafin kisan naki ya zo kan Kulu ki ja mana bakin mutane."
Bintoto ta ƙyalƙyale da dariya Kandala ma tana taya ta, haka suka ci gaba hirarsu mai cike da shagala tare da barkwancinsu da suka saba yi a tsakaninsu koyaushe.
***
Watanni a tsakanin da rigimar kajin Bintoto ta ji sauƙi, saboda hannun nata yana samun kulawa hakan ya sa ta yi saurin warkewa, sai ɗan abin da ba a rasa ba, wani lokaci ma har tallar goro tana fita. Kandala kuma kwana biyu ne ta yi da ƙugun ya koma daidai. Da ma can buguwa ce kawai babu abin da ya same ta.
Kamar koyaushe, Bintoto tana ɗauke da tiren tallarta tare da ƙawarta Jamila, wadda ita ma tiren tallar ne a kanta za su je cin kasuwar garinsu, suna ta hirarsu a kan hanya. Babu zato suka hango wata dalleliyar mota ta nufo hanyar da suke kai, cike da ƙauyanci suka bi motar da kallo baki a sake har da tsayawa gefen hanya idonsu a kan motar har ta wuce.
A hankali motar ta fara rage gudu tana dawowa baya har ta ƙaraso inda suke tsaye ta tsaya, mamaki cike da fuskokinsu har zuwa lokacin da suka ga mai motar ya zuge gilashin motar tare da leƙo kansa yana faɗin,
"Sannun ku 'yanmata, don Allah ta wace hanya zan bi na je gidan Hakimi?"
Ƙawar Bintoto ta fara yi masa nuni da hannu Bintoto ta yi saurin tsamuke ta a cinya da ƙarfi tana yi mata signal a kan ta yi shiru, sannan bakinta yana rawa ta ce da shi,
"Bari mu zo mu nuna maka hanyar don daga nan akwai tazara sosai da gidan, kwatancen zai yi maka wahalar ganewa. Buɗe mana motar mu shiga sai mu kai ka har gidan da kanmu."
Kasancewarsa babban mutum, kai-tsaye ya gano motar take so su shiga shi ya sa ta tsiro da wayon, yana 'yar dariya ya buɗe musu motar jikin Bintoto yana rawa ta afka ciki, garin rawar jiki sannan da rashin iya shiga motar kafarta da takalmi ta fara ɗorawa ta yi tsalle ta faɗa da ƙarfi, har tiren goron ya buge mata goshi, babu shiri ta kai hannunta saman goshin tana shafawa tana faɗin,
"Wash! Allahna!"
Sannan ta yi saurin gyara zamanta tana leƙo da kanta ta kalli Jamila da ke tsaye tana kallon ta gabaɗaya ta gama tsorata, saboda tana jin fargabar ta shiga a yanke mata kai kamar yadda ta ji labarin ana yi a birni,