Showing 84001 words to 87000 words out of 107295 words

Chapter 29 - MENENE RIBATA BOOK Complete By Ummee Yusuf.txt

18 Nov 2025

1262


๐Ÿ™†๐Ÿ™†๐Ÿ™†


ยฉ *2020*


๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™€

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/





*~โœ๐Ÿฝโœ๐ŸฝGOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONโœ๐Ÿฝโœ๐Ÿฝ~*


*~We are bearer's of so golden pen๐Ÿ–Š~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden penโœ,behold our words.~*
*~A product of our pen๐Ÿ–Š,savour our words, for it will cause you no pain.~*


On the authority of Abu Hurayrah (may Allah be pleased with him), who said: I heard the Messenger of Allah (peace and blessings of Allah be upon him) say:

"The first of people against whom judgment will be pronounced on the Day of Resurrection will be a man who died a martyr. He will be brought and Allah will make known to him His favours and he will recognize them. [The Almighty] will say: 'And what did you do about them?' He will say: 'I fought for You until I died a martyr.' He will say: 'You have lied - you did but fight that it might be said [of you]: 'He is courageous.'' And so it was said. Then he will be ordered to be dragged along on his face until he is cast into Hell-fire. [Another] will be a man who has studied [religious] knowledge and has taught it and who used to recite the Qur'an. He will be brought and Allah will make known to him His favours and he will recognize them. [The Almighty] will say: 'And what did you do about them?' He will say: 'I studied [religious] knowledge and I taught it and I recited the Qur'an for Your sake.' He will say: 'You have lied - you did but study [religious] knowledge that it might be said [of you]: 'He is learned.'' And you recited the Qur'an that it might be said [of you]: 'He is a reciter.' And so it was said. Then he will be ordered to be dragged along on his face until he is cast into Hell-fire. [Another] will be a man whom Allah had made rich and to whom He had given all kinds of wealth. He will be brought and Allah will make known to him His favours and he will recognize them. [The Almighty] will say: 'And what did you do about them?' He will say: 'I left no path [un-trodden] in which You like money to be spent without spending in it for Your sake.' He will say: 'You have lied - you did but do so that it might be said [of you]: 'He is open-handed.'' And so it was said. Then he will be ordered to be dragged along on his face until he is cast into Hell-fire."

[Muslim (also by at-Tirmidhi and an-Nasa'i)]

ุนูŽู†ู’ ุฃูŽุจููŠ ู‡ูุฑูŽูŠู’ุฑูŽุฉูŽ ุฑูŽุถููŠูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุนูŽู†ู’ู‡ูุŒ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ุณูŽู…ูุนู’ุชู ุฑูŽุณููˆู„ูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุตูŽู„ู‘ูŽู‰ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ู ูˆูŽุณูŽู„ู‘ูŽู…ูŽ ูŠูŽู‚ููˆู„ู: ุฅูู†ู‘ูŽ ุฃูŽูˆู‘ูŽู„ูŽ ุงู„ู†ู‘ูŽุงุณู ูŠูู‚ู’ุถูŽู‰ ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ุงู„ู’ู‚ููŠูŽุงู…ูŽุฉู ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ู ุฑูŽุฌูู„ูŒ ุงุณู’ุชูุดู’ู‡ูุฏูŽุŒ ููŽุฃูุชููŠูŽ ุจูู‡ู ููŽุนูŽุฑู‘ูŽููŽู‡ู ู†ูุนูŽู…ูŽู‡ู ููŽุนูŽุฑูŽููŽู‡ูŽุงุŒ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ููŽู…ูŽุง ุนูŽู…ูู„ู’ุชูŽ ูููŠู‡ูŽุงุŸ ู‚ูŽุงู„ูŽ ู‚ูŽุงุชูŽู„ู’ุชู ูููŠูƒูŽ ุญูŽุชู‘ูŽู‰ ุงุณู’ุชูุดู’ู‡ูุฏู’ุชูุŒ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ูƒูŽุฐูŽุจู’ุชูŽุŒ ูˆูŽู„ูŽูƒูู†ู‘ูŽูƒูŽ ู‚ูŽุงุชูŽู„ู’ุชูŽ ู„ูุฃูŽู†ู’ ูŠูู‚ูŽุงู„ูŽ: ุฌูŽุฑููŠุกูŒุŒ ููŽู‚ูŽุฏู’ ู‚ููŠู„ูŽุŒ ุซูู…ู‘ูŽ ุฃูู…ูุฑูŽ ุจูู‡ู ููŽุณูุญูุจูŽ ุนูŽู„ูŽู‰ ูˆูŽุฌู’ู‡ูู‡ู ุญูŽุชู‘ูŽู‰ ุฃูู„ู’ู‚ููŠูŽ ูููŠ ุงู„ู†ู‘ูŽุงุฑู. ูˆูŽุฑูŽุฌูู„ูŒ ุชูŽุนูŽู„ู‘ูŽู…ูŽ ุงู„ู’ุนูู„ู’ู…ูŽ ูˆูŽุนูŽู„ู‘ูŽู…ูŽู‡ู ูˆูŽู‚ูŽุฑูŽุฃูŽ ุงู„ู’ู‚ูุฑู’ุขู†ูŽุŒ ููŽุฃูุชููŠูŽ ุจูู‡ูุŒ ููŽุนูŽุฑู‘ูŽููŽู‡ู ู†ูุนูŽู…ูŽู‡ู ููŽุนูŽุฑูŽููŽู‡ูŽุงุŒ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ููŽู…ูŽุง ุนูŽู…ูู„ู’ุชูŽ ูููŠู‡ูŽุงุŸ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ุชูŽุนูŽู„ู‘ูŽู…ู’ุชู ุงู„ู’ุนูู„ู’ู…ูŽ ูˆูŽุนูŽู„ู‘ูŽู…ู’ุชูู‡ูุŒ ูˆูŽู‚ูŽุฑูŽุฃู’ุชู ูููŠูƒูŽ ุงู„ู’ู‚ูุฑู’ุขู†ูŽุŒ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ูƒูŽุฐูŽุจู’ุชูŽุŒ ูˆูŽู„ูŽูƒูู†ู‘ูŽูƒูŽ ุชูŽุนูŽู„ู‘ูŽู…ู’ุชูŽ ุงู„ู’ุนูู„ู’ู…ูŽ ู„ููŠูู‚ูŽุงู„ูŽ: ุนูŽุงู„ูู…ูŒุŒ ูˆูŽู‚ูŽุฑูŽุฃู’ุชูŽ ุงู„ู’ู‚ูุฑู’ุขู†ูŽ ู„ููŠูู‚ูŽุงู„ูŽ: ู‡ููˆูŽ ู‚ูŽุงุฑูุฆูŒุŒ ููŽู‚ูŽุฏู’ ู‚ููŠู„ูŽุŒ ุซูู…ู‘ูŽ ุฃูู…ูุฑูŽ ุจูู‡ูุŒ ููŽุณูุญูุจูŽ ุนูŽู„ูŽู‰ ูˆูŽุฌู’ู‡ูู‡ู ุญูŽุชู‘ูŽู‰ ุฃูู„ู’ู‚ููŠูŽ ูููŠ ุงู„ู†ู‘ูŽุงุฑู. ูˆูŽุฑูŽุฌูู„ูŒ ูˆูŽุณู‘ูŽุนูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ูุŒ ูˆูŽุฃูŽุนู’ุทูŽุงู‡ู ู…ูู†ู’ ุฃูŽุตู’ู†ูŽุงูู ุงู„ู’ู…ูŽุงู„ู ูƒูู„ู‘ูู‡ูุŒ ููŽุฃูุชููŠูŽ ุจูู‡ูุŒ ููŽุนูŽุฑู‘ูŽููŽู‡ู ู†ูุนูŽู…ูŽู‡ู ููŽุนูŽุฑูŽููŽู‡ูŽุงุŒ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ููŽู…ูŽุง ุนูŽู…ูู„ู’ุชูŽ ูููŠู‡ูŽุงุŸ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ู…ูŽุง ุชูŽุฑูŽูƒู’ุชู ู…ูู†ู’ ุณูŽุจููŠู„ู ุชูุญูุจู‘ู ุฃูŽู†ู’ ูŠูู†ู’ููŽู‚ูŽ ูููŠู‡ูŽุง ุฅูู„ู‘ูŽุง ุฃูŽู†ู’ููŽู‚ู’ุชู ูููŠู‡ูŽุง ู„ูŽูƒูŽุŒ ู‚ูŽุงู„ูŽ: ูƒูŽุฐูŽุจู’ุชูŽุŒ ูˆูŽู„ูŽูƒูู†ู‘ูŽูƒูŽ ููŽุนูŽู„ู’ุชูŽ ู„ููŠูู‚ูŽุงู„ูŽ: ู‡ููˆูŽ ุฌูŽูˆูŽุงุฏูŒุŒ ููŽู‚ูŽุฏู’ ู‚ููŠู„ูŽุŒ ุซูู…ู‘ูŽ ุฃูู…ูุฑูŽ ุจูู‡ู ููŽุณูุญูุจูŽ ุนูŽู„ูŽู‰ ูˆูŽุฌู’ู‡ูู‡ูุŒ ุซูู…ู‘ูŽ ุฃูู„ู’ู‚ููŠูŽ ูููŠ ุงู„ู†ู‘ูŽุงุฑู. ุฑูˆุงู‡ ู…ุณู„ู… (ูˆูƒุฐู„ูƒ ุงู„ุชุฑู…ุฐูŠ ูˆุงู„ู†ุณุงุฆูŠ)




~*WRITTEN BY*~ โ„ข _Golden Pen Writers Association_


~*DAGA ALQALUMAN*~๐Ÿ‘‡๐Ÿป.....โœ

โ™ฆ *Ummee Yusuf* ::--Maman Yusuf, marubuciyar *UMMU SALMA.*

โ™ฆ *Aminatu Hassan* ::-- *0um-Deedat*, marubuciyar *BAN FI KARFIN TA BA.*

โ™ฆ *SUMAIYYA BABAYO ABDULAHI* ::-- *SUMIEE B.*, marubuciyar *AMINTA.*

โ™ฆ *KHADIJA MUHAMMAD* ::-- *0ne luv*, marubuciyar *ฦ˜AREENATEEY.*

โ™ฆ *FATIMA UMAR MODIBBO* ::-- *FATIMA BATULA*, marubuciyar *SAIF KO MALEEK.*

โ™ฆ *BINTU AHMED* ::-- *CYNOSURE* marubuciyar *SHABIHATY (ME KAMA DA Ni).*

~*DEDICATED*~ _To All Victims That Are Related To The Story_

~*WARNING*~ _K'irk'irarren labari ne ba'ayi dancin zarafin wani ko wata ba. Sunayen da suke ciki kama daga na mutane zuwa na gari an k'irk'ire su ne domin fad'akar,ilimintar game da nishad'antar dame karatu, dan haka ba'a yarda wani ko wata ta juya wannan labarin ta kowace siga ba._


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!*



โ™ฃ _Scene Five_

~*Page 24*~

Cikin fushi Salma ta ฦ™araso kusa da Jameela ta fincikota, tace; "wallahi baki isa ba dole ki bar mini miji na, na baki amana shine zaki ha'ince ni?".

Jameela ta taษ“e baki tace; "wannan kuma matsalar ki ne, ke in banda hauka kalar taki taya zaki sami miji kamar wannan amma ki zauna wasa", Salma kuwa babu abinda take banda jijjiga Jameela tana kuka.

Abdulkareem kuwa da yaga abin ba zai ฦ™are ba, da kanshi ya hau raba su, da ฦ™yar ya fincike Jameelar a hannun Salma.

Salma kuwa lokaci guda ta fita hayyacin ta, babu abinda take yi sai kuka idanun ta sam sun rufe faษ—i take; "macuciya Allah ya isa tsakani na dake".

Abdulkareem dai jan hannun Jameela yayi suka fice daga ษ—akin, Fatima da Firdausi wanda hayaniyar su Salmar ya tayar dasu, Fatima ta riฦ™o Salma wacce ke kwance saman tiles tana kuka tace; "Aunty kiyi haฦ™uri".

Salma tace; "Fatima ku tafi ku bani waje, mutane gaba ษ—aya macuta ne basu da amana, Fatima kije nace", dole haka Fatima ta tafi ta barta.

Salma bata tashi daga wajen ba har aka yi kiran sallar asuba, haka ta miฦ™e jikinta babu ฦ™arfi ta shiga bayi tayi alwala ta hau darduma ta fara sallah.

Sai da ta idar sannan ta tashi su firdausi domin suma suyi sallah, kan kujera ta koma ta kwanta tana tariyo rayuwar su ta baya ita da Abdulkareem ษ—in.

Har gari yayi haske sannan su Firdausi suka fito suka shiga kitchen domin haษ—a abiษ“ kari, Salma na kwance tana jinsu amma saboda yadda zuciyar ta da jikinta babu daษ—i yasa ko ษ—ago kai bata yi ta kalle su ba.

Sai da suka gama sannan Fatima tazo ta tsugunna kusa da ita tace; "Aunty Salma mun gama, zamu kawo miki naki ne nan?", Salma tace; "kuci kawai idan zanci zan muku magana", Fatima ta ษ—an yi jimm sannan tace; "shikenan".

Fiddausi ta jera abincin saman tray sannan ta nufi part ษ—in amarya dashi, sai dai me tana zuwa ta samu a kulle dan haka ta bubbuga.

ฦangaren Amarya da Ango kuwa suna zuwa ษ—aki Jameela ta mantar dashi wata Salma haka suka sha love ษ—in su a matsayin su na sababbin amare.

A lokacin da Firdausi ta buga ฦ™ofar suna bayi suna wanka tare, Jameela cikin salon ษ—aukar hankali tace; "Annurin zuciyata bari na duba naga ko waye", da gayya ta saka ฦ™aramin towel ta fito a haka kai a jiฦ™e don ta san Salma ce kuma tana so ta baฦ™antawa Salmar rai.

Sai dai kash! Tana buษ—ewa taga Fiddausi dan haka ta haษ—e rai, Fiddausi kuwa ta ฦ™aฦ™alo murmushi tace; "barka da safiya Amarya dama Aunty ce tace na kawo muku abin kari".

Jameela ta harare ta sannan tace; "kije kice mata bama buฦ™atar abincin ta domin iya abinda na bashi da daddare jiya da wanda ya bani ya ishe mu yinin yau", tana gama fadar haka ta maida ฦ™ofar ta rufe.

Fiddausi ta kama baki tana mamakin halin Amaryar, haka ta maida kayan zuwa ษ—akin Salma wacce bama ta san anyi ba, Fatima tana karyawa taga Fiddausi ta tulin abinci ta dawo.

"meya faru kuma?", Fiddausi ta faษ—awa Fatima duka abinda ya faru, Salma tana jinsu sai dai bata da ishashshiyar lafiyar da zata amsa musu.

Haka suka dinga didimar su har sai da Maman su tayi kiran su akan su koma gida sannan suka tattara kayan su suka tafi.

ฦangaren amarya da ango kuwa bayan ta koma tace; "matar ka ce tazo yi mini gargaษ—i wai kona bar gidan nan ko ta kashe ni", yayi murmushi me ciwo cikin ษ“acin rai yace; "da kuwa na ษ—auki mummunan mataki akanta".

Jameela tayi munafikin murmushi, sai da suka taimakawa juna suka shirya sannan Jameela ta shafa cikin ta tace; "Haskena yunwa nake ji fa".

Yayi ษ—an jim sannan yace; "bari naje na amso a wajen Maman Husna idan ta girka", ba tare da tace komai ba ya juya ya fice.

Da sallama ya shiga ษ—akin, komai a gyare yake fes dashi, Salma tunda ta ษ—ago ta kalle shi ta maida kanta tana rufe idanu, zuciyarta kamar ta tsago ฦ™irjin ta, ta fito haka take ji dama ace zata iya ษ—aukar wuฦ™a ta soka mishi ya mutu kawai kowa ya huta.

Abdulkareem kuwa mamaki yake yi da tunanin sauyin halin Salma wato ko gaisuwa ba zai samu ba, cikin haษ—e fuska yace; "ina abin karin mu".

"Lallai namiji munafiki ne", abinda Salma ta faษ—a kenan a ranta amma a fili tace; "bar girka daku ba", tana faษ—ar haka ta juyar da kanta gefe.

"wai wannan wane kalar hali ne kika ษ—auko Salma kamar kwana biyu kin dena yanzu kuma mugun halin yana so ya dawo?, Salma ni kike wulaฦ™antawa ko, har Jameela zaki je ki yiwa kashedi akan ta bar miki gida idan ba haka ba zaki kashe ta ko? Yanzu ban isa dake ba ko to kiyi duk abinda kike ganin zaki yi sai dai ki sani yadda na ษ—auki wulaฦ™anci a da yanzu ba zan ษ—auka ba domin kuwa da da yanzu da bambamci", yana gama faษ—ar haka ya fice daga ษ—akin.

Salma ta saki kuka wai ko zai sanyaya mata rai akan abinda Abdulkareem ษ—in ya aikata mata, lallai rayuwa kenan.

Yana fita ya koma ya cewa Jameela tayi haฦ™uri ta ษ—ora musu abin kari, cikin kissa tace; "ayya Haskena kada ka damu ni da nazo neman aljanna", yaji daษ—i sosai a da ya san yaji kalan kalaman nan daga wajen Salma sai dai a yanzu da Jameela ta faษ—a sai ya tabbatar da cewa ya cutu na samun rashin kulawa daga matar shi.

Suna gama karyawa jama'a suka fara zarya domin ganin ษ—akin amarya hakan yasa Abdulkareem ficewa daga gidan gabaki ษ—aya.

Salma na kwance zazzaษ“i ya rufe ta kuma tana jiyo zuwan kowa har dangin su Abdulkareem ษ—in amma babu wanda ya leฦ™o yace ci kanki nan fa ta fara zubar da hawaye domin ta san cewa Jameela ta cuceta kuma ta kaita ta baro domin kuwa itace silar da ta dinga yiwa dangin Abdulkareem ษ—in rashin mutunci yanzu gashi sun dena ganin farinta yayin da Jameelar kuma ta sami damar shigewa ฦดan uwan mijin nasu.

Har dare Salma na kwance abinda yake tayar da ita sallah, su Husna ma an dawo dasu gidan amma abin mamaki babu wanda ya shigo inda take.

Haka Salma ta kwanta cikin baฦ™in ciki, domin kuwa yaran ta ma gudun ta suke yi, wannan ya ฦ™ara tayar mata da hankali.

Ta kira yayyin nata tayi musu complain amma kowa cewa yake yi Allah ya ฦ™ara ita ta jawa kanta.

Ranar ma dai Salma bata yi wani barcin kirki ba domin kuwa ga rashin lafiya ga kewar yaran nata da mijin ta haka ta kwana a wahalce.

Da safe kuwa da ฦ™yar take iya buษ—e idanu saboda yadda suka kumbura gashi sunyi jajur dasu, ga wani irin ciwo da kanta yake yi.

Abinda ke ฦ™ara bata mamaki rashin shigowar mijin nata inda take tun jiya da safe da yazo ษ—akin nata karษ“ar abinci be kuma takowa inda take ba.

Haka ranar ma ta wuni a kwance sai dai idan taji yunwa ta janyo flask ษ—in ruwan zafi ta zuba tasha sai kuma sallah.

Kuma yanzu abin ya fara bata tsoro domin kuwa yaran nata sai dai ta jiyo hayaniyar su ษ“angaren Amaryar haka duk wani wanda zai zo wajen ta.

Tana neman me bata shawara a rayuwar ta, duk da ta san meya kamata tayi amma tana buฦ™atar me ษ—ora ta akai, Kuka kam da yana magani da yayiwa Salma har hawayen nata ma da ace suna ฦ™afewa da sun ฦ™afe kuwa tsabar kuka ta rasa inda zata saka rayuwar ta, kwana biyu kenan amma duk ta fige ta lalace.

Washe gari zata amshi girki a hannun Jameela duk da dai amarya ce kuma tun daren farko basu kuma haษ—uwa ba, ita Salma ko ฦ™ofar ษ—akin ta bata fita komai a ษ—aki take yi dan tana da kitchen da bayi a ciki.

Har lokacin bata da wata cikakkiyar lafiya, dan haka babu abinda tayi na gyaran ษ—aki ko kuma girki ko dai wani abin.

A haka Abdul yazo ya same ta, ya baje hanci ya shaฦ™i ฦ™amshin da yanzu Jameela ta sabar mishi amma maimakon haka sai ฦ™ari da yaji domin kuwa har amai yau Salma sai da ta kwara shi.

ya ja tsaki cike da jin haushi, ya kalli yadda ta kwanta can ฦ™uryar gado, ba dan Jameela ta koro shi ba babu abinda zai kawo shi wajen wannan matar wallahi.

Ya ษ—an matsa kusa da ita yace; "Maman Husna", Salma da tun shigowar shi tana kallon shi ta amsa da ฦ™yar yace; "ina abinci na".

Ta ษ—an yi jim sannan tace; "nifa babu abinda na dafa", ya ja dogon tsaki sannan ya fice, wajen Jameela ya koma ya marairaice mata inda ita kuma ta cika mishi ciki da abinci tana ฦ™ara jan shi da fira sai da ya raba dare sannan ya baro ษ—akin nata.

Salma ta kalle shi sannan ta kalli agogo ษ—aya saura, ta koma ta kwanta domin kuwa amai ne ya tada ita, Abdulkareem kuwa cikin alamun rashin gaskiya yace; "tunda baki dafa kin bani ba ai dole ne naje inda za'a bani".

Salma tana jin shi amma ta kanta take yi dan haka bata tsaya bashi amsa ba, haka ya nemi waje ya kwanta.

Wajen ฦ™arfe uku na dare jikin Salma ya ฦ™ara tashi sosai, haka ta miฦ™e cikin jiri amma kan ta kai bayi aman yazo dan haka anan ta tsugunna ta fara kwara shi.

Abdulkareem cikin barci yaji kakarin amai, dan haka ya sauko ganin Salma na amai a wahalce ya ษ—aga hankalin shi sosai ya tallabota har ta gama sannan ya ษ—aga ta ya nufi bayi da ita.

Shi ya taimaka mata ta gyara jikin ta sannan ya kaita saman gadon ya kwantar da ita shi kuma yazo ya gyara wajen da tayi aman.

Koda aka idar da Sallar asuba da wuri Abdulkareem ya dawo daga masallacin yazo ya ษ—auke ta domin tafiya asibiti.

ฦŠakin Jameela ya ฦ™wanฦ™wasa ta buษ—e ฦ™ofa jikinta sanye da hijab wanda ke nuni da sallah ta idar.

"Maman Husna ba ta da lafiya zamu je asibiti", ya faษ—a mata, Jameela tace; "Innalillahi! Meya same ta? Bari na shirya mu kaita tare".

Abdulkareem ya lumshe idanu yana jin daษ—in yadda take nuna tsantsar ฦ™aunar ta ga shi da matar shi da ฦดaฦดan shi duk da ฦ™asan zuciyar shi yana gargaษ—in shi akan Salma ma haka ta nuna da farko.

Jameela data fito daga ษ—akin tayi saurin tallabo Salma tana faษ—in; "Haskena bari na riฦ™e ta", Salma taji wani abu ya caki zuciyar ta.

Haka Jameela ta taimaka mata har suka isa motar Abdulkareem ษ—in ya saka ta a ciki suka fice daga gidan.

Wani asibitin kuษ—i suka je wanda yake kusa, sun sami ฦดan aikin dare basu tafi ba dan haka su suka yi mata duk abinda ya dace.

Da yake asibitin kuษ—i ne kafin gari yayi haske har sun gama mata komai an ษ—aura mata drip ta sami barci ma.

Ganin ฦ™arfe shida da rabi yasa Jameela tace; "Haskena bari naje gida ka san yara na suna da makaranta yau idan na shirya su suka tafi na sama musu abinda zasu ci sai na dawo".

Yace; "muje na kaiki nima sai nayi shirin zuwa wajen aiki, tunda ta sami barci", haka suka miฦ™e suka fice daga ษ—akin.

Salma da duk taji abinda ke faruwa ta girgiza kai hawaye yana biyowa ta idanun ta, ga zafin ciwo ga kuma zafin kishi da kuma karayar zuciya data samu daga ฦ™awar tata kuma aminiyar ta.

Tayi tunanin zasu dawo tare amma koda ta farka Jameela ta samu a zaune, Jameelar tana ganin ta farka tace; "sannu, mun dawo kina barci shine Haskena yaga zai yi latti yace bari kawai ya tafi".

Salma bata ce komai ba banda kauda kai da tayi kawai, Jameela ta taษ“e baki tace; "da kin haฦ™ura kin bini a sannu da nima zan sassauta miki sai dai ki sani duk iya ษ—aga hankalin ki da shige da ficen ki babu wanda zai yi tasiri a kaina dan haka ki kwantar da hankalin ki kawai, Abdulkareem yanzu sai Jameela haka Jameela sai Abdulkareem", tana gama faษ—ar haka ta fice daga ษ—akin.

Salma taja dogon tsaki tana me dangwarar da kofin data ษ—auko domin haษ—a abin kari, lallai dama bahaushe yace mutum mugun ice.

Tana cikin wannan tunanin taga an turo ฦ™ofa an shigo, ta ษ—aga kai tana kallon wacce ta shigo,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login