Showing 39001 words to 42000 words out of 110329 words
Chapter 14 - YARENA ADDININA Book By Jamila Umar Tanko JUT.txt
kanki. Ina zakije ki zauna wanda yafi nan gidanku ga ki da dan Jariri. Na sake rushewa da kuka na ce "Ni ba zancan dan Jariri bane ya daga min hankali. Mama Tabita bakya ganin yadda Mahaifina ya zama? Tabita ta bude baki tana mamakina can tace "Na dauka babban farin cikinki ne yanzu hankalinki zai kwanta binciken da kika dade kina yi akan addinai kala-kala, me yasa kowa da abinda yake bautawa ba'a bautawa abu daya Mahaifanki suna bin addinai daban-dabam, yanzu Mahaifiyarki da Mahaifinki da ke da kannanki kun zama abu daya kuke bautawa. Allah Yasa Baban wannan yaron shima ya zama yana bautawa abun da kuke bautawa. Tasa hannu ta dafa kafadata ta ce "Zo mu shiga gida in kintsaki ke da danki daga ganinku kunsha wuya.
Na fisge kafadata naki tafiya na tsaya cak na rasa abun yi, jin zuciyata nake tamkar ana kwankwatsamin don takaici, wani jiri ne yake daukata yake shirin ya yar dani kasa. Tabita na lallashina bana fahimtar abunda take fada. Ukuba tayi ukuba, tashin hankali yayi tashin hankali na zura da gudu gidan su Hamma Huzaifa inje in tambaye shi, ya akayi yana raye ya bari haka ta faru da Mahaifina. Sai Mahaifiyarsa ta ce min ai a lokacin dana ganshi dinann a bakin mota kayansa ake zubawa a mota tafiya zaiyi Saudia. Jami'ar koyan addinin Musulunci ta Madina ya tafi karo ilimim addinin na tsawan shekaru hudu. Ta dauko min wasikar daya bari a bani. Na bude na karanta, ashe Hamma Huzaifa yana tsananin sona bai fadamin ba sai a wasika. Na sulale na zauna a tsakiyar dakin su Maman Huzaifa ina ta sharbar kuka. Maman Huzaifa tayi ta bani baki ta ce "In kwantar da hankalina in daina kuka duk abun daya samu bawa jarrabawa ce daga Allah. Na ji dan sanyi a raina dana samu mai lallashina mai nuna min akwai Allah. Na share hawayena da gefen mayafina nayi ajiyar zuciya. Mama ta matso kusa dani ta ce "Fatima, Huzaifa ya shigo dazu yana hawaye ya shaida mun dalilin hawayensa ke ya gani da dan Jariri kin haihu. Yayi tsananin bakin ciki da bacin rai da kika watsar da duk abubuwan da ya koya miki tun kina yarinya, yace mun tunda yake bai taba ganin yarinyar da take da matukar hankali da tunani da sanin ya kamata kamarki ba, ya shaku dake yana kuma godewa Allah da Allah Yasa kika Musulunta ta sanadiyyar sa, yasan kuma ba karamin riko zaki yiwa addininki ba. Amma hankalinsa yayi mummunan tashi da yaga abun da bai taba zata ba a gareki. Nasan duk inda yake yanzu yana can yana tunani da bacin rai. Da kyar na lallashe shi ya tashi ya tafi shi da direba za'a kaishi filin jirgi.
Iman ta girgiza kai ta ci gaba da cewa "Sai ajiyar zuciya nake na kasa yiwa Maman Huzaifa bayani. Nayi shiru na kasa magana. Sai ni sai zuciyata da Ubangijina muka san gaskiya, babu abin da zan fada su yarda dani, tashin hankalin da nake ciki ba zai barni in iya bayani ba. Ni da Maman Huzaifa muka yi shiru muna tunani can na daure na bude baki nayi magana na ce "Mama nazo wajen Hamma Huzaifa ya aka yi ya bari haka ta faru da Mahaifina? Maman Huzaifa ta kalleni ta ce "Meya faru da Mahaifinki Fatima? Sai na rushe da kuka na ce "Mahaifina na gani sanye da kayan bauta irin na Mahaifiyata, da alama ma wani babban mukami suka bashi a wajan bautarsu. Mahaifiyata ta ja Mahaifina ya bar addinin Musulunci ya bi nata. Cikin shesshekar kuka na ci gaba da cewa "Har yanzu ni Musulma ce ban bar addinin Musulunci ba, yanzu ma nake kara zurfafa a cikinsa, nazo da niyyar in tunkari Mahaifina in shaida masa na karbi addininsa, na Musulunta kuma zan bishi koda kuwa Mahaifiyata zata yankani. A yanzu nake son tsananin taimako da shawarwari daga Hamma Huzaifa sai gashi Allah mai yadda Yaso ya dauke min Huzaifa lokacin da nake tsananin bukatar taimakonsa, wanda bana fargaba bana kokonto, da jikinsa da dukiyarsa zai taimake ni in rike addinina. Bugun kirjin da nake ina tinkaho Mahaifina Musulmi ne zan iya binsa in Musulunta, sai gashi komai ya canja min. Bani da sauran mai karfafa min gwiwa inci gaba da bin addini Musulunci sai Allah. Meya sa Babana yayi min haka? Danme ya bari suka rinjaye shi ya bar addininsa, addinin gaskiya, addini mafi tsafta mafi can-canta a bishi? Bayan tsawan shekarun da aka dauka yana rike da addininsa, yaki shiga nata yanzu kuma kwatsam ya bari ta rinjayeshi. A tunanina shine namiji ni kuma babbar *yar mu zamu hadu mu hada kai mu rinjayeta ta shigo Musulunci sai gashi shi ta rinjaye shi. Allah ne kadai gatana, shine jagorana, Shi zai tsareni Ya kareni, don bazan iya canja addinina ba saboda Mahaifina ya bar addinin, ko don Huzaifa ya bar kasar. Na sake kifa kai akan gwiwata kuka mai radadi ya ketomin.
Maman Huzaifa ta matse hawayen daya cika mata ido ta dafa kaina ta ce "Fatima kinyi gaskiya kada kibar addininki komai ukuba. Dare da rana, safe da yamma Huzaifa yana tunani, gashi zai tafi wazai ci gaba da taimakonki akan addininki, yana ta sake-sake yana neman shawarata. Sai muka yanke hukunci kafin ya tafi yaje ya sami Mahaifinki a boye ya sanar da shi cewar kin Musulunta ya ci gaba da baki goyon baya ki rike addininki. Kafin Huzaifa yaje ya fada masa sai rashin lafiyar ciwan kafa ya dami Mahaifinki bayan tafiyarki makaranta. Kafar ta rure, ta kumbura ko fita baya iya yi, ganin halin da yake ciki shi ya hana Huzaifa ya je ya sanar masa na ce ya bari ya samu sauki tukunna don ya dade yana jinya. Anyi maganin asibitin, anyi na gargajiya abu ya faskara kullum kafar sake suntumewa take. Aka rasa kan ciwon musamman idan dare yayi ciwon yafi damunsa ihunsa har gidan nan. Baban Huzaifa ma yayi masa kokari, duk inda ya samu labarin mai magani zai je ya dauko shi ya kawo shima yayi bajintarsa ya tafi, ciwo dai yana nan danye sharaf. Ciwo daga Allah babu wanda yasan sanadiyyar ciwon, haka kuma babu wanda yasan maganin ciwon.
Iman ta sharbe hawaye, suhaif ya sake sa hannu a aljihunsa ya dauko mata wani hankici ya mika mata, ta karba ta goge hawaye. Jama'a sai sake gyara zama suke suna jin wannan abun al'ajabi. Taci gaba da cewa
"Na dakata da kukan da nake na tattara hankalina gaba daya ina sauraran Maman Huzaifa, zuciyata cike da fargaba da tsananin tausayin Mahaifina da kuma kaguwa inji karshen labarin. Me ya hada ciwon kafa da canja addini? Maman Huzaifa ta ci gaba da cewa "Kinsan tsakanin mata da miji sai Allah, ashe Mahaifiyarki koda yaushe tana lallashin Mahaifinki ya yarda ta kaishi wajen bautarta, a kwai wasu turawa da suka shigo garin nan suna yada addininsu. Allah Yana basu iko su warkar da mutum duk tsananin ciwo, amma fa da sharadi kafin su warkar da mutum. Zasu saka masa doka idan ya warke dole ya koma addininsu. Wanda bashi da rabo, hankalinsa ya gushe, ciwo ya tsananta so yake ya rabu da ciwon ya huta, sai idonsa ya rufe ya manta magani da ciwo duk yana hannun Allah, sai kaga mutum ya amsa musu da "Eh na yarda idan na warke zan koma addininku. Kuma babu mahalukin daya isa su warkar da shi ya tsere yaki shiga addininsu, kana warkewa abu na farko da za su yi maka shine su baka babban mukami a wajan bautarsu, su baka kudi masu yawa idan kana dashi ma sai su kara maka lunkin naka, su zamana koda yaushe suna tare dakai suna koya naka addininsu har sai sun tabbata addinin ya ratsaka ka manta da naka na da, kafin su daga maka kafa. To irin haka ne ya faru da Mahaifinki. Da tsananin ciwo ya dame shi ya amincewa Mahaifiyarki, wacce take member ce a cikin kungiyar, ta dauko wadannan turawa suka zo suka dinga zano masa sharuddan gaba daya ya amince. Allah Ya basu iko suka warkar da shi a cikin sati biyu kacal yayi garau, duk da ransa bai so ba dole ya dulmiya ya bar addininsa. Wato ranar da muka ji labarin haka ta faru da Mahaifinki hankalinmu ya tashi musamman Huzaifa ke yafi tausayawa, babu yadda zamu yi dukkanmu. Huzaifa ya so ya fasa tafiya Madina ya zauna saboda ya taimaka miki ki rike addininki amma babu yadda za'ayi ayi haka, tunda ya gama komai na tafiya har sun turo masa da takardar an dauke shi, suna nemansa a wannan lokacin za'a fara karatu. Mahaifinsa ya ce lallai ya zo ya tafi.
Iman ta ce "Nayi kuka, nayi takaici har kamar zan zautu. Daga karshe na dangana, na yiwa Maman Huzaifa sallama ita kuma taci gaba da bani baki tana kara karfafamin gwiwa akan ko ba Huzaifa ita zata maye gurbinsa iya karfinta zata taimaka min duk abinda ya cushe min na game da addini in zo in tambayeta zata warware min. Sannan duk lokacin sallah in dinga yin wayo ina sulalo jiki ina zuwa dakinta ina yin sallah a boye a ranar da Mahaifanki suke gida. Na mata godiya na fito na nufi hanyar gidan mu. Kafin na iso gida nake jiyo kukan dan Jaririna a Boy's quater, da alama wanka Mama Tabita take yi masa. Hankalina ya tashi na nufi inda suke da sauri ina tunanin idan an gama yi masa wankan wanne kaya za'a saka masa gashi bani da kudi. Na isa inda suke kan baranda na zauna a gefe ina kallonsu sai wanke shi take da sabulu. Ta juyo ta dubeni ta ce "Ashe ko wankan haihuwa ba'ayi masa ba. Yau ki ka haife shi ne? Na sunkuyar da kai kasa na ce "Jiya da daddare aka haifeshi. Tabita ta maimaita abunda na fada, "Jiya da daddare aka haifeshi. Ban sake cewa komai ba. Ta ce in shiga dakinta cikin akwati in dauko wankakkiyar atamfarta in kawo ta lullubeshi. Na tashi na shiga dakin na dauko zanin na kawo mata ta lullebeshi. Sai tsotsar hannu yake saboda yunwa. Ta jawo dan kwandon kayan kwalliyarya ta dauko mai basilin tana shafa masa. Ta ce "Bari in gama shafa masa mai sai ki karbe shi ki bashi nono ya sha yunwa yake ji. Ko babu ruwan nonon bai fara zuba ba? Nan fa gabana ya fadi na ce "Eh bai zo ba. Cikin rawar murya na fada. Tabita ta kalleni ta ce "Pretty ki kwantar da hankalinki, ki rungumi danki, ba'a kanki aka fara ciki ba a haihu, ashayar da dan ko ruwan nono bai zo ba dole ki bashi ya dinga sha har ruwan ya zo. Nan ma gabana ya sake faduwa na ce "Mama Tabita ba sai na bashi nono ba, ina laidar da kika karba a hannuna akwai Madararsa a ciki. Tabita ta nuna min inda ta ajiye ledar. Na tashi na shiga kicin na dauko kofi da cokali na tarar da wata katuwar tukunya cike da ruwan zafi akan murhu yana ta tafasa, wai ruwan wankan jego ta dora min. Na dibi kadan a kofi na zo na zauna a kusa da ita na dama madarar na firfita ya huce sannan na mika mata, ta dinga tarfa masa yana sha har ya koshi. Bacci mai dadi ya kwashe shi, ta tambayeni ina kayan sawarsa a saka masa na ce "Bashi da kaya. Cike da mamaki ta sake tambayata "Ina Mahaifinsa? Nayi shiru can na ce "Yana Bauchi, ta ce "Baisan kin haihu bane, ko bai karbi cikin bane ya kyaleshi tsirara? Na sake yin shiru can na ce "Yasan an haifeshi mana. Tabita ta girgiza kai don tausayi ta tashi ta shiga daki da jaririn, ta kwantar dashi akan katifa ta dauko Jakarta ta fito. Ta kalleni ta ce "Bari inje kasuwa na siyo masa riga ko guda daya ce kafin muga yadda za'ayi. Na laluba cikin ledar da na zo da ita na zaro sauran kudina daya rage na bata na ce ga sauran kudina ki hada ki siyo masa. Ta karba ta zuba a jaka sai ta ce min "Ga ruwa can a murhu idan ya tafasa ki juye kiyi wanka. Ko baza ki iya juyewa ba saboda jikinki ba kwari in zauna idan ya tafasa in juye miki in miki wanka yadda zaki gasu sosai? Nayi sauri na ce "Yi tafiyarki zan iya juyewa, zanyi wankan da kaina. Ta amsa min da to ta tafi ta nufi kasuwa. Tana fita na tashi na debi ruwa dai-dai wanka, na kwalfe sauran na zubar a rariya na kashe wutar. Na shiga nayi wankana da soso da sabulun sosai saboda nayi datti da yawa. Bayan na shafa mai nake tunanin kayan da zan saka, don kayana kakaf na baro su a can Bauchi, kuma sauran da na bari suna cikin gidanmu a dakina, bazan iya shiga gidan ba ina tsoron arangama da Mahaifana. A gefen katifa na takure daure da tawul ina kallon kyakkyawan jariri mai kama da Ubansa sak, sai addu'a nake tofa masa Allah Ya sa kada ya biyo halin uwarsa da ubansa. Allah Yasa Musulmi ne mai yiwa Musulunci hidima. Shigowar Mama Tabita ce ta katsemun tunanin da nake. Ta shigo dauke da leda, tana shigowa ta mikomin ledar na karba na bude. Riguna ta siyo masa kyau kala biyu, da *yan wandina (panties) na manya shima biyu. Ta ce "Wandinan manyan naki ne, "Na yi murmushi na ce "Na gode Mama Tabita. Ta farke riga da wando daya ta sakawa Jaririn ta sake kwantar da shi tana jijjigashi har ya sake komawa bacci. Muryar Mahaifiyata ce ta daga mana hankali tazo bakin kofar dakin tana ta bugun kofar tana fada "Tabita yau ba zaki fito ki dora mana abincin rana bane? Yanzu karfe goma sha biyu da rabi na rana ga yara sun fara jin yunwa. Aikin abinci na dauke ki ko aikin jego? Tabita ta hau rawar jiki tayi wuf ta fito tana bawa Mahaifiyata hakuri. Ita kuma kamar sake zugata ake sai fada take. Fadan dai Tabita ake yiwa amma maganar duk tawa ce. Wai ita babu ruwanta in rube mana ni da Jaririn kada Tabita ta sake makara bata dora abinci ba kuma ta tabbatar ta gama musu kowanne aiki kafin ta je ta fara gyara wani shegen Jariri. Na yi shiru sai kwalla nake nasan sai mun wulakanta ni da yaron nan, in ma ba'a koremu ba daga gidan. Ina zan je in zauna ni da Jaririn nan idan aka kore mu? Nake tambayar kaina da kaina.
DUK WANDA BAISAN AN QARA DA YAMMA BA YA SHIGA WAJEN "SHOW MORE" ZAI GANI
Sannan ba'a kammala na 1 ba yau da yammacin insha Allah Surayya Abukar zata karasa.
Reedwan Suraj Isma'il
YARENA ADDININA
CIGABAN LABARI.
Fadila tayi nadama ta gamsu da shawarwarina ta shaidamin in Allah Yaso ko kwana uku bazata
karayiba agarin nan zata kwashe kayanta ta
gudu ta koma garinsu tanemi gafarar iyayenta
tarike addininta. Nima na shaida mata da zarar
anyiwa yan jami'a hutu zan lallabasu janet su bani
kudin mota in koma gida duk da bansan mezan fadawa iyayena ba dakuma yadda zamu karke da
mahaifiya akan sabon addinina.
Fadila ta zage tadaura zanina tazo ta tayani girki.
Ita tayi miyar taushenan tas. Harriet ce ta shigo
tana tafe tana layi idonta sharkab da hawaye.
Muka tashi muka tareta muka rirriketa mun dauka ma ko nakuda takeyi domin watanni
cikinta tara cifcif. Muka zaunar da ita akan
tabarma muna tambayarta meke damunta,
dakyar ta iya bamu amsa tace na tsani
rayuwata,rayuwata ta dagule, nafi sha'awar
mutuwa da inci gaba da rayuwa. Karuwanci ba rayuwar alkhair bace. Ina labe tundaxu abayan
wundo inajin hirarku, pretty kin fimu hankali kin
fimu sani ciwon kanki, kinfimu jin tsoron Allah.
Naji natsani kaina. Ni jahilace wace basan addinin
da nake cikiba saboda wurin bautar iyayen
nawama bana zuwa. Nagamsu da addininku addinine me tsafta addinin gaskiya. Zan karbi
musulunci in mutu a ciki musulunc." gaba su
suhaif suka dau kabbara. Iman ta fashe da kuka
taci gabada cewa "nida fadila da harriet muka
rungume juna muna ta kuka. Aranar na
musuluntar da harriet ta zabi suna khadija. Na sata tayi wanka kamar dai yadda hamma huzaifa
ya koyamin. Nafara koya mata karatun salla da
yadda ake yinta. Abincin da bamu iya ciba mu
dukka hankalinmu a tashe muna nadama. Bayan
munyi sallar isha'i. Fadila tace zata tafi gidan gibrel
ta hado kayanta washe gari zataje banki ta kwashe kudinta ta gudu garin su amma kafin ta
tafi zata zo tabamu kudin mota muma mukoma
gida. Sai dai fatan Allah yasadamu da alhairinsa.
Ta tafi ta barni da harriet abu kamar a mafarki
harriet ta musulunta. Ta zauna zaman dirshen wai
ita adole yau saita koyi karatun sallah. Har sha biyun dare ina koya mata karatun dana iya, ta
tashi tayi alwalla ta sake yin magariba da isha'i
sannan muka kwanta.
Nafara bacci kenan harriet ta daka min duka na
tashi figigit saina ganta a durkushe tana
murkususun zafi. Na kunna fitilar lantarkin dakin sai naganta afujajan sai zufa take tana cije baki
wai cikinta ciwo. Nace ko nakuda ce? Tace eh.'
gabana yafadi nahau salati na rirriketa nida ita
dukka yarane bansan yaya zanyi mata ba. Nafita
da gudu na kwankwasawa mr.segun daki naga
kwado a datse abakin kofar shima yau bazai kwana a gida ba. Ga janet ma bata dawo ba, na
dawo wajen harriet sainaga wani ruwa yana
fitowa daga jikinta ciwan kuma kara karuwa
yake sai ihu take tana kuka. Nima na fashe da
kuka jikina yadau karkarwa. Nace "yaya zamuyi
yau? Na tambayeta akwai kudi ajakarta ne inje insamo mota? Tace naira ashirin ce kawai a
jakarta, fitar da take aiba namijin dayake
daukarta da wannan tsohon cikin. Wani waje
take samu tazauna tayini cur sannan ta dawo
gida bakin cikin rayuwane kawai ya isheta. Nace
to bari in dauki naira ashirin in nemi achaba inje in kirawo micheal yazo yakaita asibiti ko yaki ko
yaso shiyayi mata cikin ai. Harriet fadi take
inyisauri in kirawo shi yazo yakaita asibiti kafinta
mutu. Nadauki naira ashirin na fita da gudu. Dare
yayi sosai bbu yan achaba, na tuna akwai wani
dan achaba. dakinsa awata boy's qauter dake kusa datamu. Naje da gudu na kwankwasa masa
kofa nace yataimaka yazo yakaini wani wajen
nan cikin G.R.A. ne zanbiyashi, yafito da babur
dinsa nahau ahanya yake tambayata "lafiya? Na
shaida masa "harriet ce zata haihu zan kira
wanda yayi mata