Showing 87001 words to 90000 words out of 110329 words
Chapter 30 - YARENA ADDININA Book By Jamila Umar Tanko JUT.txt
balarabiyar fa? Iman ta ce "Matar Hamma Huzaifa ce da yaransa. Zubaida ta gaisheta da turanci, Iman ta ce "Ai bata jin kowanne yare sai larabci, *ya*yanta ne suke jin fulatanci da turanci. Iman ta fassarawa Zainab abun da Zubaida take cewa wato sannu da zuwa. Zainab tayi murmushi ta mikawa Zubaida hannu suka gaisa. Zubaida tayi gaba suna biye da ita har cikin gida tana cewa "Ku shigo ku zauna, ashe yau akwai labari kala-kala. Ga Iman ga Hamma Huzaifa sannan ga matarsa balarabiya, ga kuma Yayana Suhaif wai ya za muyi? Naja'at ta ce "Ai kuwa baza ki sha labarin komai ba dan kuwa Iman bata iya surutu ba. Katin biki kawai zamu baki mu tafi a gidana suka sauka.
Suhaif da Iyayensa zaune suke a dandasheshen gidan da Suhaif yasa aka rushe gidansu na da aka mayar dashi na zamani. Ya zuba musu kaya na alfarma na zamani, idan ka shiga gidan baza ka taba zata a Doko kake ba, sai ka fito kofar gida. Goggo ta dube shi taga a hautsine yake kamar wani abu yana damunsa. Ta ce "Baban gida kamar kasha wuya a Umarar nan, naga ka rame duka ka hautsine kamar ba kai ba. Shi yasa na ce ka bari muje da Azumi, kace ta Mauludi tafi rashin cikowa. Mahaifinsa ya ce "Da gaske ne ai ta Maulud tafi rashin jama'a. Wane irin wuya zai sha kamar wani wanda ya je babu guzuri? Goggo ta ce "Allah ganinsa nayi kamar ba shi ba.
Suhaif yayi ajiyar zuciya ya ce "Babu wata wuya da muka sha kawai dai yanayin rayuwar ce haka.
Suka dauki lokaci mai tsawo suna hira sai Suhaif ya bude wata *yar jaka a kusa dashi ya zaro katina guda biyu ya mikawa Baba daya, Goggo daya. Baba ya iya karatun Hausa, Goggo kuwa babu ko ABCD ta jujjuya katin ta ce "Shegantaka zaka yi mun, ka fada min da baki ko katin meye. Ko auren aka dauro daga Makka bamu sani ba, ka samu wata ne? Suhaif yayi murmushi ya ce "Baba ya karanto da karfi kiji. Baba ya ce "Daurin auren Huzaifa Ahmad Jalingo da Fatima Lamin Jalingo. Su duka suka hada baki "Wacece Fatima? Suhaif ya yi ajiyar zuciya ya ce "Katin daurin auren Hamma Huzaifa da Iman ne. Sai Goggo ta dau salati mai hade da kuka kamar an fada mata mutuwa. Baba ya cabki kunnan Suhaif yana ja yana fada cewa yake "Shin na fada maka ko ban fada maka ba? Na ce ka hakura ka auri wata, ko ban fada ba? Daman banda hauka a ina ka taba jiran mutumin da baisan ana jiransa ba. Nan sai suka dinga yiwa Suhaif nasihohi kala-kala cewar kada ya sake ya ce zai tsangwami kansa ya shiga damuwa, ya dauka haka shine yafi alkhairi, ya nemi wata ya aura. Shi kuma ya rokesu su yiwa Allah suyi masa alfarma su shirya aje bikin nan dasu saboda Iman ta zama *yar gida. Goggo bata musa ba, ta ce zata je harma da *yar gudunmawarta, Iman ai *yarta ce. Baba ne yake dujewa da kyar Suhaif ya lallasheshi gami da yi masa alkawari da zarar sun je bikin Iman sun dawo a watan shima zasu ji nasa auran. Yayi musu alkawari ya yadda da kaddara zai nemi wata ya aura. Sunji dadi sosai sun yi masa addu'a Allah Ya yi masa albarka ya musanya masa da ta gari. Suhaif ya dauki jakar kayansa ya nufi dakinsa hawaye ne ke zuba sharr-sharr daga idanuwansa. Ya kwanta yana tunani haka kuma yake kuka, saboda ya kasa bacci ya kasa daina son Iman har yanzu. Sai ya tashi cikin dare ya yi ta sallah, ya yi azumi ya roki Allah Ya kawo masa karshen damuwar nan da ta haddasu a zuciyarsa ta Iman shekara da shekaru.
Washe gari Iman, Huzaifa matarsa da *ya*yansa suka shirya suka fito dan kama hanyar tafiya Yola. Najib da matarsa Naja'at suka musu rakiya har filin jirgi. Najib ne ya biya musu kudin tikitinsu duka, Huzaifa yayi-yayi ya bari ya biya ko rabi ne. Najib yaki ya ce shima bashi ya biya ba, tun jiya Suhaif ya bashi ya ce ya biya musu. Suka yi ta godiya suka shiga jirgi suka tafi, sannan Naja'at da Najib suka dawo gidansu.
Ana jibi daurin auren Iman da Hamma Huzaifa. Suhaif ya yi waya Abuja aka kawo masa wasu sababbin motocinsa fil-fil a ledarsu guda uku da ya shigo dasu daga GERMANY. Motocin duka ukun irinsu daya, kalar fentinsu daya bakake kirar zamani wadanda ake yayinsu a lokacin. Ana gobe daurin aure kuma da sassafe suka shirya a daura dasu. Idan da wuri aka daura su juyo a ranar idan kuma an samu African time su sake kwana. *Yan Doko sun hallara a Kano gidan Baba na Kano, Najib da Naja'at sun iso da sassafe sai Zubaida da mijinta Muslim da *yan tagwayenta da mai renonsu Lantana suma sun iso akan lokaci. Ana shirya yadda za'ayi tafiyar, wannan ya ce a shiga babbar mota daya tafi, wancan ya ce araba a shiga kananan motoci a jeru a tafi da direbobi. Suhaif ya ce dalilin da yasa ya aika Abuja aka kawo masa sababbin motocin nan iri daya guda uku, sai dan su tafi dasu zai fi tsari, kuma suna da saurin tafiya, gasu da tudu dan haka nisan nan bazaisa su gajiba. Yana so idan sun tashi dawowa suje filin jirgin Yola su dawo ta jirgi. Babansu ya ce "Ban gane muje a mota ba mu dawo a jirgi waye zai dawo da motocin, direbobin? Idan haka ne mu tafi a jirgi mana. Suhaif ya ce "A'a so nake in bawa amarya kyautar daya, angon ma kyautar daya sai in tuko dayar in dawo ni da wanda baya son hawan jirgi. Baba na Doko ya zabura ya ce "A'a Suhaif har kyautar motoci biyu zaka yi? Haba-haba sunyi yawa irin wadannan motoci masu tsada galla-galla dasu a ledarsu. Baba na Kano ya dakatar da Baba na Doko ya ce "Kyaleshi karka hanashi alheri. Suhaif mai kyauta ne, kuma duk wanda harkarsa ta taso Suhaif yana yi. Da dai ace bai wadata gida bane zai wadata na dawa shine zamu hanashi, ai abun farin cikinmu ne har muka samu yayi hakuri ya dangana, har zai halacci wajen bikin har ma ya dauko kyauta ya basu yayi musu fatan alkhairi. Suhaif hakan da kayi yayi, Allah Ya saka da alkhairi kaci gaba da hakuri da dangana Allah Zai saka maka da alkahirin sa.
Mota daya Muslim ne yake tukawa, Zubaida agaba. Kujerun baya kuwa mai aikin Zubaida ce da *yan tagwayenta. Daya motar kuwa Najib ne yake tukawa, Naja'at a gaba, Mama da Goggo a baya. Sai daya motar Suhaif yake tukawa Baba na Kano a gaba, baya kuma Baba na Doko shi kadai. Suka yi addu'o'i sannan suka kama hanya. A jere suke tafiya, suka nufi garin Jalingo. Jalingo Ja garin Baba, shiga da kaya ka fito da gammo. Inji masu kirari.
Nima sai na dana kirarinmu.
KANO TA DABO TUMBIN GIWA KO DAME KAZO MUN FIKA
Ko da musu ne????????????????
Reedwan Suraj Isma'il
>>>>>>>>>>>>>>> YARENA ADDININA
___CIGABAN LABARI
Tafiya suke babu ji, babu gani taki ta kare. Sunyi sallar azahar a hanya, haka la'asar ma, suna yi suna tsayawa suci abinci, sannan suci gaba da tafiya. Basu jigata sosai ba, kasancewar motocin lafiyayyu ne masu sanyin A.C, ga lausasan kujeru kamar akan gadonka kake. Kasancewar Huzaifa ya basu kwatance a rubuce basu sha wuya ba, suna shigowa Jalingo sai suka yi tambaya ba tare da bata lokaci ba aka samu wanda yayi musu jagora har kofar gidan su Iman. Iman da Mahaifiyarta suna zaune a daki. Falon gidan da sauran dakunan da farafajiyar gidan duk mata ne suke ta aikin abinci. Dangin Mahaifin Iman ne jingim, suka taho mota-mota daga Gombe cikinsu har da Kakarta wacce ta haifi Babanta, sauran kuma *yan uwan Mahaifiyar Iman ne da kawayenta, da makwabta suka taru ana ta soye-soye da dafe-dafe saboda masu zuwa daurin auren gobe. Wata yarinya ce karama ta shigo har dakin da Iman take ta sanar mata ta zo waje ana kiranta, tayi baki daga Kano. Tana jin kalmar Kano ko tantama babu tasan su Suhaif ne, don haka tayi zumbur ta tashi da murna ta bude labulen windo ta leka. Ta juyo ta dubi Mahaifiyarta da fara'a cikin harshen turanci ta ce "Mummy da gaske su din ne kuwa. Mahaifiyarta tayi dariya ta ce "To jeki maza ki tare su, gidan nan ba zai shigu ba ki kaisu can gidan da aka gyara na saukar baki. Ni kuma zansa a hada musu abinci a kai, sai nima in zo mu gaisa. Iman ta ja mayafinta ta fito da murna ta nufi wajen motocin su Suhaif.
Kafin ta karasa ta hango Hamma Huzaifa har ya gansu yaje wajensu suna gaisawa. Iman ta nufo inda suke, ido mai kalle-kalle, idon Suhaif ya hango masa Iman ta tunkarosu. Ya ji gabansa ya yanke ya fadi, sai yake kokarin dimaucewa. Duk wanda ke wajen zai iya gane halin da Suhaif ya shiga yanzun nan. Ba Suhaif kadai ba duk wanda ya ga amarya Iman sai ya sake kallonta, wato kyau ta kara yi kamar yau aka cirota daga leda, ta sha kunshin bakar fulawa a fararen kafafuwanta da hannayenta, ga wasu siraran kitso anyi mata yisin-yisin kai ka ce ba da hannu aka yi su ba. Da yake yau mayafi ta yafo, kuma atamfa ta saka super anyi mata dinkin riga da siket. Tana zuwa sai ta je wajen su Baba ta zube har kasa ta gaishe su. Cikin fara'a suka amsa gami da sanya mata albarka a cikin auranta. Ta wuce wurin su Goggo ta durkusa nan ma ta gaishesu. Goggo ta kamo hannunta ta ce "Taho nan Iman *yata mu gaisa sosai, gaisuwar yaushe gamo. Sai Iman ta fara hawaye Goggo ma tana nata. Iman ta karasa wajen su Naja'at ta karbi Hauwa a hannun Zubaida suma tana fara'a tayi musu sannu da zuwa. Huzaifa ya mikawa Iman makulli ya ce "Jeki ki bude musu can gidan su shiga su huta sun sha hanya. Suhaif ya ce da Huzaifa "Su Baba sunce a nuna musu Hotel baza su iya zama anan ba, mata sun yi yawa. Huzaifa ya ce "Ah! Daman matan ne kawai anan mun riga mun kama dakuna a Hotels. Bari su gaisa da Babana da Baban Iman suna falon gidanmu, mu je in kaisu. Huzaifa na gaba, Baba na Doko, Baba na Kano, Suhaif Najib da Muslim suna biye dashi a baya har falon da Mahaifin Huzaifa da Iman suke a zaune a gidan su Huzaifa.
Iman da su Goggo tuni sun shiga gidan saukar bakin, shima kusa ne a tsakanin gidan su Iman da Huzaifa yake. Shima gidan irin gidajensu ne na gwamnati. An share shi an shimfida sabon rog carpet da sababbin katifu, filillika da sababbin zannuwan gadaje. Bandakuna kuwa sababbin bokitaine da butoci. Babu abunda su Goggo suka fara yi sai sallar magaruba da isha'i, daga nan sai suka dinga shiga wanka. Bayan nan sai suka hallara a falo suka fara cin abincin da aka jera musu kala-kala. *Yan Uwan Huzaifa da *Yan Uwan Iman suna ta shigowa suna gaishe su. Da yawa daga cikinsu ko Hausa basa ji sai fulatanci. Iman tana zaune tana fassara, tana kuma gabatar da su. Suna ganin kanwarta Hajara (Rabecca) kafin ta gabatar da ita Zubaida ta ce "Amma wannan kanwarki ce ko? Don kuna kama. Haka Mahaifiyar Iman tana shigowa su Goggo suka ganeta. Ta zo ta zauna bayan sun gaisa sai ta shiga yi musu godiya, ta ce Iman ta fada mata duk abun arzikin da suka yi mata, don haka sun zama *yan uwa. Duk da ba Hausa sosai take ji ba. Su Goggo suka ce babu komai. Zuciyarsu cike da tambaya ai Mahaifiyar Iman ba Musulma ba ce a labarin da ta basu. Yaya suka ganta da hijab har kasa tana kiran Allah da Annabi?
Suhaif, Huzaifa, Najib da Muslim ne suka shigo. Goggo ta ce "Ina kuka shiga ne? Ga abinci fa jifgi ku zo ku ci ku kaiwa su Babanku suma. Huzaifa ya yi sauri ya ce, "Ai su har an kaisu masaukinsu a Hotel sun kwanta, sun ci abinci tare da su Babanmu. Su kuma su Suhaif mun ci tare, sannan suma sun je masaukinsu sunyi wanka sun ajiye kayansu. Yanzu ma zuwa muka yi su gaishe da Mummy (Maman Iman). Su Suhaif suka durkusa suka gaisheta cikin harshen turanci, tayi ta godiya da shi albarka. Mama, Goggo, Zubaida da Naja'at babu wanda bai kawo wa Iman gudunmawa ba. Suka firfito da gudunmawarsu suka jifge a gaban Iman da Mahaifiyarta sai godiya suke. Daga karshe Mahaifiyar Iman tayi musu sallama, ta ce zata aiko yara su zo su kwashe kayan, ta fita Mahaifiyar Huzaifa da kannensa ne suka shigo, suma aka gaggaisa suna godiya suma. Bayan sun tashi sun fita sai Zubaida ta taba cinyar Iman ta ce "Iman bayan kin bar Doko meya faru? Na ga Mahaifiyarki da hijab, ta Musulunta ne? Najib ya ce "Wannan Zubaidar akwai shegen surutu da tambaya. Mama ta ce "Zubaida ta baci da magana na rasa dalili, gashi ke ba bangaren jarida kika karanta ba. Naja'at ta ce "Kun manta mijinta Muslim dan jarida ne? Sai su duka suka kyalkyale da dariya. Goggo ta ce "A'a ku bar su kawaye ne fa, suyi hirarsu. Ba tare ku ka gansu ba? Gida daya, daki daya, ajinsu ma daya a Doko.
Iman ta ce "Lah ai ba laifi bane dan ta tambayeni, idan ma babu wanda ya tambayeni a cikinku sai in ce baku damu dani ba. Ranar da na bar Doko a motar *yan sanda, tashar unguwa uku suka kaini, suka saka ni a zungureriyar mota mai zuwa Jalingo. Suka bani kudin motata a hannuna, nayi musu godiya suka tafi. Ina ganin sun fita daga tashar na fito daga motar na tari tasi sai gidan Mummy Naila dan in ga Abdul-Malik kuma in mata sallama nasan idan na bar Kano na bari kenan. Da na je sai tayi matukar mamakin ganina ita da sauran ma'aikatan gidan da suka sanni da. Abdul-Malik ya warke ras har ya girma yayi wayo abinsa. Kamar zai gane ni sai kallona yake tayi ba kiftawa. Mummy Naila ta hau tambayata ina na tafi ne? Kuma meyasa na tafi? Kamar wata jahila zan hada kaya in bar gidan, in ce bana son ganin Abdul-Malik cikin wannan halin. Ina ruwan Allah, Zai iya yanke HukuncinSa akan bawansa yadda yaso. Na kasa amsa mata wadannan tambayoyi sai hawaye nake na rungume Abdul-Malik. Ta sa aka kawo min abinci na ci, sai ta ce in shiga dakina in yi wanka in shirya, taga alamar a gajiye nake. Na shiga dakina na bude dirowata, abun mamaki kayana suna nan babu wanda ya taba, an hada min su a waje daya. Bayan nayi wanka na zabi bakar doguwar riga a cikin kayana na saka. Sannna na dinga jero sallolin da ake bina. Abdul-Malik ne yake bude kofar dakin da nake yana lekowa, ya kalleni sai ya koma da gudu. Mummy Naila ta leko da kanta ta ce in fito falo idan na gama muyi kallo da hira. Na fito muka zauna a falo taci gaba da tambayata. Babu fa'idar in boye mata komai, duk da ba komai ba ne zai iya faduwa. Na gyara zama na fara neman gafararta, kuma na bata hakuri saboda zata ji labari sabanin na farko dana bata. Na zaiyano mata makasudin barina garinmu, saboda in zo in rungumi addinin Musulunci ne nabar gidanmu, kasancewar Mahaifiyata ba Musulma ba ce kuma ta rinjayi Mahaifina shima ya bita ya bar Musulunci. Na fada mata dalilin da yasa na bar gidanta kuma don kawai ina jin tausayin Abdul-Malik na matsanancin halin da yake ciki na rashin lafiya abun yake ta damuna, saboda ina son Abdul-Malik. Sai na bata labarin rayuwata a Doko, na ce na kara samo ilimi. Yanzu kuma nabar Doko zan koma garinmu Jalingo in je in sami Iyayena in yi amfani da iya ilimim dana samo in musu nasiha, in wa'azantar, in kuma tunasar dasu su rungumi addinina. Duk wannan bayanin da nayi mata babu in da na sako zancen Matsafan da suka addabeni, domin zaiyi wuya ta fahimceni. Ita ba *yar Nigeria ba ce, wata kila ma basu taba jin labarin tsafi ba, ko kuma irin wanda suka sani ba irin namu ba ne.
Mummy Naila ta fahimceni sosai, ta ce kuma ta kara sona da tausayina fiye da da, ta shaida min tunda take a zamani irin wannan bata taba ganin wacce ta sadaukar da rayuwarta ba, ta shiga wahala da halaka dan kawai ta rike addininta, sai ni. Ta nuna damuwarta akan rabuwa da ni, ta ce ba dan dole ba da baza ta barni in koma gida ba. Har yau har gobe bayan tafiyata bata samu mai rainon danta ba tsakani da Allah irina. Na yi mata godiya da alkawarin zumunci tsakanin ni da ita ba zai rabe ba, ko da bata kasar nan zan je duk inda take. Na karbi lambar wayarta, ta dauko kaya da kudi masu yawa ta bani. Washe gari ta hadani da motarta da direba ya kawoni har nan garin, kofar gidanmu.
Naja'at ta ce "To ya kika tarar da Iyayenki? Iman tayi ajiyar zuciya ta ce "Kannena da *yan unguwa sun rude da murna, da ihu suka zo suka tareni. Mahaifiyata da Mama Tabita a guje suka fito suka rungumeni muna kukan murna. Kanina ya ruga ya kira Babanmu a Masallaci. A bin daya fara farantamin rai shine da naga Mahaifina rike da carbi a hannunsa, haka kuma shi da kanina Abubakar dukkansu abun salla rangadede a goshinsu. Bayan na kintsa na ci abinci, nayi wanka, nayi salloli. Mahaifina ya kirani falo shi da Mahaifiyata da kannena, duk suna zaune. Ya tambayeni ina na shiga shekaru biyu? Na fara musu labari tun daga farko har karshe.
Mahaifina ma ya bani labarin abunda ya faru tun daga farko har karshe. Ya ce "Allah ne Yayi zan dawo in same shi tare da Mahaifiyata har sun rabu, yayi shekara guda cur a garinsu Gombe shi