Showing 18001 words to 21000 words out of 110329 words
Chapter 7 - YARENA ADDININA Book By Jamila Umar Tanko JUT.txt
"Sannunku da shara, suna ganin Malaminsu sai dukkansu suka durkusa suka gaishe shi, ya amsa musu cikin lankwashasshiyar murya mai dauke da jimami. Kallo daya zaka yi masa ka san yau hankalinsa a tashe yake. "Malam yau kuwa lafiya? Iman ta tambayeshi. Malam Yahaya ya nisa yayi shiru yana tunani na wani dan lokaci. Sai gaba dayansu gabansu ya hau faduwa suka bar abinda suke suka nufo inda yake tsaye jikinsu na karkarwa. Malam Yahaya ya ce "Ku yi hakuri ku koma gida yau baza'a yi makaranta ba. Ku tari masu zuwa a hanya kuce sai nan da sati guda za'ayi makaranta. Rakiya ta dafe kirji ta ce "Lafiya? Iman kuma tuni hawaye ya fara kwaranyo mata babu abunda take sai karkarwa tana fargabar taji me zai fito daga bakinsa ya ce "Kamar yadda kuka sani dukkan mai rai saiya dandana mutuwa, Allah Ya yiwa dan uwanmu abokinmu, yayanku rasuwa a jiya da daddare yanzu muka dawo daga binneshi. Iman taji kafarta bazata iya daukarta ba saboda tashin hankali sai ta durkusa ba tare da ta iya bude baki ta yi tambayar da take so tayi ba. Waye ya rasu? Malam Yahaya ya ce "Malan Hadi ya rasu "Innalillahi wa'innailaihirraji'un suke karantawa yayin da Iman ta dora hannu aka tana jin jiri yana jujjuyawa da ita, hawaye kuwa daya na bin daya. Ya ce "Kar kuyi kuka addu'a zaku yi masa, ku tashi ku rufe ajin ku tafi gidanku. In ya so ko da yamma sai ku hadu kuje kuyi wa iyalansa ta'aziyya. Ya wuce ya tafi da sauri yana share hawayen da ya cika masa ido ganin kukan da Iman take shi yasa shi kuka.
Rakiya da Laure suka goge guntun hawayen daya cika musu ido suka zo kan Iman wacce kukanta ya ribanya nasu, suna lallashinta dakyar da sudin godhi suka lallasheta ta tsagaita da kukan da take ta tashi daga tsugunan da tayi ta fito suka rufe ajin suka nufi hanyar komawa gidajensu. A hanya suka dinga cin karo da dalibai, suna ganinsu Iman suna dawowa sai suyi turus su tsaya. Sai suyi masa bayanin cewa ba makaranta saboda rasuwar Malam Hadi. Nan dai kowacce ta rafsa salati ta juya gida. Su Rakita suka yiwa Iman Sallama da suka zo lungun gidansu, suka shiga Iman kuma ta wuce ta nufi hanyar gidansu. Dai dai kan kwanar da Iman zata shiga gida ta ci karo da dandazon *yan ajinsu su biyar suna tafiya makaranta Iman ta tsaya suka gaisa. Talatu ta ce "Ah Iman mantuwa kika yi kika dawo? Iman ta girgiza kai hawaye ya zubo mata ta ce "Ba ayin makaranta yau saboda Malam Hadi ya rasu. Raiha ta ce "Wai yaya malaman makarantar nan suke ta rasuwa haka a jere a jere? Kunga ba'ayi sadakar arba'in din Malam Nayaya ba sai Malam shehu ya rasu. Ga shi ba'a fi wata biyu ba da rasuwar Malam Shehu Malam Hadi ya rasu. Allah na tuba. Mai jidda ta ce "Kuma dukakansu lafiya-lafiya ake rabuwa dasu sai dai aji sun mutu, babu ciwo. Ku kalli Malam Hadi jiya-jiyan nan fa ya zane *yan ajinmu ya farfasa mana baya. Lallai da yasan zai mutu da baici zalinmu ba. Dan ba laifin fari bare na baki ya hau dukanmu.
Iman ta girgiza kai yayin da wasu hawaye masu zafi suka zubo mata ta ce. "Ya *yan uwana musulmai ku yadda da kaddara, kuma duk mai rai saiya dandana mutuwa, ko da ciwo ko babu ciwo sai an tafi. Allah Baya barin wani don wani yaji dadi. Ikon Allah Ya wuce haka ba mutuwar malamanmu a jere ba idan yaso zai iya hada garin nan koma kasar nan ko duk duniya ya kashe bazai karuba ba zai ragu ba. Shine Ya haliccemu kuma ya rayamu haka kuma zai kashemu a duk sanda Yaso fatan mu Allah Ya sa mu cika da Imani. Cikin sanyin jiki da gasgata maganar Iman ta ratsa zuciyoyin su dukkansu suka ce "Amin. Iman ta dafa kafadar Maijidda ta ce "Maijidda babu kyau fadar abu marar kyau akan mamaci domin shaidar duniya ita ake masa a lahira. Ku fadi abun alheri ko kuyi shiru. Domin Musulmi dan uwan Musulmine, kuma abunda kaso wa kanka kasowa dan uwanka. Muma za muso idan mun mutu ayi mana shaidar kirki. Dan Allah mu yafewa Malam Hadi koma me yayi mana. Allah ya yafe mana gaba dayanmu. Gaba daya suka ce "Amin mun yafe masa kuma Allah Ya jikansa. Zaka iya ganin farin cikin da Iman taji a fuskarta tayi addu'a, dukkansu suka daga hannayensu sama Iman na kwararo addu'a suna amsa mata da amin suka shafa. Sai Iman ta ce "Da yamma bayan la'asar dan Allah mu hadu a bakin ajinmu mu dunguma muje gidansa muyi musu ta'aziyya ko ba haka ba? Dukkan su suka ce "Haka yayi in Allah Yaso zamu je.
Ummi ta ce "Mungode Iman kina gaya mana gaskiya, shiyasa muke son zama dake muna karuwa. Akwai ki da hankali, tunani, hakuri, ga ilimin addini, Iman sai na ganki nake tunawa da wani abun addini. Dubi yadda kike shiga kamar a Makka shi yasa nake kokarin in dinga koyi da ke. Iman ta yi murmushi ta ce "Na gode Allah Ya shige mana gaba to sai anjimanku saida yammar. Ta juya ta tafi.
Maimuna bakuwa ce a garin jiya tazo gidan su Raiha *yar uwarsu ce Mamakin Iman ya hanata yin magana tun dazu cikin zumudi bata bari Iman tayi nisa ba ta ce "Wai wacece take burgeku saboda addininta? Iman ta ce muku sunanta? To karya take muku, taudararku take a nan garin dan tasan baku santa ba. Rafkatu sunanta, bama musulma ba ce arniya ce bata da addini. Har cikin shege tayi ta haihu a kashe Dan. Bata da kunya har danbe take da mahaifiyarta akan idona, kai in takaice muku tana cikin kungiyarnan ta matsafa masu shan jini wato (secretSociety). Sai karaf a kunnan Iman, Iman ta juyo a fusace ta kalli Maimuna suka hada ido, sai ta juya taci gaba da tafiya ba tare da tasan inda take jefa kafafuwanta ba saboda tsananin hankali da rudanin data shiga.
Hmmm Sai Allah Ya Kaimu Gobe Da Yardar Allah.
Reedwan Suraj Isma'il
>>>>>>>>>>>>>> YARENA ADDININA
_____CI GABAN LABARIN
Tana tafe tana layi ta shiga wani gida mai *yar gajeriyar katanga ginin kasa mai dauke da daki guda daya dan karami. Gidan wani tsohon mahaukacine wanda Allah Yayi masa rasuwa. Tun bayan mutuwarsa babu wanda ya gyara gidan ya shiga duk da bashi da mata balle da ko jika da zai gada. Danginsa kuma suna tsoron su shiga gidan don sun canfa gidan wai aljanu ne a ciki duk wanda ya shiga zai mutu. Kan kace kwabo gari ya rude da maganar. Duk gidan da kazo giftawa zancen ake wai annoba ta shigo garin nan. An shaidawa mai gari halin da ake ciki. Suhaif kuwa tamkar mahaukaci zaka iya kiransa babu abin da yake sai fada da zage-zage da duk wanda ya kira Iman mayya. Yasa iyayensa a gaba sai magana yake yana cewa duk su suka tonawa yarinyar nan asiri da suka koreta gashi ta shiga wani hali ta shiga gidan da babu wanda yake iya shiga ya zauna, kuma karyane babu maye a duniya. Tun suna bashi amsa har suka kyaleshi yana maganarsa shi kadai a tunaninsu baya hayyacinsa damuwa ce ta fara taba masa kwakwalwarsa. Yaga abu ya faru baro-baro kowa ya gani ace karya ake mata sharri ne.
Haka Suhaif ya kwana bai runtsa ba. Najib yayi iya kokarinsa ya kwantar masa da hankali abun ya faskara. Karfe uku dai-dai na tsakar dare Suhaif na zaune akan katifarsa daram-dakam babu ko alamar bacci a idanuwansa. Najib yana kishingide yana gyangyadi don shima ya kasa kwanciya ganin Suhaif ya ki ya kwanta. Suhaif ya taba Najib, yayi firgigit ya bude ido. Suhaif ya ce "Najib bansan halin da Iman take ciki ba a cikin wannan mugun gidan da aka canfa shi. Babu makwabta gaba da baya, amma Allah sai Ya sakawa yarinyar nan. Najib ya murtsike ido ya ce "Suhaif ka nutsu ka duba maganar nan akwai kamshin gaskiya, ka ji ance yarinyar data tona mata asiri mutuwa tayi a lokacin. Sannan ance lokacin da samari suka tareta zasu daketa suffarta canjawa tayi, idonya yayi jajawur, gashinta ya mimmike, hannunta yayi cako-cako, uwa uba ance tafiya take akan babban *yan yatsunta. Ka duba kaga wanne mutum ne zai iya tafiya akan yatsan kafarsa guda daya? Ka tuna maganar data fada maka ta ce kada ka zama makaho alhali kana gani. Kada ka zama kurma alhali kana ji. Daga karshe ta ce kada ka biyewa abunda zuciyarka take tsananin so alhali ba alhairi bane a tare da kai. Har ka damu ka dinga tunanin ko me take nufi to yanzu ga amsar da take nufi, ta ce ka kiyaye kaki kiyayewa. Suhaif ka zama makaho alhali kiri-kiri kaga abubuwan da suka faru, ka zama kurma alhali kana ji ana fada, kabi son zuciyarka alhali ita ba alhairi bace a tare da kai, ko wannan ka tuna kasan ta fada maka da bakinka ga yadda take. Suhaif ya harareshi ya ce "Ban gane ga yadda take ba? Najib ya ce "Ah ta fada maka a fakaice ita mayyar ce. Suhaif ya daka tsawa ya dakatar da Najib da hannu ya ce "Ya isheni haka Najib, zagin ya isa na dauka kana bayana ashe kana bin maganar *yan gari kana kiran Iman da mayya a gabana. Danme zan yadda da bayaninka? Najib ya dafa kafadar Suhaif ya ce "Dakata kaji dan uwana. Suhaif ya fisge jikinsa ya mike tsaye fada yake tun karfinsa "Babu abinda zanji daga gareka kawai ka kyaleni Malam. Najib na kallonsa yaje ya dawo daga wannan bango zuwa wannan a cikin daki sai fada yake. Najib ya gyara filo ya fara shakar baccinsa don yaga wannan abu na Suhaif ba kararre bane. Can yayi juyi ya kalli Suhaif ya ganshi akan abun sallarsa yana ta nafilfili yana addu'o'i, ya koma yayi kwanciyarsa ya ci gaba da baccinsa ya ce a zuciyarsa "Haka yafi maka alhairi idan ciwo ne Allah sai ya yaye maka.
Da safe karfe takwas Suhaif ya jiyo muryar mahaifinsa a tsakar gida sai yayi farat ya fito bayan sun gaisa, mahaifinsa ya dubeshi shekeke ya ce "Me kake so kace naga bakin ka na son magana. Suhaif ya sosa keya ya ce "Eh Baba ina son magana, daman abunda ke faruwa dazu da asuba bayan masallaci mai gari ya aiko aka yi kirana akan zancen Iman ance tana cikin dan dakin nan har yanzu, mutanen dake kusa da nan duk sun kasa kwanan gidajensu. Ya ce mun yaya za'ayi a fitar da ita daga garin? Shine nake so ku bani izini ni zan je wajenta inyi magana da ita ta fito ta tafi. Goggo ta yi wuf ya fito daga kicin ta ce "kaje ina? Bazai yiwu ba gidan da ba'a iya shiga ko bata a ciki balle tana ciki, masifa biyu kenan. Baba ya dakatar da ita da hannu ya ce "Raliya kwantar da hankalinki yanzu Suhaif ba yaro bane karami wanda bai san ciwon kansa ba tunda har suka yi magana da mai gari ki barshi yaje in har zai iya magana da ita ya ce ta fito ta bar garin to alhamdulillahi. Suhaif ya duka yayi godiya ya juya ya tafi Goggo ta rushe da kuka yayin da kannansa ma su Naja'atu suka sa kuka suna "Yaya Suhaif kar ka je. Ko juyowa bai yi ba balle mahaifinsa ya canja shawarar hanashi zuwa. A zaure ya hadu da Najib a tsaye yana jiyo maganar da ake a tsakar gida. Ya dubi Suhaif, Suhaif ya dube shi sai Suhaif ya kawar da kai yace gaba da tafiyarsa ya nufi kofar fita.
Maganar Najib ce ta dakatar dashi cak ya tsaya a inda yake ya ce "Suhaif yaushe Maigari ya kiraka ya ce ka shiga ka fito da Iman daga gidan nan? Ina tare da kai tun jiya haka da suba tare muka je masallaci muka dawo daki yaushe kaje gurin Maigari? Suhaif ya hasala ya ce "Nayi karyane don su cire mun takunkumin da suka yimin na kada inje wajen Iman. In har kana so ni da kai mu daina gaisawa har abada to kaje kace musu karya nake. Najib ya ce "Muna sonka ne kuma duk mai kaunarka bazai so ka jefa kanka cikin halaka ba. Suhaif ya yatsine fuska ya ce "Inhar kuna sona sai ku so abunda nake so, amma duk kun ki Iman gudunta kuke, tun daga magaruba kowa ya rufe gida haka da asuba kusan kowa yaki fitowa masallaci. A tunanina babu mai kaunata a garin nan tunda kun ki Iman Alhamdulillahi tunda kaina zan jefa a halaka ba wani ba, yaci gaba datafiya ba tare daya kara sauraron maganar da Najib yake fada ba. Najib ya fito yana kiran Suhaif amma ko juyowa bai yi ba yayi tafiyarsa, hawaye mai zafi ne yake zubowa daga idanuwan Najib don bakin cikin halakar da dan uwansa yake jefa kansa.
Suhaif na isa kusa da gidan yaga jakar kayanta a yashe a cikin kasa da takalmanta da hijabinta ya durkusa ya tsince ya karkade ya nufi cikin gidan. Ya yi bismillah yayin daya jefa kafarsa a cikin gidan gami dayin sallama a kofar dakin, yaji shiru ba'a amsa ba. Mutanen da suka hango shi a lokacin da yake shiga gidan suka tsaya daga nesa suna kallon ikon Allah suna sauraron abunda zai je ya dawo tsakanin Suhaif da wannan Dodanniya. Dodanniya mana Iman ta zamar musu a garin nan duk a firgice suke.
Ya ji gabansa na faduwa kasancewar dakin da duhu bai hango kowa ba a cikin dakin. Ya sake kwada sallama gami da kara tura kai cikin dakin ya shiga ba'a amsa ba kuma baiga kowa ba. Ya ajiye kayan dake hannunsa ya bude windon dake dakin, nan da nan haske ya gauraye dakin sai ya waiga kowacce kusurwar dakin babu abinda yake hangowa daga kura sai yana a jikin bango. Yayi matukar razana daya hango idanuwan Iman a bayan kyauran dakin tana kallonsa. Ya shaki numfashi yayi ajiyar zuciya da karfi don ganin Iman cikin wannan hali ya tsorata shi. Gashi kanta buyu-buyu babu dan kwali. Daga yadda yaga idanuwanta suna wurwurgawa yasan ba lafiya ta ke ba. Ya dan matso kusa da ita yayi mata sallama, bata amsa ba. Kallonsa take tamkar hoto. Ya nisa ya ce "Ga hijabinki kisa, ga takalminki kisa da jakar kayanki kizo mu tafi wani garin ba anan garin ba. Bata tanka masa ba, ya sake matsowa ya mika mata hijabin ya ce ta karba ta saka ko gezau bata yi ba sai kallonsa take tayi. Yayi magana harya gaji bata amsa masa ba, ya kira sunanta wajen sau ashirin bata amsa masa ba. Daga karshe ya ajiye mata kayan a gefe. Ya ce "Ko yunwa kike ji bari naje in suyo miki kosai da koko.
Ya je ya suyo ya zo ya ajiye mata a gabanta ya koma ya ciko mata ruwa a botiki da kofi ya kawo mata yayi-yayi taci kosai ta sha kokon, tasha ruwa. Idan zata yi alwalla ga ruwa a bokiti taki magana. Yayi da Hausa, yayi da turanci, ya burkuta mata dan abunda ya sani da Larabci da Fulatanci wai ko ta daina jin Hausa abu ya faskara Iman dai kallonsa take. Daga karshe ya fashe da kuka, yayi kuka har ya gaji ya tashi ya taho gida.
Mahaifinsa da Najib sun yi masa tambayar duniyar nan yaya Iman? dan takaici yaki amsa musu, ya kwanta yayi shiru sai shi sai abunda yake damunsa a zuciyarsa. Haka abincinsa na rana ana kawo masa ya dauka ya kai mata na safen nanan ko taba shi bata yi ba, tana nan zaune a bayan kofa inda ya barta. Ya dauke na safe ya ajiye mata na rana ya tafi. Daya kawo na dare sai ya tarar dana rana shima bata ci ba. Abun yayi matukar tayarwa da Suhaif hankali musamman irin duhun dakin daya barota dare yayi. Ita kadai ya shiga wasi-wasi anya kuwa Iman dinsa ce wannan ko kuma ba mutum ba ce daman? Ina son Iman, Iman ina sonki. Karki min haka Iman. Karki koma wata halittar da baza mu iya zama tare ba. Suhaif ya fada a baiyane yayin da yake kwance a dakinsa hawaye yayi masa kawanya. Najib na gefensa sai kawai ya dube shi ya girgiza kai don tausayi.
Haka Suhaif da Iman suka kasance kullum zai kai mata abinci sai uku a rana haka kuma zai dawo ya dauki kayansa ko loma daya bata yi ba. Haka zaiyi maganar duniyar nan baza ta amsa ba. Yanzu kanta a sunkuye yake ko idonta bata dagowa ta kalleshi balle yasa rai zata yi masa magana sun kwana biyu a haka a ran na ukun ne ya shigo gidan da yamma ya tarar da abin al'ajabi. Tun daga bakin kofa ya ga warin takalminta daya da wani abu kuma a jikinsa ja kamar jini. Ya tsaya yana kallon takalmin saiya wuce ya shiga dakin sai yaga warin takalmi a rataye a daure yana lilo ajikin azarar da ke rufin dakin shima jan abu a jiki. Iman na zaune ta juya bayanta wannan karon ta fito daga bayan kofar. Sai Suhaif yaji jikinsa ya dau karkarwa. Muryarsa na rawa ya ce "Iman meke faruwa, me nake gani haka? Kada ki cemun zargin mutane gaskiya be. Ya daka tsawa kamar zararre ya ce "Ki fada min, kimin magana ko ke wacece? Shin ke mutum ce ko ba mutum ba ce? Yau bazan bar dakin nan ba sai kin kasheni na huta. Kina wahalar dani kina tsorata *yan garin nan. Naki yarda a zarge ki, na kasa hakura da sonki. Ki kashe ni na huta da bakin cikin nan, sai ki bar garin ki bar *yan uwana a garinsu. Ko motsi bata yi ba balle ta juyo ta kalle shi. Wannan karon jama'ar dake taruwa suna hangen kofar dakin da Suhaif yake shiga sun fara razana saboda suna jiyo muryarsa da karfi yana fada.
Cikin fushi ya sa hannu ya finciko Iman da karfi ya juya fuskarta. Amma me? Baisan