Showing 27001 words to 30000 words out of 178828 words
Chapter 10 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt
ne, ko kaɗan baka darajani, tsakani da Allah kana gani na amma ka tafi bayan ka san gidan a kulle na wuni a titi ni da ɗanka ko kishin iyalinka baka yi, duk namijin da ya san darajar kansa da ta iyalinsa ba zai wofintar da su su wuni a titi b...
Wani gigitaccen mari ya ɗauke fuskarta da shi, da yake marin ya je mata ne a bazata sai ta ji tamkar ba da hannu aka mare ta ba, marin da Kalifa ya gani ne ya sa ya ruɗe ya fashe da wani kuka ya yi kanta ya je bayanta ya ƙanɗame ta har lokacin yana kuka, bata kula Kalifa ba duk da kukan nasa yana taɓa mata zuciya. Tana dafe da kumatun da ya mara ta kalle shi idanunta taf da hawaye ta ce
"Ni ka mara Nasir?"
Kamar zai kai mata wani marin ya ce
"An mare ki fitsararriya ko za ki rama ne? Har ni za ki ce ban san darajar kaina ba, kuma wallahi sai na faɗawa wannan uban naki ya gargaɗe ki don zai iya zuwa ya ga gawarki matuƙar baki yi wa bakin ki linzami daga furta min kowace kalma ta zo bakinki ba" Yana gama faɗar hakan ya juya ya nufi falo, Kalifa ta ɗauka har lokacin yana kuka da alama tsorata ya yi da marin da aka mata tana ɗaukansa ya maƙalƙale wuyanta bata san lokacin da ta fashe da kuka mai sauti ba. Ta jima tana kuka mai cin rai kafin ta yi shiru ta goge hawayen, jin Kalifa ya yi shiru ya kwantar da kansa a kafaɗarta, sai ta duba sai ta ga ya yi bacci haka ta kawo shi falon ta kwantar da shi a kan kujera ta koma ta yi alwala ta zo ta kabbara sallah.
Lokacin Nasir yana bedroom, sai da ta yi azzahar da la'asar tana yi tana hawaye duk sujadar da ta kai sai ta faɗawa ubangiji damuwarta a kan ya magance mata, tana shirin miƙewa ta yi mageriba sai ga Nasir daga bedroom ɗin kamar an jefo shi, gabanta ya zo ya tsaya yana riƙe da wayarsa da take ringing da alama wani yake kira don wayar a handsfree take ma.
Kamar daga sama sai jin muryar Baba ta yi yana cewa
" Assalamu alaikum malam Nasiru mutumin kirki" Wani murmushin gefen baki Nasir ya yi kafin ya haɗe rai kamar Baban yana ganinsa ya ce
"Ni wallahi Baba ba na cikin yanayin da zan amsa sallama gabaɗaya raina a ɓace yake"
Buɗar bakin Baba sai ya ce
"Sadiya ce ko? Wannan yarinya mai ya sa bata jin magana wai, haka fa ta kwaso jiki wai wuni ta zo gidan nan na korata ɗakinta da tsakar rana shi ne kuma da ta dawo ta ɓata maka rai" Sosai Sadiya ta ji duk ta muzanta dole Nasir yake mata abin da ya ga dama saboda mahaifinta shi yake bashi kowace dama, shi yake zubar da kima da darajarsa, shi ya sa ba ya siya mata mutunci bata san wane irin uba ne ta samu ba.
Nasir ba yabo ba fallasa ya ce
"Ai Sadiya bata san darajar miji ba ko kaɗan, ban da zagi da baƙaƙen maganganu babu abin da take a gidan auren ta, yanzun nan ta gama cewa ban san darajar kaina ba da ta iyayena" Ya faɗa cike da ɓacin rai, Sadiya jin har da ƙarya ya shirga bata yi mamaki ba da ya yi haƙuri ma in dai Baba ne a kan a samu matsalar da za ta koma masa gida ba sai da ƙarya zai mata faɗa ba.
Baba ya ce
"Bata wayar" Wani kallo Nasir ya mata yana wani ƙanƙance ido irin na fitsararru ya miƙa mata wayar tana ƙoƙarin danna wayar Nasir ya katse ta da faɗin
"Kar ki kuskura ki cire min waya a handsfree ki bari in ji, idan ma shi yake ɗaure miki tsantsa ki rainani" Yana gama faɗar haka ya koma kan kujera ya zauna tare da harɗe ƙafafu.
Baba ya ce
"Sadiya wallahi ki fita idona in rufe, mijin da ya rufa miki asirin kike zagi, shin wuta balbal kike son shiga Sadiya?" Kallonta ta mayar kan Nasir da ya kaɗa kai alamar ta dai ji rufa mata asiri ya yi.
Kafin ta samu zarafin furta komai Baba ya ci gaba da cewa
"Wallahi idan ba so kike in zo har gidan in saɓar miki ba ki masa biyayya ko wuta ya ce ki faɗa ba dole ki shiga ba Sadiya tun da mijinki ne aljannarki tana ƙasan ƙafafunsa, kin samu Allah ya tarfawa garinki nono kin yi aure amma kike tada fitina da dai ban san ki da haka ba ko ƙawaye kika samu suke hure miki kunne?" Jin Baban ya dakata ta gane kamar ya bata damar magana hakan ya sa ta ce
"Baba tun da na dawo yana ganina fa ya tafi da mukullin a titi muka wuni sai yanzu ya dawo kuma bani da damar da zan nuna ban ji daɗin abin da ya yi min ba sai ya kai min hannu? Marina fa ya yi Baba yana ta faɗa wa iyayena maganganu... Cike da faɗa Baba ya katse ta ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba yana ta ɗora mata rashin gaskiya a ƙarshe ya ce idan ya ƙara jin wata magana ta ɓullo sai ya saɓar mata.
Duk abin da ake Nasir yana ji, kawai murmushi yake saki jin Baba ya ce ta ba Nasir haƙuri a kan kunnensa ya ji haka ta buɗe baki ta bashi haƙurin cikin dashashshiyar muryarta, sannan Baban ya ce ta ba Nasir wayar tana jin yadda ya ringa ba Nasir haƙuri tamkar zai ari baki yana ta yi wa Nasir ɗin godiya kamar wanda ya masa kyautar kujerar makka.
Juyawa kawai ta yj ta koma kan sallayar ta fara sallar magriba, tana saddaƙarwa da cewa wannan gidan auren kamar kurkuku yake a wajenta, sai dai ta san ba za ta dawwama a haka ba akwai ranar ƙin dillacin ta san ko ba jima ko ba daɗe sai Allah ya mata sakayya a kan zalincin da Nasir yake mata, ko da bayan ranta ne kuwa.
Bayan ta yi har isha'i ya zo ya buɗe store ya ɗakko mata taliya rabin leda ya miƙa mata, karɓa ta yi ta nufi kicin ɗin ta shiga kunna gawayi don mahaifiyar Nasir ta yi uwa da makarɓiya ta hana ta kunna gas ɗin da Nasir ya saya tana amarya ɗan ƙarami, ta ce ita Sadiya bata dace da amfani da Gas ba saboda a gidansu da icce ake amfani. Dakyar ta samu gawayin ya kama ta ɗora tuwan zafi ta dawo falon, sai ta ji kamar ta rufe ido ta buɗe ta ganta a wata duniya daban. Tun da ya bata taliyar ya fice, ta gama dafawa ta soya manja ta zubo abincin ta ajiye ta ɗauki Kalifa ta ke ta wanke masa ido da baki tuni ya ware don dama yunwa yake ji, haka yake cin abincin kaɓr me saboda yunwa, ita kuwa kaɗan ta samu ta ci shi ma duk babu daɗi.
Haka ta yi shimfiɗa ta kwantar da Kalifa ta shiga ta yi wanka tare da ɗauro alwala ta saka rigar bacci marar nauyi ta yi addu'a ta kwanta har lokacin Nasir bai dawo ba, ganin an kawo nepa ta tashi ta saka cajin wayarta ta koma ta kwanta tana rungume da filo tana ta tunanin lamarin gidan aurenta, rana zafi inuwa kuma ƙuna, hawaye yana ta bin kumatun ta mafita take nema ita dai da za a ji damuwarta a magance mata da da daɗi amma babu mai saurarenka iyayenka kawai burinsu ka zauna a ɗakin miji daɗi da wuya ko da kuwa a wulaƙance ne. Tana ta wannan saƙa da warwarar bacci ɓarawo ya yi awon gaba da ita.
Nasir sai wajen ƙarfe goma saura ya shigo gidan, yana can majalisa da abokai ana ta hira, yana shigowa ya rufe ƙofar gidan ya shigo gidan yana wani bada faɗi, sai kuma ya ga baiwar tashi bata ma falon tsire da coca colan da ya shigo da su ya zauna ya baje a falon ya cinye a shanye lemon ya tashi ya bar mata takarda da robar a wajen. Bayan ya gama abin da zai yi ya saka hannu a aljihu ya fito da wani ƙullin ruwan magani a farar leda ya tula ya shanye ya fito ya jefar da leda, kayansa ya cire daga shi sai singlet da ƙaramin wando ya haura kan gadon bayan ya kashe gabaɗaya fitilun. Kasancewar Kalifa a ƙasa take masa shimfiɗa a kan ƙaramar katifa da yake gidan ciki da falo ne, sai kicin da banɗaki kawai sai kuma ɗaya part ɗin inda ciki da falo sai ɗaki ɗaya wanda an fara ginin an kai linta amma ba a ƙarasa ba. Yana hawa gadon ya kwanta ya miƙa hannu ya shiga tashin Sadiya, cikin bacci ta ji yana buga mata ƙafa ta ɗago jajayen kumburarrun idanunta ta kalle shi ta cikin ɗan hasken farin wata da ya ratso ɗakin.
Cike da gadara babu tausasa murya ya ce
"Haƙƙina na zo karɓa" Ranta ne ya sosu wai mutumin da ya gama ci mata mutumci har marinta ya yi amma yanzu kuma ya zo da wata buƙata, a kasalance irin na wanda yake cike da bacci da gajiya ta ce
"Dan Allah Abban Kalifa ka mini lamuni yau wallahi ba na jin daɗin jikina" Kamar wanda ta watsa masa wuta haka ya zaburo mata ya ce
"In baki taliya ki cika ƙundunki ki shi ne tawa buƙatar ba za ki biya min ba? To in dai wancan taliyar da na ga kin ajiye mini a ƙaramin filas ce kike yi wa ki je ki ɗauka ni nama da lemo na sha, idan kin cinye sai ki zo ina jiranki da alama ƙoshi ne baki yi ba shi ya sa kike mita" Cike da ƙosawa da kalamansa ta ce
"Ni ba yunwa nake ji ba kawai dai zuciyata ce babu daɗi"
Zaune ya miƙe ya saka hannu ya daki kan katifar kan gadon ya ce
"Ko zuciyarki da daɗi ko babu wannan ke kike sakawa kanki kuma ke kika ga za ki iya, ni dai yanzu haƙƙina dole ki bani tun da sadaki na bayar" Tun da ya yi wannan furucin bata ƙara furta komai ba ya cire kayan jikinta, babu wani ɓata lokaci ya shiga biyan buƙatarsa ya daɗe yana abu ɗaya sai da ya gaji don kansa ya ƙyaleta, ita kuma tana kwance kamar gunki don dama babu wani abu da take fuskanta a lamarin don damuwa ta gama yi wa zuciyarta katutu, shi kuma lamarin mu'amalar aure ana son gabatar da shi a lokacin da ake cikin walwala farinciki haɗe da annashuwa.
*IBRAHIM*
Kafin ya ƙarasa gidan su Jidda ya haɗa uban gumi sharkaf abin ka da wanda ya saba rayuwa cikin AC gida AC mota AC office ma AC.
Ko da ya zo bai ƙarasa saitin gidan ba daga ɗan can gefe ya tsaya yana hangar ƙofar gidan, sai lazimi yake a zuciyarsa, yana addu'ar Allah ya sa ya dace.
A can cikin gida kuwa Aliya ce take gwada wata doguwar rigar abaya maroon da takalmi haɗe da wata jaka sai murna take tana cewa
"Gaskiya Kasim ya iya zaɓe"
Umma ta yi karaf ta ce
"Wannan ai za a je da shi, kin ga duk da ba mai arziƙi ba ne ai yana da wadatar zuciya, daga ganinsa irin mazan nan ne masu bautawa mace, kika dai yadda yake miki wahala komai ya samu ke yake yi wa"
Aliya ta ce
"Umma ai wanna da kike gani bawan mace ne"
Umma ta ce
"Ai tun da dai yana da karatun digirinsa digirgir kuma yana da ƙashin arziƙi daga gani, gashi yana sonki yana bauta miki tabbas in kika aure shi kakarmu ta yanke saƙa, wuyarta ya samu aikin gwamnati da takardun nan basa ai shi kenan kin zama babbar mace" Wani uban tsalle Aliya ta daka tana murna tana sanar da Umma Kasim ɗin ma ɗazu ya ce zai saya mata sabuwar waya. Da gayya suke ta maganganun nan da yada magana duk abin da suke Jidda tana jin su, ita damuwarta ma da jiya da daddare Abba ya tara su ya ce kowacce ta fitar da miji shi bai san cewa Jidda bata da wani tsayyaye ba, ita kuma tana jin nauyin sanar da Abban.
Ta yi nisa a tunani Umma ta ƙwalla mata kira, tana fitowa ta saka ta wankin kaya, haka ta karɓa don dama yau Ummar ce ta hana ta zuwa islamiya saboda aikin gidan. Aliya ce ta gama saka kayan gabaɗaya a leda ta cewa Umma za ta je gidan su Amatullahi ta kai ta nuna mata Umma ta ce
"Yawwa maza kula ki je ki nuna mata kin kece raini kuma kina da mijin da xa ki aura na nunawa sa'a" Ta faɗa tana kallon saitin Jidda da ta duƙufa wajen wankin zanin Ummar. Ko da Aliya ta ɗauki ledar ta fito ƙofar gidan, Ibrahim daga can inda ya tsaya ya hango ta, kasancewar bai shaida ta ba sai ya taho domin yana son ya tambaye ta ko Jidda tana ciki, bai gane ta ba sai da ya zo dab da ita, ita kuma Aliya a lokacin da ya ƙaraso tana ƙoƙarin kara waya a kunne don Amatullahi take kira za ta ce mata gata nan za ta nuna mata kaya. Ganinsa ya sa ta fasa kiran wayar ta kashe tana ƙare masa kallo, tabbas ko daga bacci ta tashi ba za ta kasa shaida wannan fuskar tasa ba.
Fuska ta yatsina tana masa kallon ƙwaf, shi kuma gabaɗaya kansa ya kulle da ya ganta don tabbas ya shaida ta ita wacce ta ciwa direbansa mutunci ranar nan. Gabaɗaya ma sai bakinsa ya ƙi bashi haɗin kai wajen yin sallamar da ya yi niyyar mata, bare a kai ga tambayar da zai mata a kan Jiddar tana cikin gidan.
Aliya kuma sai ta shiga masa wani kallon raini tana yatsina, gabaɗaya sai ya tsargu da kallon nata amma sai bai ce mata komai ba, cike da mamaki da gatsali ta ce
"Oho sai yanzu na je ghana, kai duniya mutane sai a barsu, wato dai Allah ya tona maka asiri ashe dai ganin kana da kyau shi ya sa kake aron mota da kaya masu kyau kana yaudarar ƴaƴan mutane ko? Har da aron direba da yake janka a mota, wato ka zaci ba zan gane ka ba, to ta Allah ba taka ba wannan ai kai ne a wanki gara!" Ta faɗa tana wani zagaya shi, gabaɗaya sai Ibrahim ya kasa magana ita kuma ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, har da faɗin ɗan talaka dama bai iya samun wuri ba wato har da cewa wa yake nemanta lokacin da ta je wajensa a motar ashe dai duk kanwar ja ce shi ma dai talaka ne bai ajiye ba bai bayar ajiya ba.
Shi dai yana kallon ta tsabar mamaki ma ya rasa mai zai ce.
Ganin haka sai ta ce
"Shi ne ka lallaɓo koɗaɗɗun ƙafafunka da wasu tsoffin kayanka sa suka gaji da wanki, to wallahi ni na fi ƙarfinka ne, kar ma ka ɓata lokacinka wajen mini magiya ko roƙona don ina cikin mutanen da suke cewa da wuya ta kar su ai gwara daɗi ya kar su"
A can cikin gida kuwa Umma ce ta ce Jidda ta ɗauki bokiti ta fita famfon waje ta ɗakko ruwa ta ƙarasa wankin, da yake ruwan ya ƙare, duk da akwai mai ruwan da yake kawo musu ruwa amma saboda ta ga Abba ba ya nan ta aike ta ɗakko ruwan, haka ta ɗauki bokitin ta fito ba don ta so ba.
Aliya tana cikin masa wannan maganar har wani nuna shi da yatsa take a daidai nan ne Jidda ta fito, sai da gabansa ya buga da ya ganta sanye take da wani blue ɗin hijabi har ƙasa hijabin yana da hannu sai bokiti a hannunta fuskarta babu walwala. Tun da ta fito kallo ɗaya ta musu ta wuce da yake wajen famfon kusa da gidan da yae kusa da gidansu ne ta tara ruwan ta ciko ta ɗakko.
Ta zo za ta shige gida ganin abin da Aliya take yi wa Ibrahim sai ta ce
"Haba Aliya, a titi kike wannan ɗaga muryar?"
Cike da ɗaga murya ta ce
"An yi ɗin uwar pan shishshigi" Juyawa ta yi ta shige gidan, shi kuma kallon ta kawai yake yana son ganin gudun ruwanta, sai da ta gama masa ɗiban albarka ta ce
"To a yi gaba ko a samu wata dai amma wannan Aliyar sai Kasim!." Tana faɗa ta juya ta tafi tana wani juya mazaunan da su da babu duk ɗaya.
Gefe ya koma yana ƙarewa jikinsa kallo yana mamakin cewa kenan dai shi talaka a wajen wani shi ba komai ba ne, sannan wasu suna ganin duk rashin mutuncinka in har kana da kuɗi to kai mai kirki ne in kuma baka da shi da kai da babu duk ɗaya, dama ya fahimci cewa Aliyar nan ƴar son banza ce don ranar ma a idanunta ya ga son banza ƙiri ƙiri.
Ko da ta je gidansu Amatullahi nan ta shiga bata labarin Ibrahim suka ringa zaginsa suna ce masa matsiyaci, Aliya ta ce
"Oh har zan ce in yi saki na dafe da Kasim ɗina ashe dai ba arziƙi ba ne yake kirana tsiya ce"
Amatullahi ta ce
"Humm! Ba ke kike cewa wani kyakkyawa ba ne"
Aliya ta ce
"Ke dai bari a yau na gane cewa duk arahar kunu ta banza ce in babu gaya a ciki" Suka ci gaba da ɗaga kayan Kasim suna zuba masa albarka.
Fitowar Jidda za ta ƙaro ruwa sai ta gan shi jingine