Showing 129001 words to 132000 words out of 178828 words
Chapter 44 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt
babu kofin ya riƙe ƙugunta suka tafi ɓangaren Meenal ɗin.
GIDAN SU ZALIKA
Gabaɗaya Mamy ta gigice hankalinta ya tashi ji take tamkar zai gushe mata domin abu ne da take gani tamkar ba a zahiri ba addu,a take a zuciyarta Allah ya sa mafarki take, domin sai hakan ya fi mata sauƙin rayuwa a ce wannan abin a zahiri ne. Juya kwallin take a hannunta tabbas pills ne, wato maganin hana ɗaukan ciki. Hannunta yana karkarwa ta buɗe kwalin ta ga duk an ɓalli maganin alamar an sha kenan wato an yi amfani da shi.
A fili ta furta
"Allazina iza asabathum musibatun ƙalu innalillahi wa inna ilaihi raji'un"A take ta ji wasu hawaye masu zafi suna zubowa daga kwarmin idanunta zuwa dakalin fuskarta, kuka take sosai marar sauti ko ta ji sauƙin abin da take ji a ranta, yau ita ce da matsalolin gidan miji sannan mijinta ya yi watsi da ƴaƴansa tamkar ba ya raye, ya bar mata ragamar komai kuma duk da tana iya bakin ƙoƙarinta amma sai da aka fara samun tangarɗa a lamarin tarbiyar a fili ta furta
"Ina godiya a gareka ya ubangiji da wannan jarabawar, ya Allah ka bani ƙarfi da ikon rungumar duk wata jarabawa da za ka jarabceni da ita, na san ka na ji kuma kana gani ya rabby ka kawowa baiwarka mai rauni ɗauki bani da tsumi bani da dabara" Ta faɗa tana rushewa da wani sabon kukan, ta jima tana kuka har sai da ta ji zuciyarta ta ɗan saki, duk da ta san abu ne mawuyaci wannan mummunan dafin ya fita daga zuciyarta amma dai tana fatan Allah ya yaye mata domin shi babu abin da ya gagare shi.
Maganin ta je ta sanya a drower ɗinta, ta dawo ta ɗauki jakar ta mayarwa Zalika ɗakinta wace har lokacin tana ta shan bacci abinta.
Da safe ta je ɗakin Zalika ta same ta ta fito wanka kana zaune gaban madubi tana shafa mai sannan ga kayan da ta fitar za ta saka a kan gado a ajiye. Ta rufe ƙofar ta je ta samu waje ta zauna bayan ta yi sallama Zalikar ta amsa tana cigaba da abin da take.
Mamy ta ce
"Zalika wajenki na zo ina son magana da ke" Zalika tana shafa powder ta ce
"Ok Mamy" Sai da ta kammala ta zo ta saka kayantw sannan ta zauna a kusa da Mamy tana danna waya.
Mamy ta ce
"Bani jakar can taki zan yi wani abu" Gaban Zalika ya buga kasancewar ta san akwai maganinta a ciki kuma ba za ta so Mamyn ta gani ba. Tana ɗan nuna alamar tambaya ta ce
"Mamy jakata kuma mai za ki yi da ite?" A nan ne Mamy ta ji wani abu kamar kibiya ya caki zucuyarta, domin kuwa hakan yana nuni da cewar maganin ne Zalika bata so ta gani, hakan yana nuni da cewar Zalika tana neman maza, duk da Mamy ta san a jakartw ta gani amma zuciya irin ta uwa gani take ba maganin hana ɗaukan cikin ba ne duk da ta san haka ne amma so takr ta buɗe idonta ta ga mafarki ne hakan zai zama mafi sauƙi ga ruhinta.
Mamy tana danne abinda take ji ta ce
"Mene ne a jakar da na ga kin razana? Ba handout ne da biro da wasu abubuwan amfani na makaranta ba, mene ne baƙo a ciki, ko kin manta tun kina nursary ne nake haɗa miki school bag ɗinki idan kin dawo ma ni nake adana miki ita yaushe abubuwan suka sauya kuma" Zalika tana ɗan diriricewa ta ce
"No babu komai Mamy kawai dai ina sauri ne na je na yi break fast sannan ina da lacture ne ba na son na makara" Idanun Mamy suka cika da ƙwalla tana kallonta ta fito da kwalin hannunta da ta ɓoye ta buɗe tafin hannunta gaban Zalika ne ya buga da ƙarfi tana kallon kwalin hannun Mamy inda jikinta ya ɗauki karkarwa tana ƙoƙarin baɗa laɓɓanta don ganin ta ce wani abu sai dai gabaɗaya alamomin rashin gaskiya sun bayyana a gare ta a inda Mamy ta gama fahimtar cewa tabbas ba mafarki take ba Zalika dai ƴarta tallin tal guda ɗaya ƴa mace wacce daga ita bata da wata ƴa macen sai Mubin ita ce ta san namiji, namijin ma ba mijin aurenta ba namijin titi shin zarginta gaskiya ne ? Idan ba gaskiya ba ne da mai zalika za ta kare kanta?
A take zuciyar Mamy ta shiga raya mata
'Lallai akwai aiki ja a gaban iyaye mata wajen sanya idanu a rayuwar ƴaƴansu yanzu a ce har yarinya tana iskanci a waje amma uwarta bata ankara ba, shin ina fitar budurci da ake gane cra wannan ne karo na farko da yarinya ta fara sanin ɗa namiji? Amma a ce uwa bata lura ba duk da kasancewata uwa mai sanya idanu a rayuwar ƴaƴana amma har abu ya yi nisa ban sani ba, kenan wayon ƴaƴan yanzu har ya kai su ɓoye abin da babba zai kasa ganewa!
Mad about you
Delina de merly
My way intense
Gucci guilty men
Vanilla 28 kayali
Khamrah
I want choo
Creed aventus
Amber oud
Sugar baby
Club de nuit
Olympea
Stronger with you
Reef 33
Dior sauvage
212 VIP man
Blue de channel
Pink shiffon
Jadore
Bombshell
Pure seduction
Versace bright crystal
La vie est belle
Versace Eros man
*🎉 PROMO NA ƘARSHEN SHEKARA GA MATA! 🎉*
*Ki bar tsohon shekara da matsala, ki shiga sabuwa da gyara!*
Mun yi sabbin kaya don nuna soyayya da kulawa ga wanda suke son mallakar ɗaya daga cikin waɗannn abubuwan ko kuma duka.
*Ga kayanmu masu inganci da kike bukata:*
1️⃣ *Maganin Matsi Gam-Gam* Don matsi 1500 maimakon 2500
2️⃣ *Maganin Sanyi* Yana kawar da dukkan nau’in infection da wari, ƙaiƙayi, ƙuraje rikicewar al,ada 2500 maimakon 4k.
3️⃣ *Sabaya 3 in 1* Gyara breast, hips sannan tana gyara jiki 5k maimakon 7k.
4️⃣ *Maganin Gyaran Breast* Yana ciko da breast, ga masu shirin yin yaye da kuma wanda breast nasu yake buƙatar gyara 3k maimakon 4500.
5️⃣ *Daka* Tushen ni’ima 1500 maimakon 2500.
🎁 PROMO NA MUSAMMA
Ranar ƙarshe 31 ga Disamba, 2025
Ki gyara jikinki, ki faranta ran mijinki, ki shiga sabuwar shekara da armashi.
MAMAN AFRAH
09025576222
https://chat.whatsapp.com/DDmSp3AUB7gJnJQLnau59V?mode=hqrt1
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 2️⃣4️⃣
JIDDA
Da matuƙar tashin hankali a tattare da ita take faɗin
"Lafiya mai ya faru?" Ta faɗa duk ta diririce saboda yadda ta ga mijin nata hankalinsa a tashe. Bai bata amsa ba don hankalinsa yana ga wayar da yake amsawa sai ta ji yana faɗin
"Gani nan Mummy" Yana gama wayar ya yu hanyar fita daga ɗakin cikin sauri lura da ta yi kamar hankalinsa ya bar jikinsa ta yi saurin riƙo rigarsa ta baya, tare da yin sauri ta sha gabansa suna fuskantar juna tamkar za ta saki kuka ta ce
"Ina tambayarka ko lafiya amma shi ne baka faɗa min ba" Kallonta ya yi sai kuma ya ga ta bashi tausayi hannunsa ya kai ya shago gefen fuskarta ya ce
"Ki yi haƙuri hankalina ne ya tashi, Mummy ce ta ce Daddy ya yanke jiki ya faɗi " Cike da tashin hankali ta ce
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Ƙofar ya buɗe suka fito dagaɗaya ta ga ya fice a hayyacinsa, suna sakkowa ƙasa ya nufi hanyar fita Jidda ta ce
"Ka jirani in ɗakko hijabina" Bata jira cewarsa ba ta yi hanyar ɗakinta sai gata ta ɗakko hijabi a hannu a falon ta shiga sakawa tana gama sakawa sai ta ga Baba Kuluwa riƙe da plates za ta shiga kicin ta buɗe baki ta ce
"Baba zan fita za mu je gidan Mummy" Baba Kuluwa ta ce
"Lafiy Hauwa'u" Jidda ta ce
"Daddy ne ba ya jin daɗi" Fatan samun lafiya ta masa Jidda tana juyawa sai ta ga Ibrahim ɗin ba ya nan da sauri ta fita ganin ya bar ƙofar ma a buɗe. Ko da ta fita ta same shi har ya shiga mota, tana zuwa ta ce
"Ka ba direba ya kaimu na ga kamar ba za ka iya tuƙin ba" Cikin sanyin murya ya ce
"Zan iya" Bata sake magana ba ta buɗe ta shiga mai gadi da suke zaune suna hira da sauran ma'aikatan gidan ya tashi buɗe musu get kowa yana ɗaga musu hannu cike da girmamawa suka fita, gidan Mummyn suka kama hanya ko magana Ibrahim ba ya yi kasancewar jin muryar mahaifiyarsa da ya yi tana kuka a waya ƙaran wayarsa da take ajiye a gefe ne ya sanya Jidda ɗaukan wayar ta miƙa masa ganin sunan Mummy da sauri ya danna ya kara a kunnensa, ji ya yi Mummy tana faɗa masa sun tafi asibiti adirshin asibitin ta faɗa masa don haka ya juya kan motar suka kama hanya.
Ko da suka zo asibitin sun je ɗakin da aka kwantar da Daddy yana kwance lifet kamar gawa sai likita da yake sanya masa ruwa a hannu Mummy tana zaune a gaban gadon ta kifa uban tagumi idanunta jajawur. Haka su ma suka tsaya suna ganin ikon Allah. Bayan likitan ya gama abin da zai yi sai ya ce da Ibrahim su je office suka fita aka bar ɗakin daga Mummy sai Jidda da take ta faman ba Mummy baki.
Mummy ta ce
"Jidda lafiyarsa ƙalau fa, babu abin da yake damunsa, muna hira kawai miƙewar da zai yi ya yanke jiki ya faɗi sumamme" ,Jidda ta ce
"Subhanallah ki yj haƙuri Mummy in sha Allahu zai samu lafiya" ,Mummy tana share hawayen da ya gangaro mata ta ce
"Allah ya sa amma na tsorata da lamarin nan, gaskiya rayuwa abin tsoro ce "
A haka Ibrahim ya shigo direban gidan Mummy yana biye da shi riƙe da ledar magunguna sai kuma katan ɗin ruwan roba.
Har lokacin Daddyn bai farka ba don dai yanzu numfashin sa ya dawo kawai dai bacci yake, Ibrahim ya ce zai je masallaci ya yi sallah direban ma dama yana ajiye ledojin ya fita Jidda ma sallar ta yi ita dama Mummy tana hutun sallah ne
Wajen ƙarfe tara da rabi Mummy ta ce au tafi gida saboda Jidda sai Ibrahim ya ce zai kaita gidan ya dawo ita ma Jidda ta ce a asibitin za ta kwana amma Mummy ta ce a kaita gida..
Suna tafiya tana ta kwantar masa da hankali ga tausayinsa ya kamata, ko abinci bai ci ba ga rashin lafiyar Daddy mai gadi yana buɗe musu get ya shiga da motar mai gadi yana rufe get inda mai ba flowers ruwa ya taho da sauri ya zo yana ƙoƙarin buɗe masa motar cikin girmamawa amma sai ya dakatar da shi yana faɗin ba fitowa zai yi ba. Jidda ce ta juya ta kamo hannunsa ta sanya cikin nata ta matsa yatsunsa tare sa rausayar da kai ta ce
"Annurin zuciyata idan fuskarka ta zama babu walwala sai na ji komai ya sare mini, sannan sai na ga gabaɗaya duniyar ta mini ƙunci tare da yi mini wani irin duhu" Iska ya fesar daga bakinsa ya riƙe sitiyarin motar da hannu ɗaya duk da ba tuƙi yake ba, ya saka ɗaya hannun da take murzawa ya riƙe nata gamgam ya ce
"Ki bari har na dawo daidai Jidda yanzu damuwar Mummy da halin da Daddy yake ciki ya rufe komai amma ki sani zuciyata a buɗe take tana sane da ke sannan da ke take rayuwa"
Kallonsa take yadda fuskarsa ta yi fayau ta ce
",Plss mu shiga ciki na haɗa maka shayi mai ɗan kauri ka sha" Kai ya shiga kaɗawa alamar ba zai sha ba, amma ganin ta shagwaɓe fuska sai ya ji yana so ya faranta mata hakan ya sa ya yi na,am sai suka fito a tare tana riƙe da hannunsa suka shige cikinm gidan, a falon ƙasa ta masa masauki a kujera ta nufi kicin ko hijabin bata cire ba, shayi ta haɗo masa ta ɗoro a ƙaramin kofin tamgaran da ɗan ƙaramin plate ɗin kofin ta zo tana juyawa da tea spoon.
Ko miƙa masa bata yi ba ta shiga bashi a baki har sai da ta ga ya shanye tasss sannan ta ajiye a ƙasan kafet tsaye ya miƙe yana mata sallama ya juya zai fita yana dab da fita daga ƙofar falon ya juyo sai kuwa ta ƙarasa da sauri ya buɗe mata hannunsa ta shige ya rungumeta sannan ya yi kissing goshinta ya ce
"Ni zan tafi sai Allah ya kaimu gobe" Amsa masa ta yi ya ɗaga mata hannu alamar bye-bye ita ma ta ɗaga masa ya fita.
Tsakiyar falon ta koma ta aunkuya za ta ɗauke kofin shayin sai ga Saude ta zo ta karɓa ta je kicin ta wanke ta ajiye, ta fito sai ta ga Jidda zaune hakan ya sa ta mata ya mai jiki bayan ta faɗa mata da sauƙi sannan ta masa fatan samun sauƙi.
Sama ta haura jim kaɗan ta fito da kayan tuwon nan bayan ta ɗauke cokali da tuwon da Ibrahim ya gutsiro zai ci lokacin da Mummy ta kirashi wanda kiran ya yi sanadiyyar rasa nutsuwar zuciyarsa sanadin rashin lafiyar mahaifinsa. Tana sakkowa ta yi kiciɓis da Saude hakan ya sa ta ba Saude kayan tuwon ta ce ta kai kicin, karɓa Saude ta yi Jidda tana komawa sama Saude ta shiga kicin har da rufe ƙofa ta tsaya ta ƙarewa tuwon kallo tana ganin gurbin da akamcire a jikin tuwon wanda da alama cokali ɗaya ne kuma ga gutsuren lomar nan a gefen plate ɗin, wata ajiyar zuciya ta sauke tana hamdala don ta san akwai abin da Aliya ta yi a saman, wanda tana zaton hakan zai kasance wani abu ne ta barbaɗa a miyar tuwon sannan zarginta da take ta rayawa a ranta cewar cokali duk da ba za ta iya hasashen ainihin abin da ya yj silar ganin cokali a bra ɗin Aliya ba amma kawai ta gwammace ta salwanatar da cokalin haka ta juye tuwon duka da miyar a baƙar leda ta wanke kwanukan ta gyara kicin ɗin. Ta fita da wata doguwar wuƙa a hannunta da kuma ledar da ta sauye tuwo da miyar sai wannan cokalin. Sai da ta je garden ɗin gidan can tsakanin wata bishiya ta haƙa babban rami ta jefa ledar da cokalin ta yi addu,a ta mayar da ƙasar ta rufe wajen sai da ya yi kamar ba a taɓa tona wajen ba, sannan ta bar wajen tana jin wani shauƙi.
Ko da ta yi shirin kwanciya ta saka kayan bacci pink colour masu laushi sosai ta shafa turare, ta hau gadon ta kwanta sai ta ji gabaɗaya ɗakin da gadon sun yi mata girma kasancewar babu tauraron zucuyarta Ibrahim.
Filonsa da yake kwanciya ta janyo kusa da ita tana shaƙar ƙamshin turarensa tana jin tamkar tana kusa da ita tun da basu taɓa nesa da juna ba tun da suka yi aure.
Daga ƙarshe ta ɗakko ƙafafunta ta sakko ƙasa ɗakinta ta nufa ta je ta kwanta a ganinta za ta samu sauƙi salama da sasaauci na tunanin Ibrahim da take ji tamkar shekara suka yi ba sa tare da shi.
Aliya tun da ta gama waya da Amatullahi sai ta kira Umma tana sanar da ita cewa aiki ya kammala, Umma ta ringa rawa da juyi a ɗakinta tana jin daɗin yau sun hau turbar zama masu arziƙi. Ko da Kasim ya dawo shi kansa ya yi mamakin ganin yadda fuskarta take a washe bata sai wani nan nan take da shi, bai san cewa tana yin hakan ne don ta hango tsantsar wata dama da za ta samu a rayuwa. Indomie ta dafa masa yau don badangarci da hannunta take bashi a baki ba ma da fork ba. Gabaɗaya daɗi ya cika Kasim ya kalle ta yana murmushi ya ce
"Haƙiƙa ni a cikin maza ɗan gata ne a wajen matata, matata tana sona!" Ya faɗa yana buɗe baki ta bashi indomie ɗin. A fili ta ce
,
"Idan miji bai zama ɗan gata a wajen matarsa ba a ina zai zama" Ta faɗa tana kallonsa.
A zuciyarta kuma ta ce
'Wanda dai nake so da muradi yana can sai dai very soon zai dawo gare ni tabbas zan murza kan naira har sai ta tabbatar ta zo hannun da za a bata wahala" Suna ta hira har suka kammala don ita ko a bakinta ta ce a ƙoshe take wani irin farinciki take ji irin farincikin nan mai hana ka cin komai duk da dama bata tare da yunwa.
Ko da suka zo kwanciya ma bayan ta sha maganinta a ɓoye na hana ɗaukan ciki tana rayawa a ranta cewa ta kusa daina shan magani da zarar ta auri