Showing 144001 words to 147000 words out of 178828 words

Chapter 49 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt

18 Dec 2025

1434

sauran. Tana jin lokacin da su Husna suka buga gidan aka buɗe musu wajen ƙarfe takwas kuma Meenal ce ta buɗe tana jin yadda take musu masifa wai sun ɓata lokaci ba su zo da wuri ba, haka ta ji suna bata haƙuri kamar wata uwarsu.


Har suka gama suka tafi bata fito ba Kalifa kuma har lokacin bacci yake kasancewar jiyan ya yi ta gijifgijiftu a gidan kaka, saboda gajiya shi ya sa bai tashi da wuri ba. Bayan tafiyarsu sai ta gyara ɗaki ta share tas ta yi goge goge sai ta kunna turaren tsinke, tsakar gidan ta shiga sharewa, sai ta ta je tana tattarawa sai kawai ta ga wani abu da ya bata mamaki, da sauri ta kai hannu ta ɗakko tana juya shi a hannunta gabanta ya buga da ƙarfi domin tabbas ko tantama babu zip ɗin jakarta ne, abin da ya sa ta game shi zip ɗin jakarta daga aarshensa a ɗan lanƙwashe yake ba komai ya lanƙwasa shi sai wani lokaci ya cije ya ƙi ziguwa shi ne ta maƙala shi jikin ƙofa ta cisga da ƙarfi shi ne ya lanƙwashe daga wajen kamawar, abin da ya bambanta wannn da nata shi ne wannn baƙiƙƙitin da shi kamar wanda aka ƙona shi.


Tsaye ta miƙe tana aara ƙare masa kallo fitowar Nasir da Meenal daga ɗaki ya sa ta yi saurin juyowa, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kai kamar ya ga kashi sai dainita ba wannn bane a gabanta saboda yanzu abinnda yake gabanta na mamaki da al,ajabi ya danne komai. Ba ta san lokacin da ta ce

"Wallahi wannna ƙarfen zip ɗin jakata ne" Dududdummm gaban Meenal ya harba da ƙarfi amma saboda ƴar bariki ce sai ta basar tana mayar da kallonta kan Nasir tana wani kashe murya shi kuma yana biye mata bai ma damu da maganar da Sadiyar ta yi ba sai da Sadiya ta ankara da abin da ta ce sannan cike da sanyin murya ta ce

"Ina kwana Abban Kalifa, an tashi lafiya" Ta faɗa a tare don gabaɗaya ta shiga ruɗu da tunanin yadda aka haihu a ragaya.

Amsawa ya yi kamar an masa dole ganin haka sannan kuma ta ga alamar Meenal ba za ta bari su yi maganar ba sai ta ce

"Wallahi jakata da nake ajiye kuɗin cinikina ne ta ɓata rasa ta na yi kuma abin mamaki yanzu da nake shaarar nan sai na ga ƙarfen zip ɗin a can" Ta faɗa tana nuni da inda ta ga zip ɗin. Meenal kai ta kawar gefe domin kar a hango jirginta shi kuma tamkar ta faɗa masa saƙon mutuwa ya gaɗe girar sama da ƙasa ya ce

"To ko ni ne na ɗauka?" Ya tambaya cike da gatse. Kai ta girgiza alamar a,a ganin yana neman ɗora mata jakar tsaba kaji su bi ta sai ta ce

"Kawai dai ina mamaki ne wallahi abin kamar almara"Hankalinsa ya mayar kan Meenal da take magana cikin muryar ɓaci duk ta wani shagwaɓe fuska.


Meenal tana ta mamakin yadda aka yi da ta ƙone jakar bata ɗauke da ƙarfen zip ɗin ba.

Ya fara tafiya Sadiya ta ce
",Ina da magana "

Ya ce

"Za ki iya faɗa tun da babu bare a nan" Kallon fuskar Meenal ta yi wacce ta murmusa fuskarta ta nuna alamar murmushin ƙeta wato da alama ta zama ƙarfen ƙafa komai ma a gabanta za a faɗa. Daurewa ta yi tana danne takaicin da suke ƙunsa mata wanda watarana sai zuciya ta zuga ta a kan ta rama sai kuma wata zuciyar ta ce ta ƙyale watarana saj labari!.

Tana kallon yanayin fuskarsa ta ce

"Gawayina ne ya ƙare ɗazu ma dakyar ya isa na yi amfanj da safe... Numfashin ta ya tara da faɗin

"Sadiya ni ba na son almubazzaranci ta yaya za a yi gawayjn a ce har ya ƙare to ni ba ni da kuɗj yanzu sai dai ko in bada itace a kawo miki" Ƙwalla ta taru a idanunta bayan da gawayi take amfanj Meenal tana amfani da gas sannan kuma tana cancantawa amma kuma yanzu a mata maganar ita ce jin hakan Meenal ta ce

",Gas ɗina ni ma fa ina ga ya kusa ƙarewa" !Wani irin washe baki ya yi ya ce

"Tohm zan saka miki idan na dawo" ,Tana masa bye bye ya fita ya tafj Sadiya kuma ta kasa motsawa ma daga wajen, wannan abubuwa ne masu tarin yawa da suke nuni da cewa Nasir ya gaji da ita, sai dai tana jiran ranar da Allah zai kawo mata mafita a lamuran nan. Tana jin yadda Meenal take dariya har da ƙyaƙyatawa da ta ga ta nufi ɗaki, ko da ta shigo ɗakin zaman dirshan a falon tana tunanin ƙarfen zip ɗin da ta tsinta ta rasa ta yaya haka ya faru ta rasa kalar tunanjn da za ta yi, iya hasashe da tunanin ta bata samu amsar ba da a ce a buɗe ɗakinta yake za ta zargi komai ma sai dai a rufe yake sannn da mukulli ta fita idan ba aljannu ba waye zai ɗauka?. Kukan da Kalifa ya saki ne ya dawo da ita daga tunanin da take.

Zuwa can aka zo sayen manja ganin babu ƙullal ne a leda saj ta buɗe jarkar ta tsiyaya a za ta ƙulla saj ta ji warin kananzir cike da faɗuwar gaba ta kai hancinta jikin ƙofar amma sai ta ji warin tamkar ta shinshina jarkar kananzir, da sauri ta saki murfin jarkar ta nufi ɗayan ta farin mai gabanta yana faɗuwa ta buɗe amma cikin ikon Allah sai ta ji babu warin hamdala ta yi a ranta tana ta kissima abubuwa a ranta duk da an ce zato zunubi amma kam tana ta zargi a zuciyarta.

Ko da ya tafi ko ƙeyarsa babu bare a samu wanda zai kawo mata itacen da ya ce, da rana dai gari da madara da sugar ta haɗa musu suka sha, tana tausayin Nasir ranar da haƙƙi zai tambaye shi musamman haƙƙin ɗansa Kalifa domin shi yaron ko kaɗan bai san daɗin uba ko kulawarsa ba ga shi koyaushe daɗa wayo yake, ita damuwarta ma yadda yaron idan ya ga ana mata abu yake nuna rashin jin daɗi ta hanyar kukansa ko kuma yake goge mata hawaye yana ambaton Momma Abba ne? Duk da tana iya yinta don ganin bata kuka a gabansa.

Tana tsakar gida lokacin almajirin Meenal yana mata sharar baranda, ita kuma ta kinkimo jarkar man mai warin kananzir sai kawai suka yi ido huɗu da Meenal ta mata dariya, hakan ya sa a ƙufule Sadiya ta ce

"Wai mai kika mayar da ni ne Meenal sai kike kallona kina min dariya kamar wata mahaukaciya kika gani?" Dariyar ta ƙara yi a karo na biyu sai Sadiya ta ce

"Ko mai mutum ya yi ya je shi da Allah domin yana can a madakata yana jiransa duk daren daɗewa akwai mutuwa sannan akwai hisabi shi dai ubangiji ba ya yafe haƙƙin wani a kan wani" Ɗan dum Meenal ta yi sai ta ji ta kasa cewa komai domin zuciyarta ta fara raya mata ko dai Sadiya ta gane ita ta mata sata kuma ita ta zuba mata kananzir a cikin jarkar manja, domin yanayin furucinta ya bayyana kamar dai akwai wani abu.

Ɗakinta kawai ta wuce ba tare da ta ce komai ba. Da yamma Sadiya ta masa waya tw ce za ta je gidan Hajiya bai musa ba don ya san wani neman wajen ne za ta je tun da Hajiya dai ba ra,ayinta take yi ba, sannan kuma ya san tana zuwa za ta dawo a kan sawunta tun da ba ma lallai a ƙara mata magana daga gaisuwa ba.

Ko da ta je gidan Hajiya ta samu Hajiya zaune a gindin murhu tana tuƙa tuwo, sai goge ido take saboda hayaƙi, ta amsa mata babu yabo babu fallasa don su Hibba ma ba sa gidan sai ita kaɗai. Tabarmar da aka shimfiɗa a wajen ta zauna, ko Kalifa Hajiya bata wa magana ba. Sai da ta rufe tukunyar bayan ta gama tuƙawa ta taso ta shiga ɗaki ta jima sannan a shelaƙe ta fito ta zo ta zauna daga can bakin barandar

Sadiya ta ce
"Dama wata magana na zo da ita... Hajiya ta tari numfashin ta da faɗin

"Sadiya ni ba na sin kinibibi da gutsiri tsoma, wace irin magana ana zaune ƙalau dama duk mace ai sai ta yi haƙuri a gidan miji sannan dama idan kika san ma ba ke kaɗai ba ce sai dai ki kauda kai saboda wani namijin idan ba ya ra,ayin ɗaya ya fi ra,ayin ɗaya a cikin matansa sai dai wacce ba ya ra,ayi ta ɗauki dangana, idan ma ta ce sai ta ga yadda take so tabbas iska tana yawo da mai kayan kara ne!" Ɗago kai Sadiya ta yi suka yi ido huɗu Hajiyar ta kauda kai gefe, sai Sadiya ta ce

"Ba a kan wani abu ba ne dama, kin san ina sana,ar kayan sanyi to shi ne ƴan nepa suka cire wutar ɓangarena shi kuma ya ce sai ina biyan kuɗin wuta ... Hajiya ta tare mata numfashi da faɗin

"Ai ya yi daidai! Kina neman kuɗi kuma a ce sai ya biya kuɗin wuta? Ko shi kike ba kuɗin cinikin yake sakawa a aljihunsa" Girgiza kai Sadiya ta yi daman ta san ba za a mata adalci ba hakan ya sa ta ce

"Yanzu ai na ce zan ke biya amma kuma bai san an mayar mini ba, ana zuwa neman kayan sanyin ina cewa babu kada kasuwar ta mutu shi ya sa dama na ce bari na zo na faɗa miki ko za ki masa magana"


Hajiya ta ce

"Sai ki ɗauki na annabawa ki jira lokacin da idan ya gama busar iska zai sa a gyara miki, abin da sana,ar da kike ta fi goma ko kin ɗauka ba sani ba ne, tun da laila ta ƙiya sai a koma caca, ai a yadda kike caskar kuɗina wannan gidan da ke matan da suke son miji ne da ko aikin hajji ne ma kin biyawa Nasir tun da ta dalilin zaman gidansa da albarkarsa kike samun kuɗi" Shiru Sadiya ta yi ta ma rasa mai za ta ce sai kuma ta daure ta ce

"Yanzu gawayina ya ƙare kuma na faɗa masa ya ce ba shi da kuɗi ita kuma ta ce babu gas ya ce zai saya mata..

Hajiya ta katse mata hanzarin wajen faɗin

"Ya isa Sadiya na gaji da jin ƙorafinki ai dama tun da na ga kin ɗakko ƙafafu da ciki tirtsi tirtsi ke ga kaza sarkin haihuwa san sai dai ƙorafe ƙorafen ne zai kawo ki Allah na tuba gawayin me duk neman kuɗin da kike ma ai ke ya dace kike ciyar da kanki, kuma da kike maganar gas ni baki ga da abin da nake amfani ba tun da gas ɗin ya ƙare sai kawai mai baro na gani da itace Nasir ya aiko, tun da ya haɗu da mace mai jan akala da ragamar rayuwarsa sai dai mu zuba ido"

Sadiya ta ce

"Amma ni ma ai haƙƙina ne ya saya mini, kuma duk arziƙin da mace take da shi Allah bai ɗora mata ɗawainiya da kanta ba, ko da ta fi mijin nata kuɗi haƙƙinta na komai yana wuyansa sai dai idan ita ce ta ga dama bisa kyautatawa!"

Hajiya ta ce

"Yi min wa,azi Sadiya kin san ai ni kidahuma ce babu abin da na sani"

Sadiya ta ce

"Ba haka ba ne Hajiya, wallahi jiya da na fita gidan Kaka na dawo na rasa jakata da nake saka kuɗaɗe a ciki, sannan jarkar manja na tarar da kananzir a ciki...

Tun bata kai aya ba Hajiya ta ce

"Bakya fitar da zakka ne, ai dama wanda ba sa fitarwa da dukiya zakka su asara take faɗawa" Kallon Hajiya kawai take sai kuma ta ce

"Ai sana,ar tawa bata kai munzalin da zan fitar mata da zakka ba, ina sadaka dai"

Hajiya ta ce

"Ke kika sani da yake matsaloli ne suka baibaye ki shi ne kika zo kina zana mini kamar mai biya mini karatun hadda, to sai ki ɗauki ƙafarki ki koma inda kika fito, ko a tunaninki zan zaɓe ki ne in ajiye ƴata Meenal a kan maganar siyan gawayi da gas ai wata kusar ta fi wata kinnga tafiyata" Hajiya tana kaiwa nan ta tashi ta shiga kicin ta ɗakko robar da za ta kwashe tuwo ta yi ajen murhu, Kalifa sai kallonta yake abin takaicin ko uffan bata ce masa ba wai yana jikanta ɗaya tal duk duniya.

Haka ta baro gidan ranta yana ƙuna, tana tafiya tana ta addu,a da karanta sunayen Allah a kan ya kawo mata mafita, ƙaran wayarta ne ya katse mata tunani ta ɗaga ganin sunan ƙawarta Noor tana ɗagawa ta ce

"Albishirin ki"
Sadiya ta ce
"Goro fari ƙal"
Noor ta ce

"Sunanmu ya fito a wannan tallafin da muka cike an ce gobe za a je a karɓi 75k "

Sadiya kawai sai ta ce

"Alhamdulillah, Alhamdulillah" Sai da ta faɗa sau uku Noor ta ce

"Wannan hamdalar fa?" Ta faɗa tana dariyar tsokana
Sadiya ta ce

"Wallahi kawai wata hikima ce ta ubangiji Allah maji roƙo ne, duk wanda ya dogara da shi zai kawo masa mafita, na san wannan sakamakon addu,a ta ne da na yi da yaƙi ni" Noor duk da bata san komai ba sai ta ƙara mata ƙarfin gwiwan na ta ce idan sun haɗu goben za su yi maganar.

Ko da Nasir ya dawo ta faɗa masa cewa ya saka a mayar mata da nepa za ta biya kuɗin sai ya nuna mata ba yanzu ba, ai kuwa ta ƙyale shi. Washe gari suka je suka karɓo kuɗin duk da sun samu layi, dama NIN no da BVN ne ake buƙata da aka cike aka muau hoto sai aka basu ATM mai ɗauke da kuɗin suka cire suka taho gida Sadiya ranta fari ƙal.

Lokacin da ta dawo sai ta ga ƴan nepa su biyu a ƙofar gidan wani maƙocinsu daga can gaba suna mayar masa da wutar da suka yanke, ai kuwa ta musu magana ta biya suka mayar mata da tata wutar ɓangaren nata.

Meenal ta fito daga ɗakinta sai kawai ta ga hasken ƙwan ƙofar ɗakin Sadiya ya kawo hakan ya tabbatar mata da cewa an mayarwa da Sadiya nepa ranta ya kai ƙololuwa wajen ɓaci, ta ƙufula tana jiran ya dawo don a tunaninta shi ya sa aka mayer da wutar.

Lokacin da ya dawo Sadiya ta fara jiyo hayaniya sosai ana ta tafka faɗa, sai dai bata san abn da suke faɗa ba, tana zaune tana cin farar da ta siyo sai gashi kamar an jefo shi yana shigowa ya ce

,"Wane shegen ne ya mayar miki da nepa?" ,Ya tambaya ransa a matuƙar ɓace kamar zai hau ta da duka.

Ko gizau bata yi ba ta dake ta ce

"Ni ce nan na saka aka mayar mini, saboda na ga baka da niyyar sakawa a maida, ni kuma ina da buƙatar ta, tun da dai ba ni da galihu a matsayjna na matarka da zan aamu wutar nepa a ɓangarena duk da na ce zan biya shi ya sa da na gansu a unguwar suna mayarwa da wasu na ce su zo su mayar mini na biya su kuɗinsu" Kallonta kawai yake yana kissima yaushe Sadiya ta zama haka har take mayar masa martani ko ɗarɗar babu.

Meenal da take laɓe a ƙofar ɗakin Sadiya don son jin ƙwaƙwaf domun ita bata yarda da maganarsa ba da ya ce ba shi ya sa aka mayar ba sa ga shi kunnuwanta sun jiye mata.

Da yatsa ya nuna ta ya ce

"Har ni zan saka doka a gidan ke ki ƙetara?"

Tsaye ta miƙe ta ce

"Ka sa an yanke min wuta na ce a mayar ka wofantar da maganar bayan ka san sana,a nake, na faɗa maka na rasa jakar kuɗina amma ko a jikinka, bayan fitarka daga gidan na samu jarkar manja na ɗauke da kananzir saboda na san ma ba ɗaukan maganar za kamyi da muhimmanci ba ko faɗa maka ban yi ba, na ce maka gawayi ya ƙare ka ce baka da kuɗi, na je na faɗawa mahaifiyarka amma bata goyi bayana ba, ka ga kenan ni idan na biye maka zan dawwama ne babu ƴanci shi ya sa na saka aka mayar mini saboda wannan sana,ar da ita nake tallafawa kaina" ,Tana kaiwa nan ta ɗauki ledar farar ta ta ci gaba da ci.


Rasa ma abin da zai ce ya yi sai kawai ya juya fuuu ya fita, Meenal da take laɓe bata zaci fitowarsa a lokacin ba, sai kawai ta gan shi, rai a ɓace ta sha gabansa cike da ƙaraji ta ce

"Tun wuri ka saka ƴan nepa su zo su yanke wutar nan tun da babu yawunka wajen mayarwa, kana mai gida mace ta yi abu babu izininka kenan ka zama mijin ta ce, nan gaba duk hukuncin da ka zartar ba za ta bi ba" Shiru ya yi yana nazarin maganarta, ya juya kenan zai koma yan saukewa Sadiya ya nuna mata bata isa ba sannan ya saka a yanke mata wutar sai kawai ya ga Sadiya ta fito kamar an jefo ta rai ta haɗe ta kalle su ta ce

"Idan bai zama mijin ta ce ba ai ya zama mai ɗaukan zugar mace!. Wato dama ke kika saka shi aka yanke mini wutar ɓangarena, to wallahi wallahi wallahi ki fita idona na rufe don shiru-shiru ba tsoro ba ne gudun magana ne, kuma wutar nan yadda aka mayat da ita ta maidu in dai kuɗin wuta ne zan ke biyan kayana, amma furucinki ya nuna ba wai a kan kuɗin wutar ba ne baƙincikin sana,ar ne kike...

Hannu Meenal ta ɗaga mata tana faɗin

"Ahir ɗinki Sadiya!. Na fi ƙarfin na miki baƙnciki a kan wannan sana,ar da bata taka kara ta karya ba"

Sadiya tana riƙe ƙugu ta ce

"Guntun gatarinka ya fi sari

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login