Showing 138001 words to 141000 words out of 178828 words

Chapter 47 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt

18 Dec 2025

1436

sun duba Daddyn nashi.

Bayan Jidda ta musu godiya sai kuma Umma ta yi shiru har sai da Jiddan take tambayat shirun da ta yi, Umma ta ce

"Wallahi dama wata damuwa ce nake da ita Jidda ina fata za ki share mini hawaye"

Jidda ta ce

"Subhanallahi damuwa kuma Umma?" Umma jin duk Jidda ta rikice tana nuna damuwa sai Umma ta cr

"Wallhi kuwa wani ɗan uwana ne a ƙauye jeji suka shige shi ƙafa tana nan suntum sai wari take to an kai shi wajen me magani sai aka yanka kuɗaɗe masu yawa, har dubu ɗari biyu da hamsin to yanxu sun haɗa dubu hamsin dubu ɗari biyu suke nema na ce bari na gwada sa,a ta a wajen ɗiyata mai tausayi ko za a dace!" Ta faɗa tana aikawa Jidda harara ta cikin wayar. Ajiyar zuciya Jidda ta sauke ta shiga faɗa mata cewa bata da kuɗi don jiya ta yi sayayyar wasu kaya a online za kawo mata sai dai za a iya samun dubu saba,in.

Umma ta ringa faɗa tana cewa

"Yanzu Jidda har sai an koya miki dabarar zaman aure a gidan mijin, tun da har kika samu kika auri mai aljihu da maiƙo ai kamata ya yi kike farauto mana karki yarda ki zauna kanki da murfi don yanzu kowa ya waye" Jidda cike da rashin fahimta ta ce

"Wallahi Umma ba na iya tambayar Ibrahim kuɗi ina nufin ba na iya roƙonsa, sai dai a ɗan jinkirta idan har da kansa ya bani kuɗi sai na cika miki" Umma ta hau faɗin

"Kidahuma kike so ki zama?" Wannan ya yi daidai da zuwan Ibrahim bakin ƙofar ɗakin Jidda jin tana cewa

"Umma in saci kuɗin Ibrahim kuma? Gaskiya ni ba zan iya yin sata ba ko kuɗin waye in dai ba nawa ba ne bare na Ibrahim" A daidai nan ya tura ƙofar gabaɗaya ta rikice ta saki wayar ma daga hannunta ta faɗi ƙasa sa,ar ta ɗaya wayar bata yi komai ba.

Sai ya nuna mata bai ji abin da take faɗa ba, dama kuma ya san ba za a taɓa haɗa baki da Jidda a cuce shi ba ya yarda da ita 100%
Wayar ta ɗauka ta kashe da sauri jin yana cewa har yanzu bata gama shiryawa ba, duk ta rikice yanayin da ya ga ta nuna har ya so bashi dariya amma ya danne.


Umma wani ƙuduri ta ƙudurta a ranta cewa za ta yi maganin Jidda don sai ta mata abin da wani maƙiyinta ma idan ya ganta sai ya tausaya mata.

Wani filinta ta je ta ɗaga ta sayar Abba ma bai sani ba suka haɗa kuɗin suka nufi wajen bokanya. Bayan sun damƙa mata kuɗin ta tashi tsaye tana riƙe da wani ƙaramin kasko take kewaya ɗaki a take hayaƙi ya fara fitoa daga kpwace sukurwa ta ɗakin. Lokaci gida hayaƙi ya baibaye ɗakin su duka a tsorace suke sai da ta gama ta koma mazauninta ta zauna ta dube su ta ce

"Yanzu mai kuke so a yi"

Umma ta yi karaf ta ce

"So muke a saka masa son Aliya yadda ba zai taɓa rabuwa da ita ba yadda zai tsani duk wanda ya kushe ta ko ya nuna sai ya rabu da ita, sannan a saka soyayyarta a zuciyar surukan nata wato iyayan Ibrahim ɗin, shi kuma mahaifinta wato mijina a saka masa son auren nata kuma kar ya taɓa tambayar dalili ita kuma Jidda a sanya ta zama akwai ya babu kakar wajen uba"

Aliya ta ce

"Kawai gwara ya danƙara mata saki lokaci guda idan dai ya yanke igiyar auren dolenta ta tafi ai"

Bokanya ta gyaɗa kai tana wani haɗe halen magani sai kuma ta shiga kiran sunayen wasu aljannu kafin ta buɗe hannu su Umma sai ganin wani magani suka yi kulle a farar leda an ɗorowa Bokanyar a tsakiyar hannun.

Nan ta miƙawa Umma magnin ta ce

"Wannan garin maganin za a saka shi a hancin sabuwar gawa ta namiji, bayan an masa wanka an saka likkafani kafin a rufe kan za a cire audugar hancin sai a zuba maganin a duka ƙofofin hancin sai kuma a mayar da audugar a rufe, yadda gawar nan bata da wani sauran amfani haka Jidda ba za ta sake amfani a wajen mijinta ba kuma a take zai sake ta, sanann son Aliya zai shiga zuciyarda daram, sai kuma mahaifinta da ko ma waye ba za su taɓa kawo tsaiko a kan auren ba, babu ma mai tambayar don mai aka yi " Umma tana dafe da ƙirji da hannu biyu sai karkarwa take jin furucin bokanya, tana tuna naira dubu ɗari biyu da suka bayar yanzu kuma ga wani ɗanyen aikin da take ji har gwara na cokalin da Aliya ta yi.

Aliya tana zare ido ta ce

"Bokanya ko za ki sauya aiki?" Umma ta shiga gyaɗa kai alamar gamsuwa da maganr Aliya ita kuma Bokanya ta ce

"Ai in mun faɗa sai an yi kuma ba za a canja ba, mene ne abin wahala a wannan aikin ku da kuke neman biyan buƙuta ai ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba, da kuka ci sa,a ma ban ce ku yi ridda ba"

Suna haɗa ido suka juya suna kallonta suka haɗa baki wajen faɗin

"Ridda?" Bokanya ta ce

"Ridda mana mutane nawa ne suka yi ridda saboda su samu biyan buƙata, mutane nawa za su zo mu basu hutun yin sallah na kwana arba,in ko satittika ko watanni kuma su yi"

Umma ce cikin sanyin murya ta ce

"To ai bokanya ta yaya za a yi mutum ya iya zuwa wajen gawa har ya yi abin da kika faɗa ba tare da tonuwar asirinsa ba?" Da wata mahaukaciyar dariya ta bushe ta jima tana yi sannan ta haɗiye dariyar ta hanyar haɗe rai sai kuma ta ce

"Komai a tsare yake, don haka akwai maganin da zan bayar da kowa sai ya suma a take a wajen " Umma suna gyaɗa kai ita da Aliya kamar ƙadangaru Bokanya ta miƙa

"Wnanan maganin ne na sakawa a hanci, wannan kuma daga kin shiga gidan makokin sai ki ambaci sunan mamacin tare da fakar idanun mutane ki juye garin maganin a hannunki sai ki hura da baki ta yadda maganin zai bi iska kuma ko wani ya gani ba zai tambaya ba, kina yin haka kowa zai faɗi sumamme har ki je ki gama abin da za ki yi idan kin gama sai ki ƙara ambaton sunan mamacin kowa zai tashi kuma kowa ba zai taɓa sanin ya suma ba"

Sun karɓo sun taho Umma tana ta adana maganin, don Bokanya ta ce a tsakanin su kowa zai iya yin aikin tun da an yi maganin da sunan waɗanda ake so aikin ya ci, don haka sai Umma ta ce za ta yi ita kuma Aliya dama ta ce tsoro take ji. Aliya gida ta wuce, Umma ma ta wuce gidan don Abba bai dawo daga kasuwa ba.

Umma ta je ta ɓoye maganin a wata sabuwar samirar ta, tana zaune da magriba bayan ta idar da sallah, tana jingine da bango Abba yana masallaci lokacin sai kawai daga masallaci ta ji ana sanarwa ana cewa


"Innalillahi wa inna ilaihi raji,un Allah ya yi wa malam kalla rasuwa, za a yi sutura da ƙarfe bakwai na safe, Allah jiƙansa ya gafarta masa" Zuruf Umma ta miƙe tsaye gabanta yana faɗuwa, don ta san lokacin aiwatar da aikinta ya yi duk da tana da mugun tsoron gawa, amma haka za ta durfafi wannn al,amari saboda malam kalla maƙocinsu ne daga can gefe!.





SADIYA

Da tsananin mamaki ta ɗago tana kallon Meenal wacce take tsaye hankali kwance take zaro baƙar magana, ta rasa mai ta tsare mata a gidan bayan ita ta zo ta samu a gidan amma tana son fitar da ita daga gidan mijinta ta ƙarfi da yaji!.

Meenal ta ƙara haɗe rai haɗe da yatsina fuska ta ce
"Ina fatan kin fahimta, ko kina kokwanto a kan hakan ne in nuna miki zahiran" Ta faɗa tana kama ƙugu da hannu ɗaya, Sadiya danne takaicin da yake ranta ta yi ta ce

"A kan mai zan yi mamaki ai shi mutum ba a gane shi a fuska sai dai ɗan adam bai isa ya zartar da abu a kan mutum ba sai abin da Allah ya rubuta a kansa, idan har ruwana ya ƙare a gidan nan dole zan bar gidan idan ruwan shana bai ƙare ba kuwa babu wanda ya isa ya dakatar da hakan" Ido ɗaya ta kanne tana bin Sadiya da kallo kawai sai ta juya tare da yin ƙwafa ta shige ɗaki.

Zuwa jimawa aka fara sallama, bayan an amsa masa ya sanar da cewa mai yin kicin ne da mai gidan ya kira, Sadiya dai ta masa iso ta ja ɗanta suka shige ɗaki. Nasir kuma yana fita da ya je ya gidan Hajiya ya same tw zaune ta duka uban tagumi duk ta yu baƙi ya rasa ma mene ne ummul aba,isin hakan ya zauna bayan ya gaishe ta ta amsa tana sakin doguwar hamma ta ce

"Nasir yanzu sai da na maka waya shi ne za ka zo? Yanzu sai ka kwana ka tashi baka ma zo inda muke ba Nasir?" Ɗan sosa ƙeya ya yi ya ce

"Wllahi Hajiya abubuwan ne suka sha kaina amma baki da lafiya ko" Ta ɗan kai hannu ta taɓa wuyanta da ya yi ƙashi ta ce


"Amma da duk abubuwan da suka maka yawa duk safiyar Allah sai ka zo gidan nan, kuma da kake maganar ko ina lafiya ai yunwa ita ce babbar rashin lafiya" ,Da mamaki ya ce
"Rashin lafiya kuma? Yunwar ce rashin lafiyar hajiya bakwa cin abinci ne" ,Ya faɗa lokacin da ya ga Hibba da Husna ma sun fito sun zaune su ɗin ma duk sun yi rama.

Hajiya ta ce

"Yanzu Nasir har sai wani ya faɗa maka ba ma girki ai ba girki ne ba ma yi ba ƙoshi ne kawai ba ma yi, yanzu a ce yaran nan su je su yi bautar girkwa yarinyar nan Meenal abincin kari amma take tsakura mana wani ɗan mitsitsi kamar wanda muka roƙa yanzu saboda isa ma wai hatta madara da milon ta daina tsakura mana sai dai mu sha lipton kawai kp yau da suka kawo sai haƙura na yi na sha koko haba a kan mai yarinya ƙarama z ta zama ita take juya ragamar gidanka Naasir" Iska ya hurar yana kallon yadda su Hibba suke zumɓura baki ya ce

"Haba Hajiya ita fa Meenal gidanta ne su kuma yaran nan su ma idan suka je gidajensu sai su dafa abin da suke so, sannan maganar madara cewa ta yi ta kusa ƙarewa a bari ita take sha idan tana tskurawa ba zai isa ba to kin ga ba sai an saka mata rani ba, sannan maganar rashin zuwana Hajiya da fa abincin safe nake zuwa ci yanzu kuwa kin ga acan gidan ake dafawa... Tun kafin ya kai ƙarsheb maganar Hajiya ta fashe da wani kuka mai kamar jiniyar motar ƴan sanda, ta ce

",Yanzu Nasir ni kake faɗawa wannan maganar? Wato har gorin aure kake wa ƴan uwan naka saboda wanncan matar mai ƙira kamar ta barewa, to ahir ɗinka idan ma ƙarfinka aka fi zan yi maganin abin" ,Tsaye ya miƙe cikin halin ko in kula ya ce

"Ni zan wuce, dama zuwa zan yi in kira me aikin kafinta zai je can gidan ya yi aa Sadiya kicin ɗin langa langa saboda Meenal ta ce bata son wannan haɗen kicin ɗin" ,Ya faɗa yana tashi tare da gyara zaman hularsa da yake ji kamar bata zauna ba. Da kallo sula bi shi su duka, don yanzu babu wanna soyaya da kulawar da yake basu kawai tamkar ma hankalinsa ba a kansu yake ba, sannan ita Hajiyar ko ta tsawatar a kan rashin adalcin da ta ji za a yi wa Sadiya na yi mata kicin ɗin langa-langa duk da dama abu ne da suka saba na tashin yi mata a adalci da alama Allah en ya fara kawo wacce za ta mata maganinsu.

Yana fita sai da suka ji tashin motarsa sannan Hibba ta ce

"Hajiya Yaya Nasir da tamkar ba ya cikin hayyacinsa wallahi ina jin an fi ƙarfinsa ne wato an masa asiri" Husna ta karɓe maganar da faɗin

"Ai dama daga ganin abin ma a hankalce an sana cewa Yaya ba zai aikata haka ba"

Hajiya ta goge wani hawaye mai zafi ta ce

"Ni wallahi abin nan neman fin ƙarfiba yake domin na kasa gane kai da ƙafar abin nn na yi da na sanin auren nan da ya ƙara sannan ina zargin Meenal da mahaifiyarta a kan komai duk da mahaifiyar tata tana nuna min bata ma san abin da Meenal take yi ba sai ta ce wai ita ba za ta tsawatar mata ba ai ni da ita babu bambamci zan iya tsawatar mata bayan yanzu yarinyar nan ji take kanta ɗaya da ni ta ɗauke ni tamkar sa,arta, wai har ni Hajiya Mariya ce sirija take juyawa sannan har ta bada umarni muka bi ni da ƴaƴana wai ƴaƴana ne suke zuwa suna mata girki kullum da safe sannan ta tsakura mana abincin son ranta, wallahi ko a mafarki ban taɓa tunani ba"

Hibba ta ce

"Hajiya ai wallahi yadda kika san wani tsoronta aka saka mana a rai" Haka suka ci gaba da jajantawa suna tunanin yadda za su samo mafita a shawarar da suka yanke dai zuwa wajen malami ne sai dai babu kuɗinnzuwan don yanzu kuɗin da Nasir yake basu duk ya ɗaure bakin aljihunsa sai na annabawa.

Naair yana fita ya bugawa me aikin waya ya sanar da shi su haɗu a gidan nasa, sai ya riga Nasir ɗin zuwa yana dawowa gidan ya nuna masa inda za a yi kicin ɗin haka suka tafi suka siyo komai na aikin mai baro ya kawo langa langa da katakon aka shiga aiki tuƙuru!.
An gama kicin tass mai aikin ya tafi don sai da ya sallame shi ya tafi kasuwa. Bayan ya tafi Meenal ta fito daga ɗakinta Sadiya tana jin lokacin da ta je take cewa


"Kai amma kicin ɗin ya yi kyau ji langa langan gar sheƙi yake, amma shi ma me aikin nan da ɗaurin tsantsa yake wato gar wani wajen ɗora kwanuka ya mata to Allah kyauta, din dai dama da irin wannan kicin ɗin ta dace" Sadiya bata ce komai ba ta yi kamar ma bata san mai take cewa ba don ta san tana faɗa ne don ta ji. Ko da aka kawo nepa haka ta ƙure kiɗa a gidan don ta turaw Sadiya haushi kan rashin nepar ita kuma sai ta tishe kunnuwanta kamar ma bata san tana yi ba, domin ko da almajirinta ya zo ɗaukan talla ta ce masa firjin ya samu matsala don haka ta kwashe gabaɗaya kayan cikin ta bashi ta ce ya je ya sadakar kar su lalace!.

Meenal duk wannan abin sa ta yi wa Sadiya bata haƙura ba tun da burinta ta baƙanta mata rai ita kuma Sadiya tun da ta lura Meenal tana cikin mata masu kishin kissa da kisisina sai ta tattara kamarinta ta ajiye a gefe kuma ta saka a ranta duk runtsi za ta saka haƙuri da juriya ta san da cewa watarana sai labari kuma duk abin da ka yi haƙuri to watarana Allah zai maka sakkaya a kansa, domin wanda aka zalunta babu shamakin addu,arsa uabnagiji zai karɓe ta ko da bai yi adsu,a ba za a masa sakkaya wannan kaɗai take sakawa a ranta ta ji salama.

Meenal ganin Sadiya ta danganta da maganar yanke wuta don da kuɗinta ma Naair ya ƙi ya saka a amayar mata jawai donnya nuna bata da kima da muhimmanci, sannan bata da wani galihu a wajensa, bai san darajarta ba, ganin ta mayar da hankali a kan sauran kasuwancinta na cikin gidan tana damƙar cikinikinta, kuma sai ta ga kullum tamkar ƙara buɗe mata hanyoyin samu ake don jama,a haka suke turruruwa wajen saye mata jayan tamkar kyauta take rabawa, don sai ma ta fara zargin ko dai wajen malamai ta je ta nemi kasuwa wato ko da maganin kasuwa take amfani shi ya sa take samun ciniki..

Abin da bata sani va shi ne Sadiya babu abin da ta riƙe sai addu,a idan ta yi sallah tana ɗaga hannu ta faɗawa ubangiji damuwarta sannan ta roƙe shi ya kawo mata kasuwa me albarka ya ƙara kawo mata masu sayen kayanta ta ko ina, hatta bashi da sauran masu kasuwanci suke kuka da shi idan an karɓi kayansu bashi ba a biyansu ko a basu rabi a hana rabi wata ma ta cinye kenan, to Sadiya babu mai riƙe mata kuɗi kuma addu,a ce makamin saboda tana faɗawa ubangiji ya raba ta da ƴan bashi duk wani wanda zai cinye mata kuɗinta Allah ya nesanta ta da shi.


Yau ya kama Laraba Sadiya ta tambayi Naair zuwa gidan Kaka dubiya saboda Kaka tana zazzaɓi danyake jiya ta faɗa masa da ta ganshi a tsakar gida kuma ya amince, don har yau Nasir bai shiga ɗakinta da sunan tana da baki ko matsayinta na matarsa ba ita bata ma taɓa jin ƙarin aure irin wannan ba a duk da tana ji a labari ana cewa wata idan aka mata kishiya mijin yana neman ta bashi kwananta ya ƙarawa amarya wani ya siya wani kuma ya ƙwata ta ƙarfi, kwanaki ta ji labarin matar da ta ce tun da mijinta ya yi aure shekara uku bai kusance ta ba, kai ɗakinta ma sai ya ga dama zai shiga kuma ba ya yin sama da minti goma zai fita, ashe dai ita ma al,amarin yana zuwa kanta rayuwa kenan.

Yana tafiya kasuwa ta shirya ta shirya Kalifa ta tattara kayan sana,arta ta saka a kicin ta janyo kicin ɗin ta kulle haka ma falonta. Meenal da bata san Sadiya ta tambayi Nasir fita ba sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login