Showing 177001 words to 178828 words out of 178828 words
Chapter 60 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt
da ɗoki ta ce
"Malam ka tabbata zai mu,amalanceni"?"
Ya kalle ta ya ce
"Ba saka kokwato a aikinmu"
Ta ce
"Ai na sani kawai dai mutumin yana da taurin rai ne, sannan ya tsane ni ko ganina ya yi sai fuskarsa ta sauya, kuma ko magana ba ta haɗamu hasalima iya gaisuwa ne yake haɗamu"
Boka ya ce
"Ba kallon ke mace ba kuma mutum to ko da a ce dabba ya gani wato ki ƙaddara bayan ya sha maganin ya ga akuya to saa ya haike mata kawai zai ji yana son kaɗaicewa da duk wata halitta indai mace ce" Murmushjn nasara ta yi tana faɗin
"Na gode sosai boka Allah ya...
Hannu ya ɗaga mata ya ce
"Sai kuɗin aiki dubu ɗari biyar ne" Transper ta masa sannan yana nannaga mata sai nan da kwana bakwai ko takwas za ta aiwatar da aikin. Tun da suka taho Umma takr mata nannago a kan ta san idan za ta ajiye maganin don ita Umma ta tsani ma a ce wai magani ba za a aiwatar da aikinsa ba sai an ƙayyade masa kwanaki saboda ta fi son sha yanzu magani yanzu.
A yadda Jidda ta faɗa musu cewa sati uku za su yi sai dai daga baya ya zamana sati biyu ne kuma sai ta sha,afa ba ta faɗa musu ba. Duk da sau biyu suna waya da Abba amma tun da ta ta fi ba su yi waya da Aliya ba sai Umma ce da suka gaisa a wayar Abba lokacin da ta kira shi, domin sau biyu tana kiran wayar Umma ba ta samun ta.
Sun yi ibada sosai Jidda ta mayar da hankali wajen yin addu,a da neman tsari sannan uwa uba ta sha yi wa iyayenta addu,a da nema musu gafara da rahmar ubangiji aljanna kuwa ta roƙa musu mafi girma da ɗaukaka haka kanta da kuma ginshiƙinta mijinta abin alfahrinta Ibrahim. Ta tsawaitawa Abba addu,a bisa jajircewarsa na kasancewa tsani kuma matakala da ya maye mata gurbin mahaifi. Su Umma ma ba a barsu a baya ba domin tana jinsu a tsakiyar zuciyarta a ƙarshe ta sha saka jama,ar musulmi a addu,ar neman shiriya da samun zaman lafiya mai ɗorewa.
Yau ya kama talata a yau ne suka kammala komai yau ne jirginsu zai tashi zuwa Nigeri,a ƙarfe sha biyu na rana jirginsu ya taso daga jidda awa shida ya kawo su Nigeri,a jirginsu ya sauka ƙarfe shida na yamma.
A ɓangaren Aliya yau ya cika kwana takwas daidai da dawowarsu daga wajen boka kuma yau ne ya dace ta aiwatar da aikin da zai zama cikar burin nasu. A nata hasashen kuma iya saninsu saura sati guda Jidda ta dawo wanda sun yi imanin idan ta sauka a Nigeri,a lokacin ta zama tarihi a zuciya da rayuwar Ibrahim.
Ko da ta ga dab da magriba ta tabbatar lokacjn yana gida domin wani matashin saurayi ɗan zauna gari banza da ta saka shi zama a unguwar yake kular mata da motsi shige da ficen Ibrahim a ranar. Bayan ya sanar mata ya ga shigarsa gidan, don haka lokacin da ta zo sai da ta leƙa wata tula ta tabbatar da mai gadi ba ya harabar wajen, ta yi saɗaf saɗaf ta turo ƙofar domin ta tabbatar yana banɗakin. Har ta shiga falon da yake ƙasa ba ta samu kowa ba a falon shiru don ta ji Jidda ta ce su Saude za su koma ƙauyensu har sai ta dawo.
Bayan kujera ta samu ta haura wanda yake da ɗan faɗi inda yake daga wajen kwana ta bango aka saka kujerar kasancewar kujerun irin wanda ba a saka su har bango ne.
Ƙaran tahowarsa ne ya sa ta shige wajen gabanta yana faɗuwa, tana ganinsa ya wuce daga tsakanin kujera da take hangensa, frige ya buɗe ya ɗakko maltina ya nufi saman dama tun da Jidda ta tafi sai dau ya sha drinks da snacks. A daidai nan ta lallaɓa ta haye saman saboda kasada idanunta ya rufe a kan cikar burinta.. Sai da ta hau saman ta fara dawurwurin inda za ta ɓuya domin ta kasa gane a wane ɗaki yake.
Ɗan ƙaran faɗuwar abu ta ji a ɗaya ɗakin ta haka ta tabbatar yana ɗakin. Daga jikin mariƙin ƙofa ta leƙa ta hangeshi zaune a bakin gado da ƙaramin tebur a gabansa sai maltinar a ka gabansa kuma kofin glass ne wanda ya suɓuce daga hannunsa ya faɗi ya fashe. Ganin ya miƙe tsaye ta matsa daga ƙofar gabanta yana harbawa ko da ta samu mafaka sai ta ganshi ya zo ya sauka ƙasa domin shi ransa fari ƙal yau Jiddansa za ta dawo gare shi, sai dai yana ta kiran wayarsu ba ta shiga ya san wataƙila suna hanya ne yana jiran su sanat masa sun dira ya je ya ɗakko su.
Yana sauka ta fito daga maɓoyarta ta shiga ɗakin a sukwane dama ta buɗe maganun tana shiga ta ɗaya murfin maltinar kasancewar ya buɗe kwalbar bai kai ga zubawa ba kofin ya fashe. Duka ta juye ta mayar da murfin ta yi saurin fitowa daga ɗakin, ɗaya ɗakin ta shige tana fargaba da addu,ar Allah ya sa kar ya buɗe ɗakin da take ciki. Tana shiga ɗakin ta ɗakko abin sakawa a ƙasan ta saka, don ta tababtar aiki yana dab da kammaluwa matsawar ya yi tarayya da ita to ba zai sake marmarin wata ƴa mace na har abada!.
Sannan daga ranar ta zama sarauniyar zuciyarsa zai aure ta ya zauna da ita kuma babu mai tambayar wani ba,asi sannan Jiddar za ta fuskanci ƙasƙanci.
Kayanta ta cire gaba ɗaya saboda toshewar basira ba ta ma bari ya je ya sha maganin ba dimin ta sa a ranta shan magani ai kamar an yi an gama, sai da ta shafe turaren nan kaf a jikinta ta ɗauki ɗankwalinta ta ɗaura a jikinta, a daidai lokacin ne ta fara jiyo takunsa zuwa saman murna fal cikinta sai dai gabanta ya harba da ƙarfi a lokacin da ta ɗan leƙo da tillar makamar ƙofar ta hange shi ya doso ɗakin da take, idanu ta zaro tana tunanjn shikenan dubunta ta cika tana hango taɓarɓarewar al,amura matuƙar ya buɗe ɗakin ga kayanta nan a tsakar ɗakin da bata ma ɗauke ba kuma matuƙar ta ce za ta tsaya ɗauka sannan ta nemi maɓoya akwai matsala don sai ya shigo ba ta samu mafita ba saboda ita kanta a rikice take.
Tunanin tsakaninsu da Jidda ta yi komai zai rushe shikann Jidda za ta zama ta san cewa su ba masu ƙaunarta ba ne tun da har ga shi za ta zo har cikin gidanta a lokacin da ba ta nan don kawai ta cim ma manufarta, ta san shikann kuma Jidda ba za ta sake yarda da su ba, ƴar soyayyar ƙaryar da suke nuna mata za ta daina yarda da ita ba ma lallai ta sake sakin jiki da su ba bare har su zo inda take su cika ƙidirinsu da mafufarsu a kanta!.
Ibrahim handle ɗjn ƙofar ya kama ya buɗe ƙofar Aliya da take bayan ƙofar gabanta yana dukan lugude ta yi tsuru tsuru. Shi kuma ko ɗakin ma bai kalla ba ya dai buɗe ɗakin ne hankalinsa ma ba a wajen yake ba don ya waiwaya bayansa ne, ko mai ya tuna sai ya ja ƙofar ya rufe a juya tare da buɗe ɗaya ɗakin ya shiga. Aliya komawa ta yi ta jingina da bango tana sauke ajiyar zuciya a fili har lokacin ƙirjinta yana tsananta bugu kamar zuciyarta za ta fito.
Yana shiga ɗakin ya kwashe kofin da ya fashe ya zuba a kwandon sharar da yake cikin ɗakin daga can gefe wanda babu komai a ciki sai tissue. Saurin saka kayansa ya yi yana son tafiya airport ɗakko su Jidda. Yana ɗaura agogonsa ya tsiyaya maltinar a kofin da ya sake ɗakkowa da ya sauka ƙasa. Kai ya kafa ya sha ya ajiye tare da miƙa hannu zai ɗakko wayarsa da ta ɗauki ruri yana dubawa ya ga Mummy ce hakan yana bashi tabbacin sun dira. Sai dai kafin ya ɗauka mararsa ta murɗa masa da wani irin ƙarfi, fuska ya yatsina yana kai hannunsa ya dafe mararsa a take ya ji komai ya sauya wata irin buƙata ce da bai taɓa ji ba ta mamaye ilahirjn jikinsa ji yake idan ya ƙara wasu mintuna bai samu biyan buƙatarsa ba tamkar numfashin sa zai bar jikinsa gabaɗaya idanunsa sun rufe mafita yake nema ta ko ina.
Aliya da ta gama kallon abin da yake faruwa ta ƙaramar tular jikin ƙofar hannu ta saka domin buɗe ƙofar ɗakin da yake ciki, ɗankwalin da yake jikinta ko mazaunai bai rufe mata ba. Tana shiga dama ya ba ta baya sakin ɗankwalin jikinta ta yi ya faɗi ƙasa kafin ta fara taku ta nufe shi tana wani malmalƙwashewa kamar macijiya!.
A can ƙofar gida su Jidda ne da Mummy, jidda da Mummy a baya sai Daddy wanda yake gaba direba yana tuƙawa. Sun yi ta kiran wayar Ibrahim bai ɗauka ba kuma shiru bai zo ba, hakan ya sa Daddy ya kira direba ya je ya ɗakko su. Mai gadi ya wangale musu get suka shigo Jidda ta fito daga motar Mummy tana cewa ta gaishe shi wataƙila bacci ya yi. Ga magriba ta gabato. Mai gadi yana ta mata sannu ta amsa lokacin su Mummy motar su ta har ba zuwa titi. Riƙe da akwatin ta ta tura ƙofar ta shiga tare da mayarwa ta rufe tana tunanin abin da ya hana Ibrahim zuwa ɗakko su bayan ta san ya san lokacin da jirginsu zai sauka.
*Ni ma dai maman afrah a nan na dasa aya, don gabaɗaya turka-turkar ɓangarorin nan uku ta sha min kai, domin samun cigaban labarin bar ƙarshe 500 ne shiga group za a biya ta asusun faiza abubakar 9030283375 opay, sai a tura min shaidar biya ta lambata 09025576222 idan na kammala littafin complete docment 800*