Showing 153001 words to 156000 words out of 178828 words

Chapter 52 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt

18 Dec 2025

1433

ta, domin ganin ta kawar da zarginta a kan wannan mummunar ranar da za ta fallasa asirin da take ɓoyewa, duk da ta san saɓon ubangiji ne sanna duk lokacin da za ta aiwatar da saɓon ta manta cewa shi wanda ya haramta hakan hakan yana ganinta, kuma duk abin da ka ɓoyewa wani mutum ba za ka ɓoyewa Allah ba, haka kuma duk wani abu da kake ɓoyewa don kar mutane su sani akwai ranar da ubangiji zai tona maka asiri duk daren daɗewa kuwa sai an sani!.

Maganar da Mumy ta yi ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta kai ziyara na ɗan daƙiƙu, da kuma zillon da zuciyarta take yi ta ji Mamy ta ce

"Zalika ki amsa min da bakin ki cewa mene ne wannan? " Mamy da gabaɗaya hawaye take kwaranyowa daga idanunta ta faɗa cike da tsananin damuwa Allah ne kaɗai ya san damuwa da firgicin da yake cikin ranta, sai take jin anya duk iya uƙubar da take ciki dangane da zaman aurenta ta taɓa jin raɗaɗin baƙinciki irin wannan ba, sai yau take jin makamancin raɗaɗin da uwa take ji dangane da abin da ya samu budurcin ƴarta, ta sha ji a rediyo ta sha ji a social media ana labarin an yi fyaɗe ga wasu ƴaƴan wasu ma ba ƴanmata ba ne wasu yara ne ƙanana masu ƙarancin shekaru amma ake samunwwasu mararsa imanin suna raba su da mutuncinsu, ashe haka kowace uwa take jin wannan raɗaɗin? Ta san da ciwo amma bata zaci ciwon har ya kai haka ba, ciwo ne mai tafe da rashin nutsuqar zuciya, duk da nata ciwon ya sha bamban da sauran ciqukan da sauran iyayen mata suke ji domin su sauran fyaɗe ne wato abu ne da ya faru da su ba da amincewar su ba, amma nata fa?

Nata abu ne ba tsautsayi ba hasali ma alamomi da dama sun tabbatar mata da cewa tata ƴar da amincewarta tun da ga shi har tana yawo da maganin tsarin iyali wanda bai dace a ganshi a wajen macen da bata da aure ba sai dai mace mai aure!.

Zalika tana jin tashin hankali ta yi ƙoƙarin dannewa tare da saita kanta don hakan ya bata damar linke mahaifiyarta ma,ana domin ta faɗa mata abubuwan da zai sa ta yarda da ita abin da ake kira wasa da hankali da tunani


Cikin sanyin murya ta ce

"Mamy mene ne ya sa za ki zubar da hawayenki a kan abin da ba gaskiya ba? Mai ya sa za ki shiga tashin hankali a kan abin da zargi ne? Wannan abubuwan fa gbaɗay zargi ne sannan yanayin yadda kika tunkareni da maganar ya sa na shiga cikin ruɗu" Mamy wani sashe na zuciyarta yana mata albishir da cewa duk abin da ta sanya a zuciyarta ba haka ba ne shaiɗan ne yake mata linzami, shi kuma wani sashen yana faɗa mata cewa Zalika rainin hankali take mata sannan ta yi hakan ne don ta yi wasa da hankalin ta.

Durƙusawa Zalika ta yi ta saka hannuwanta biyu ta dafe gwiwar Mamy ta yi raurau da idanunta ta ce

"Mamy ni ce fa Zalikar ki da kika yarda da ni, ni ce fa wacce kika bani tarbiya kika kula da motsina da dukkan komai na, a kan mai zan ci amanar wannan abubuwan da kika min a rayuwa? " Ta faɗa tana runtse idanunta hawaye suka zubo wani yana bin wani. Mamy kawai kallon fuskarta take ta rasa ma matakin da za ta saka wannan al,marin, amma dai ta dakatar da zucuyarta zuwa lokacin da za ta ji abin da za ta faɗa mata duk da zuciyarta tana gargaɗinta a kan kar ta yarda, don yanzu Zalika ta goge mata hadda ta sanya tana jin tsoronta.


Ta ci gaba da faɗjn


"Mamy akwai wata abokiyar karatuna matar aure ce sunanta Fatima Abdulƙadir to ita ce ta saka maganin nan a jakata ta manta da shi, ni kuma abin da ya sa na tsorata da kika nuna min saboda na san zai yi wuya ki fahjmce ni, amma dai ina kyakkyawan zato a kanki mahaifiyata na san ko da duniya za ta zargeni a kan aikata wani abu marar kyau, ke kaɗai ce za ki shaide ni yanzu Mamy idan baki bani shaida mai kyau ba waye zai miki shaidar Zalikar ki?" Ta faɗa tana ɗago kai ta saka idanunta da suke zubar hawaye ta saka a cikin na Mamy da take yi wa Zalika kallon da take son gane iya gaskiyarta.


Jin Mamy ba ta ce komai ba sai Zalika ta fahimci kalamanra suna tasiri a wajen Mamy duk da ba ta gama gansuwa cewa Mamyn za ta yarda da abin da take faɗa ɗin.

Ta ci gaba da faɗin

"Tana tafiya da maganin ne school saboda time ɗin shan maganin nata lokacin muna makaranta ne, ba ta so lokacin ya wuce ya zamana sai ta dawo daga makaranta za ta sha, shi ya sa take zuwa da shi tana ɓalla tana sha, yau da ta ɓalla shi ne ta saka a jakata lokacin muna sauri za mu shiga lacture ni kuma da muka fito sai na manta ita ɗin ma ina ga mantawar ta yi"


MAMAN AFRAH
09025576222




*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)


NA


MAMAN AFRAH


. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*

BOOK 1

PAGE 2️⃣8️⃣



MEENAL
Ihu take da iya ƙarfin ta tana ɗaga hannu kamar makauniya neman ɗauki take don a ƙwace kuɗin nan duk da ba halaliyarta na ne wato ba da guminta ta tara ba. Momi kuwa sai juyi take a tsakiyar hanyar gabaɗaya jikinta ya yi busu-busu da ƙasa ita ihun ma ba ta iyayi sosai saboda nauyin da bakinta ya mata.
Su duka kuka suke jina-jina domin sun doku sosai sai dai son zuciya bai bari kowacce daga cikinsu ta fahimci cewa alhakin wacce aka sacewa kuɗin ba ne da ta tara da gumin ta. Meenal tana yin wani juyi ta ce

"Momi sun gudu da kuɗin wayyo na shiga ukuna" Momi maimakon ta furta wata kalma kawai sai ta ɗaga hannuwa biyu tana kaɗawa tana yi wa Meenal zancen bebaye, wani takaici ne ya ƙara rufe Meenal ɗin ta ce

"Haba Momi yanzu duk wannan halin da muke ciki amma sai kike mini zancen kurame?"
Momi tana ɗan ƙoƙartawa wajen ganin ta tashi zaune saboda yadda jikinta yale tsananin ciwo tsabar dukan da ta ci, ganin tashin ba zai iyu ba ta buɗe bakinta da ya kumbura suntum saboda naushin da ya sha kamar ana saka ƙaton ƙuli-ƙuli daga cikin kumatun ta ce
"Haba Meenal baki ga yadda na daku ba kamar sakawara a turmi, wannan yara mararsa imani a ce ko tausayin shekaruna ba su ji ba suka nakaɗa mini na jaki... Shiru ta yi sai da ta ɗan huta saboda yadda take jin ciwo in tana mganar tamkar an saka gishiri a ciwo ta ce

"Ai tsakanina da su Allah ya isa!"

Meenal ta ce
"Haba Momi yanzu ta dukan da kika sha ma ke kike yi, bakya ta maƙudan kuɗin da suka ƙwace wanda ko bokan ba a kaiwa ba ya yi maganin, kuma sia magana kike kamar kin cika baki da abinci"

Tsaki Momi ta ja dakyar ta ce

"Wane shege ne ya ce miki ban damu da kuɗin ba amma ai lafiya ta fi komai, kuma da kike maganar na saka abinci a baki ba gwara in saka abinci sai dubu a bakin ba da wannan masifaffan dukan da na sha, baki ya kumbura suntum ai wannan sai na nemi mansileta" Ta faɗa tana ƙara bajewa a tsakiyar hanyar domin tana jin idan ba kama-kama aka mata ba to ita dai ba za ta iya tashi ba.

Meenal ta ce

"To da ba ke kaɗai suka duka ba, kalli hancina ji nake kamar jini ne yake zuba duk sun dauje mini, ga fuskata ma sai raɗaɗi take" Momi ta ɗan ɗago kai ta kalli fuskar Meenal wata dariya ta so wwace mata amma bata son ta yi saboda yadda bakinta yake zugi. Ganin Meenal ta yi kamar an yi murjin taliyar hausa a fuskar tata, ga wata ƙasa da ta yi buɗuɗu kamar wanda ta ziyarci yaƙin badar.

Sun jima a kwance a tsakiyar hanyar amma banu wani mahluƙi da ya biyo hanyar ma bare ya taimaka musu, haka suka ba kansu shawarar tashi su lallaɓa.

Momi ɗankwalinta sa yake can gefe ta ɗaukko ta ɗora a kanta ya kalli gabas maso kudu, amma bata damu ba burinta su samu su bar tsakiyar jejin. Haka ta ɗauki mayafinta ta yaɓa a kafaɗa tana riƙe da zaninta da ta tattare tamkar za ta yi tseran gudu. Meenal ma ta lallaɓa ta miƙe tana jin ƙugunta kamar ba a jikinta yake ba,ga shi duk haushi ya cika ta a haka ta ɗauki jakar da banu ko sisi a ciki takaicin ma da har da wayoyinsu aka ƙwace.
Haka suka tashi suna tafiya kamat masu tatata, Momi a gaba zanin nan a tattare a hannunta Meenal tana biye da ita, Meenal ta ce

"Wallahj Momi ina ga mutanen nan ƴan iska ne, ni fa ɗayan nan sai da ya jimƙe hannunsa ya dage ƙarfinsa ya kirɓa mini naushi a mazaunai" Wani gajeran tsaki Momi ta yi ta ce

"Kukan daɗu kike Meenal wallahi allon kafaɗar nan tawa kamar an buga mini filankin katako, wai hannu ne ya yi wannan aiki, ba gwara ma mazaunai wajen tsoka ba ne ni fa wajen ƙashi ne kin ga ai ni na ji abin da na ji, daga rakiya haka kawai an illa ta ni gani nan duk na fita hayyacina" Banza Meenal ta mata don ta ga kamar ma bata damu da abin da ta faɗa ba, haka suke ta tafiya amma sun kasa ganin ko mashin ne.

Suna cikin tafiya sai suka wani ƙaton mutum a amalanken shanu haka suka tare shi dama daga wata hanya ya ɓullo, suna ɗaga masa hannu da maaa magiya sannan ya tsaya, ganinsu a firgice sai ya ƙara ɓata rai, nan Momi ta dage tana sheƙa masa ƙarya cewa zumunci za su je waji kauye m nisa ziyara shi ne suka haɗu da haɗarin ƴan fashi suka musu duka duka musu ƙwace, shi dai bai ce komai ba sai cewa da ya yi su shiga tun da sun nema ya rage musu hanya. Dakyar yake tafiya su dai suna baya sun zazzaunai suna tafiyar dakyar ƙiƙar ƙiƙar.
Suna cikin tafiya tsabar wahala Momi tana jingina bayanta sai kawai gyangyaɗi ya kwashe ta, a cikin bacci ta yi mafarkin sun cim ma mummunar manufarsu, Meenal ta mallaki manyan gidaje da motoci suna mulkar Ibrahim yadda suka so. Meenal da ta kalli Momi tana gyangyaɗi har neman tuntsurawa take sai abin ya ɓata mata rai a nata ganin su da suke cikin wannan yanayin ina suka ga damar wani bacci in banda dai shi bacci ba ka sanin lokacin zuwansa.

Wasu ƴan mata ne suka ɓullo su biyu daga wata siririyar hanya, ya kasance suna gaban su Momi kamar an ce yanmatan su ɗago suka hangi amalanken shanun nan suna ganin mau tuƙawar sai suka kwasa a guje suka koma hanyar da suka fito suna faɗin

"Audu kwarto, Audu kwarto" Momi wannan ihun ne ya falkat da ita daga ɗan guntun gyangyaɗin ita kuma Meenal sai ta fara tunanin inda kwarton yake, kamar daba sama suka ji muryar mai amlanken ya ce

"Ƙarya suke mini"

Momi a zuciyarta ta ce

'In ba rami mai ya kawo rami?" ,Wato da shi suka tun da kaf dajin babu wani sai shi, kallon kallo aka shiga tsakanin Momi da Meenal don mutumin wani jibgege ne dukwanda ya sake ya damƙe shi to bai isa ya ƙwace ba. Shi kuma ya ji haushin bayyanar ƴanmatan don ya san da gaske suke tin da shi ne yake lalata ƴaƴan mutane.

Momi da ido ta yi wa Meenal signa duk da Meenal ta saba da banbaɗar da mutuncin ta ga maza sai ta ji wannan tana shayinsa shi kuma dama a nasa ƙudurin sai ya ƙarasa fa su gidansa da yake wata hanya zai tilasta musu shiga gidan don zai sanar da su zai ɗauki wani saƙo sai su wuce amma ba saƙo zai ɗauka ba, dama zai sheƙe ayarsa ne a tattare da uwa da ƴar gabaɗaya wato Momi da Meenal.

Momi ba ta yi wata-wata ba ta yi tsalle ta dira ita ma Meenal ta mara mata baya, Audu kwarto sai jin dirarsu ya yi da yake shi ya mayar da hankali gabansa, ai kuwa ya ji haushi domin ya gama sakawa a ransa cewa ya samu mata har biyu kasancewarsa hariji.

Momi suna dira suka yanke wata hanya a guje ko waiwaiye ba sa yi don ita Meenal hatta jakarta ta barta a cikin amalanken shanun, Momi da take ɗingishi lokacin tahowarsa amma yanzu ta ware ƙafa sai zabga gudu take, tsayar da shanun ya yi ya diro duk da girman jikinsa ba ya jin nauyinsa lokacin gudu a kan cikar burinsa don haka ya gwammace ya bi bayansu in ya so idan yana da rabo ko ɗaya ce a cikinsu ya kama a dokar dajin ya biya buƙatarsa.

Meenal ce a baya Momi har ta fi ta ware ƙafa su duka ko ciwon jikin da suka ce suna ji na dukan da ɓarayin kuɗi da wayar nan suka musu ba sa ji, ta ware murya ta ce

"Momi ga shi nan ya biyo mu"

Momi da sauri ta waiwayo sai ta ga ya dage tana sheƙa gudu, su duka ƙafa mai na ci ban baki ba, suka ƙara zage dantse wajen zabgar gudun famfalaƙi. gudu suke babu mai ko takalmi domin sun watsar da su. Ganin yana neman cim musu ya saka Momi ta sha wata kwatar cikin ciyayi ta durƙusa Meenal ma ta mara mata baya, suna durƙushe a wajen suna hakin gudun da suka yi, sai ga Audun ya zo sai dai ya ga hanya ta rabu biyu sannan ya rasa ina suka bi ya duba sawun su ya ga babu hakan ya sa ya ɗan tsaya yana dube dube. Yana tsaye a dab da su sai dai ya basu baya ne, jikinsa yana bashi suna wajen domin bai ga samun su na wucewa ba.


Momi bakinta har kumfa yake wajen karanto ƙulaƙuzai wa to falaƙi da nasi, sai dai a hankli take yi ba a fili ba gudun tonuwar asirinsu. Ita Meenal sai zare ido take tana kallon girmansa hatta mazaunansa kaɗai girmansu sai ya tsorata mutum.

Momi ba ta dakata da adsu,a ba don ba ta san iya mugun nufinsa a kansu ba. Ɗan ja da baya ya yi sai kuwa ya yi wa ƙatuwar ƙafarsa masauki a kan hannun Meenal, wani raɗaɗi ta ji don haka ta shiga zare ido tana ƙoƙarin rafka ihu sai dai Momi tana ta mata nuni da hannu a kan ta rufa musu asiri kar ta yi ihun. haka ta daure tana rausaya kai tamkar mai magogon naƙudar haihuwa. Idanun ya kaɗa ya yi ja sai dai a zuciyarta tana jin kamar ta hankaɗa shi ɗan gyara tsayuwa ya yi hakan ya sa Meenal jin tamkar wanda ya murtsuka ƙafar tasa wato tsananin azaba ya ƙara ratsa ta Momi kuma sai jan addu,a take duk wacce ta zo bakinta daga inda take iya hango gaban rigarsa ya ɗaga sosai daga saitin mararsa hakan ya sa ta yi mugun gani duk da cewa daga gafe ne take hange. Ajiyar da take mararsa tana ta harbin iska da alama a buƙace yake hakan ya tabbatarwa da Momi duk macen da ya damƙa sai ta gwammace kiɗa da karatu.


Meenal tana ta hawaye cikin ikon Allah kamar wanda aka ce ya tafi sai suka ji ya ce

"Ina jin gaba suka yi sai suka samu mafaka shi ya sa ban gan su ba, bari na bi bayansu wataƙika sun sauka daga tsakiyar hanya ne suna bin gefe inda da ciyayi shi ya sa na daina ganin sawunsu" Yana gama faɗar hakan sai ya zabga da gudu ya ci gaba da tafiya. Meenal ta ce

"Momi wayyo hannuna kalli yadda ya kumbura" Momi ta ce

"Meenal wa yake ta kumbuarar hannu, ki tashi mu kama hanya kar ya dawo ya iske mu a wajen nan, don wallahi wannan ya samu mace sai ya kumbura mata matantaka in ma bai ɓarɓarka ta ba" Babu yadda suka iya haka suka tashi cikin lallaɓawa suka kama hanyar da suka baro tun da ba zai yiwu su ci gaba da tafiya ba, gudun kar su yi arangama da shi!.

Gudu suka babu ƙaƙƙautawa har sai da suka ga sun zo bakin hanya" Sai haki suke suna da na sanin hawa amalanken Audu kwarto. Motoci suna wulgawa sai dai duk wacce suka tsayar sai su ƙo tsayawa don ana musu kallon kamar basu da cikakken hankali duba da kowacce babu takalmi sannan kuma kowacce ba ta da nutsuwa.


Dakyar suka samu wani mai mota ya ɗauke su da suka faɗa masa ziyara suka je ƙauyen ƴan uwansu a hanya ɓarayi suka tare su suka musu ƙwace tare da musu dukan tsiya, ya taimaka musu donnhat ƙofar gidan Momi ya kawo su, saboda ba motar haya ba c kuma shi kaɗai ne a motar. Godiya kamar za su ari baki. Sai da suka dawo gidan ƙofar gidan ma sai ɓalle ta aka yi don mukullin ma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login