Showing 141001 words to 144000 words out of 178828 words

Chapter 48 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt

18 Dec 2025

1449

ganinsu ta yi da shirin fita Sasiyar tana sanye da atamda glitter da ta saya a wajen maman afrah an mata ɗinkin ya yi kyau sai hinabi mai ƙasan net wanda yake pink ya yi daidai da wata ƙananun fulawowi pink da suke jikin atamfar sai takalmin ta marar tudu. Ta yi kyau sosai ga Kalifan ma sanye da riga da wando ƴan kanti sun yi kyau da ɗan takalminsa sosai suka fito abinsu sai kawai ta ji ƙyashi cewa wannan fa da kuɗin sana,a Sadiyar ta saya tun da ta san cewa Nasir ba zai saya musu ba. A zuciyarta ta ce

'Wannan matar matuƙar tana sana,a za ta fara haɗa kafaɗa da ni tabbas amma zan yi maganin abin' Ko kallo bata ishi Sadiya ba ta kama hannun Kalifa suka fice daga gidan sai ƙaran rufowar ƙofar gidan ta ji.

Ranta yana ta ƙuna ta koma ɗakinta. Can zuwan an jima ta ji ana ta buga gidan ta taso rai a ɓace ta zo ta ce

"Wai waye? Bashi ko tara za a damu mutane da buga ƙofa?" Muryar wani namiji ta ji yana tambayar mai gidan yana nan ta ce masa ba ya nan ta juya tana jan wani tsaki ta dawo gidan kamar an ce ta duba ƙasa a gabanta sai kawai ta ga mukullai, kallon mukullin take sosai tana son sanin mukullin mene ne don ta san ba na Nasir ba ne. A zuciyarta ta ce

"Sadiya" Kai ta shiga gyaɗawa alamar tabbayarwa ta tsugunna ta ɗauka tana duba mukullan a take wani tunani ya faɗo mata, da sauri ta koma ta sakawa ƙofar gidan sakata ta dawo da sauri mukulli ɗaya ta saka anjikin ƙofar ɗakin Sadiya sai ya shiga sai dai bai buɗe ba sai da ta sake gwada wani ya buɗe ƙofar wani tsalle ta yo da ihu a fili ta furta

"Tsuntsu daga sama gasasshe" Falon ta shigo wani ƙamashin freshner mai sanyin ƙamshi ya dakar mata hanci ko ina tsaf a gyare wajen freezer ta nufa ta buɗe tana taɓe baki sai ta ga babu komai a ciki an ma goge ta tass. Wani tsaki ta ja a fili ta ce

",Ba ke ce a gabana ba, bakya cikin target ɗina, tun da ke na gama da nake ɓangaren tun da an cire wutar nepar baki da sauran wani amfani sai zama a wajen" Ta faɗa tana jan murfin ta rufe freezer ta nufi cikin bedroom. Yadda gadon yake a ɗame shi ne abin ya bata mamaki sannan zanen gadon fari ne tass mai manyan flowers blue baki ta taɓe tana kallon kayan kan madubin.

A fili ta ce

"Yanzu zan yi abin da ya kawoni" Ta faɗa tana ajiye mukullin hannunta da yake da ta buɗe ƙofar da shi ta shiga, tana ajiyewa a zuciyarta ta ce

'Da zafi-zadi ake dukan ƙarfe, kuma da sanyin safiya ake kama fara, ba zan tsaya kallon ruwa kwaɗo ya mini ƙafa ba, in dai zaman kishi ne ni babu macen da za ta iya gagarawa da ni domin sai na mata kishi da kissa ƴar ƙasa yadda sai ta ji tsanar gidan mijin da kanta don sai na takurawa kishiya" Ta faɗa tare da buɗe drower Sadiya ta shiga bincike kayan kawai take watsowa ƙasa amma bata ga abin da take nema ba. Haka ta gama bincikenta ta mayar da su yadda suke tamksr bata taɓa su ba domin ta iya takunta.

Haka ta gama dubawa amma bata ga abin da take nema ba, ranta sai wuya yake saboda ta san tabbas yau wata dama ce da ta samu wacce ba lallai ta same ta ba. Ƙarƙashin gado ta shiga dubawa amma bata gani ba, tsaye ta tashi ta tsaya rana riƙe da tsantsa ta damƙe fatar bakinta da haƙorinta na sama. Duk cikin wani abu da take gani za a ɓiye abin da take nema ta duba amma bata gani ba, gadon ta taka ta duba saman drower nan ma babu sai da ta sakko ta lura da ƙaramar lokkar jikin bed side drower da sauri ta jufi can ta buɗe sama da ƙasa amma babu. Kasancewar biyu ne sai ta koma ɗaya gefen ta buɗe ta saman sai ta ga panties ɗin Kakifa ne a ciki wanda suke a laye, tsaki ta yi ta tuƙunɗuna su ta tura ta rufe lokar, tana janyo ta saman sai ta ga wata ƙaramar jaka pose taɓa jakar ta yi ai kuwa ta ji ɗan tudu da sauri
ta fito da jakar tana fatan a dace tana buɗewa kuwa ta ga abin da take nema wani murmushi mai bayyana haƙora ta yi ganin kuɗaɗen a ciki a laye suke kasancewar pose ɗin tana da ɗan girma, ƴan dubu dubu ne a laye sai ƴan ɗari biyar biyar sai ɗari bibiyu da ƴan ɗari ɗari. Ganin kuɗin cunkus sai abun ya bata mamaki a ƙiyasce tana tunanin kuɗin nan zai iya kusan kaiwa dubu ɗari. Fito dansu ta yi duka ta zige zip ɗin ta buɗe ɗaya gefen sai ta ga ƴan hamsin hamsin ne da sauran canjuna a ciki su kuma dai ba su fi dubu biyar ba fito dansu ta yi duka a fili ta furta


"Wai dama sana,ar cikin gida tana kawo kuɗi har haka? Lallai wannan ake cewa bar ganin ka tara ka kiyayi mai nema ashe har tana samun rufin asiri a sana,arta haka lallai na yi sake!" Ƙaran bugun ƙofar gida ne ya ankarar da ita vata san lokacin da ta tashi tsaye daga zaunen da take ba, ga kuɗin duk ta baza haka ta shiga haɗa su tana karkarwar jiki don ta san asirin ta zai iya tonuwa tunanin ta ma Sadiya ce ta dawo duba mukullin da ta jefar. Lokar ta mayar ta rufe ta naɗo ƙasan rigarta da ta zuba duka kuɗin sai da ta zo faon a guje sannan ta tuna da mukullin da suri ta juya ta ɗakko har lokacin tana ji an bugawa fitowa ta yi amma bata rufa ɗakin ba ta ce

"A nan ne? Waye?" Ta faɗa tana jiran jin muryar Sadiya kawai sai ta ji muryar wata yarinya ta ce


" Mango da zoɓo za a bani" Wani uban tsaki ta ja ta ce

"A kan wani mango za ki zo ki damu jama,a to an dajna siyar da mango da zoɓo a nan" Yarinyar ta ce

"To akwai pure water?"

Meenal ta ce

"Babu pure water sai ubanki" ,Ta faɗa a zuciye yarinyar ta ce

"Na gane ki ba anty Sadiya ba ce kishiyarta ce ƴar baƙin ciki wataƙila antyn bata nan" Tana faɗar hakan ta ɗauki dutsi ta buga a ƙofar da ƙarfi ta zuga da gudu, Meenal tana so ta zo ta buɗe ƙofar ta kikkifawa yarinyar mari amma kuma abin da take yi ya fi wancan. Ɗakin ta koma ta ɗakko jakar ta rufe lokar ta tsaya ta tabbatar da komai yana yadda yake ta fito ta zo ta kulle ɗakin. Ɗakinta ta nufa da sauri ta je ta juye kuɗin a jakarta ta fito da pose ɗin a hannunta kicin ta je ta ɗakko ashana ta xo ta kyarta ta sakana jikin pose ɗin ganin jakar ta kama ta sheƙe da dariyar mugunta, sai da ta ƙone ƙurmus ta tattara ta kwshe ta je ta yi fuloshin ɗinsa a toilet.

Mukullan ta ɗakko ta zo wajen zaure ta jefar da su a ƙasa ta koma ta kwanta a bedroom ɗinta tana lissafa kuɗaɗen da ba da guminta ba ta samu tana jin daɗinsu.

A fili ta ce

"Sadiya mu zuba ni da ke yanzu dai baki da tsumi baki da dabara idan musgunawa ta ta ishe ki ke da kanki za ki san na yi" Tana cikin wannan maganar sai sheɗan ya ƙara kissima mata wani mugun abun da sauri ta tattara kuɗin ta mayar tana mayar da jakar drower ɗinta ta fito daga ɗakin, mukullan ta sake ɗauka sai kawai ta nufi kici ɗin Sadiya ta buɗe ta dawo ta buɗe ƙofa ta aiki wani yaro ya siyo mata kananzir ta rufe ƙofar ta je ta yi abin da za ta yi ta mayar ta rufe ta ta kai ƙaramar jarkar lemon coca cola da aka sayo a ciki ta ba wani almajiri shara ya zubar mata dama jarkar tana ciki.


Sadiya sai bayan magriba ta dawo bata ma san ta jefar da mukullin ba sai da ta dawo ta buɗe aljihun jakarta ta ga ba ya nan ɗan ja baya ta yi tana haska fitilar wayarta kawai sai ta ga Kalifa ya miƙo mata mukullan ta tambaye shi sai ya nuna mata ƙasa kusa da inda take tsaye hakan ya sa ta gane a gabanta ya ɗakko sai ta yi tunanin yanzu da ta buɗe jakar ya faɗo bata sani ba.

Hankali kwance ta buɗe musu ƙofar suka shiga don zuciyarta wasai take ji babu damuwa domin Kaka ta mata nasiha da kuma ƙara bata haƙuri a kan lamarin zaman auren ta tana nuna mata komai ya yi farko yana da ƙarshe don kowace gona tana da kunyar ƙarshe ta faɗa mata idan dai mace ta haɗu da fitinanniyar kishiya ko fitinanniyar uwar miji ko dangin miji sai ta yi haƙuri duk mai haƙuri watarana zai dafa dutse har ya sha romonsa. Ta ƙara koya mata dabaru da kissa da za take nunawa kishiyar duk abin da take mata ba ya damun ta.

Sai batun ƙauracewa ɗakinta da Nasir yake da ma ƙaurace mata baki ɗaya shi ma ta ce ta yi haƙuri lokaci ne, sannan shi lokaci alƙali ne watarana da kansa zai neme ta don Kaka ta faɗa mata cewa namiji tamkar sauyin abinci haka ya ɗauki mace ta bata misali da cewa shin za ta juri cin abinci ɗaya kullum? Wato koyaushe a ce ta ci shinkafa da miya sai Sadiyar ta nuna za ta so sauyi watarana mana yau ta ci shinkafa gobe taliya jallof jibi wake da shinkafa ta haka Kaka ta nuna mata cewa to akwai ranar da Meenal za ta gunduri Nasir ɗin ya ji yana son kasancewa da Sadiya don kowacce mace halitta da baiwar ta da ban wata ta fi wata kawai dai idan kana da kyau sai ka ƙara da wanka!.

Sai da ta buɗe drower za ta ɗakko rigar bacci bayan ta yi wanka sai kawai ta ga kamar dai kayan ba haka suke ba, saboda Sadiya tana da lura da al,amura kawai sai ta fara zargin kayanta ba haka ta bar su ba duk kuwa da Meenal sai da ta gyara komai, a ƙarshe Sadiyar ta saka a ranta cewa ita da ta kulle ƙofar ɗakinta kuma ma ai babu yadda za a yi a shigo mata ɗaki me ma za a yi a ɗakinta.


Bayan sun kwanta Kalifa ya yi bacci, don tana jin lokacin da Nasir ya dawo amma ko ɗakinsu bai zo ba dama kuma ta san da hakan. Kuɗin da maƙociyar Kaka ta bata na kayan kori da spices da ta ce a turawa maman afrah za a kawo musu curry kwano ɗaya spices na shayi rabin kwank sai spices na girki kwano ɗaya, jan yaji rabi yajin daddawa kwano ɗaya, sai kuma kuka da kuɓewa da niƙƙaƙƴiyar daddawa. Don ita ma natan babu, kuɗin ta ɗakko ta lissafa tana tunanin da safe za ta yi wa maman afrah magana ta tura kuɗin sai a sako musu a mota. Lokar da take ajiye kuɗaɗenta ta buɗe za ta saka kuɗin a ciki domin tana da kuɗi a monie point sai ta yi wa maman afrar transper, tana buɗewa ta ga wayam babu jakar gabanta ya buga da mugun ƙarfi, ta sake dubawa amma babu jaka babu alamar ta, lokar ta ciro daga ciki dukanta ta shiga leƙwa amma jakar ta ce ɗaukeni inda kika ajiye!.

MAMAN AFRAH
09025576222






https://chat.whatsapp.com/DDmSp3AUB7gJnJQLnau59V?mode=hqrt1



*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)


NA


MAMAN AFRAH


. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*

BOOK 1

PAGE 2️⃣6️⃣



SADIYA

"Innalillahi wa inna ilaihi raji,un" Sadiya ta furta a fili tana miƙewa tsaye ta shiga dudduba wajen tamkar dai jakar za ta gani gabanta yana faɗuwa ta shiga dubawa amma bata gani ba duk hanklinta ya tashi saboda kuɗinta ne da take son fita kunya idan ta haihu duk wani tanadinta yana cikin kuɗin amma ta rasa yadda aka yi ta rasa jakar, tun da ta tabbatar a lokar ta saka tun da kafin ta fita ma ta saka kuɗi a ciki. Da sauri ta janye ƙaramar bedside ɗin daga wajen ta duba bayan bed side drower ko ɓera ne ya ja don ra fara tunanin ko lokar a fashe take daga baya amma sai ta ga babu wani waje da yake da alamar fashewa a jiki.

Lokar saman ta janyo tana birkicewa wai ko dai a ciki ta saka duk da Sadiya bata da mantuwa komai nata a nutse take, ma,ana ta san a lokar da ta saka kawai dai tana dubawa ne amma wayam babu ko alamar jaka bare a je batun kuɗi.Birkice ta shiga yi a ɗakin amma babu jaka babu alamarta haka ta fito falo kamar zautacciya domin ita ta san irin wahalar da ta sha a kuɗin tun da halaliyarta ce duk wani mai neman halal kuwa ya san neman halak da wuya!.

Duk hankalinta ya tashi sai da ya dawo ta ga kuɗin da ta karɓo na curry da sauransu sai ta yi tunanin wancan kuɗin ne da take nema amma sai da ta zo ta tuna haka ta dawo ta zauna tana ta ambaton Allah a zuciyarta har dai ta samu nutsuwa a zuciyarta. Tana iya jiyo ƙaran TV daga ɓangaren Meenal kuma ta san shi ma mai gidan ya dawo amma ko leƙo ta bai yj ba domin ta ji zuwansa.

Ita dai ta san ɗakinta a kulle kuma ko ma ba a kulle ba abu sabo abu ne da ba a taɓa.yimata ba wato sata, saboda ta san in har ba ita ta yi niyyar yin alheri ta ba mutum kuɗinta ba babu mai ci sai dai ko Nasir idan son kuɗinsa ya tashi ya ce ta bashi don kawai taƙamar tana matarsa bayan kuma shi ba bata yake ba. Haka ta jure ta haƙura ta kwanta tun da babu wanda za ta tunkara da maganar, haka ta yi addu,a ta kwanta tana ta tunani da ciwon rai ya ishe ta kawai sai hawaye ne suke zuba, ta jima tana hawayen nan har da sheshsheka kafin daga bisani bacci ya yi awon gaba da ita bata falka ba sia wajen ƙarfi biyu da kwata haka ta tashi ta yi alwala ta yi nafila bayan ta idar ta zauna ta yi karatun qur,ani sannan ta karanta sunanyen Allah tare da salatin annabi S.A.W ta ɗaga hannu ta ce

"Ya Allah kai kake ƙaddara komai a lokacin da ka so, ya Allah na san kai kake bayarwa kuma kai kake hanawa Allah ka san damuwata a kan jakata da na rasa ya Allah idan rabona ce ka bayyana min ita idan kuma babu rabona ka sauya min da abin da ya fi alkairi, na yarda da duk wani abu da za ka ƙaddara min" Haka ta gama faɗawa ubangiji tana hawaye tare da jero wasu buƙatub nata sannan ta ƙara yin salatin annabi S.A.W ta shafa addu,ar Ta koma takwanta sai ta ji zuciyarta ta yi wani irin sanyi duk damuwa da nauyin da zuciyar ta yi babu shi!.
Da asuba ta yunƙura dakyar ta yi sallah ta sake karatun qur,ni da yin addu,o,in ta.

Da safe da ta fito sai take jin duk babu daɗi yadda babu nepa a ɓangarenta ita bata san ma wanda za ta faɗawa ba, ɓangarenta basa son ta kai ƙaransa shi kuma nata ɓangaren basu damu da ita ba basu san muhimancjn ta ba, sai dai kawai ta san akwai sakayya. Tsakar gidan ta nufa, da yake wajen ƙarfe bakwai ne ruwan zafi za ta ɗora saboda yunwa take ji kasancewar mace mai ciki akwai jin yunwa, ga shi kuma ita bata da nepa bare ta jona a nepa. Tana zuwa ta buɗe kicin ɗin sai lokacin ma ta tuna gawayin nata ya kusa ƙarewa, a haka ta ɗauke na ƙasan buhun duk da ya zama ƙareci duk ƙanana ne, ta samu ta hura da ya kama ta ɗora ruwan. Waje ta samu ta zauna a kicin ɗin tana jiran ruwan ya tafasa tana zaunen tana kallon kayan sana,ar da suke gefe a cikin kicin ɗin aajiye manja farin mai da sauransu tana tuna yadda jakar kuɗinta ta ɓace jiya, tunaninta ɗaya yanzu idan suka ƙare yadda za ta haɗa kuɗin ta saro wasu domin ba lallai ta haɗa kuɗin ba kasancewar asarar da ta same ta duk da ta san Allah ne ya ƙaddara mata.

Da ta dama kokon, sai ta ɗauki sauran fulawar da ta rage mata wacce ita ta saya ta kwaɓa ta musu waina ta saka a fulas ta gaa sai ta ɗora ruwan zafin wanka wanda ta san ma ba lallai gawayin ya isa dafawa ba. Kicin ɗin ta janyo bayan ta ɗakko jug ɗin kokon da kuma kwanon wainar. A falo ta ajiye sai ta koma ta ɗakko plate da kofi da cokali ta dawo ta zuba wainar da kokon da ta saka sugar ta zauna tana ci bata ma ra,ayjn ci da ya ji sai da ta ji ta ƙoshi ta rufewa Kalifa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login