Showing 81001 words to 84000 words out of 178828 words
Chapter 28 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt
je kasuwa ba, ya kasa fita saboda gani yake tamkar igiyar Sadiya ce za ta tsinke idan ya bar gidan, wato kamar in baya nan Nasir zai dawo ya kawo takardar saki, amma idan yana nan ko da ya zo da niyyar sakin zai roƙe shi ya fasa sakin. Har wajen goma wayar bata shiga, wayar Arfat Baba ya karɓa ya saka lambar Nasir ya hau doka masa kira sai kuwa ya ɗauka da ta kusa katsewa.
Nasir ya ce
"Hello" Baba ya ce
"Buɗe muryarka da kyau Babanka ne mahaifin Sadiya" Da sauri Nasir ya cire wayar daga kunnensa ya duba ya dai tabbatar da numbar Baba ba ce dona ya san ya saka duka lambobin Baba a black list. Jin haka sai Nasir ya ce
"Hello ba na ji" Ya faɗa yana ciro wayar daga kunne ya shiga hura iskar bakinsa da ƙarfe, yadda Baban zai ji, Baba jin haka ya buɗe baki yana faɗi
"Baka ji na Nasir" Nasir da sauri ya katse kiran, yana shirin saka lambar a black list sai kiran ya sake shigowa haka ya ɗauka Baba ya ce
"Nasir mai ya sa ka kawo Sadiya gida" Nasir yana taɓe baki ya ce
"Laifi ta yi" Baba ya ce
"Amma wannan an yj shegiyar yarinya amma ta ce babu abin da ta yi ka kawota" Nasir ya ce
"Ruwa ai ba ya tsami banza" Nan Baba ya shiga bashi haƙuri duk da bai ji laifin da ta yi ba yana cewa zai saɓar mata Naair ya ce
"Baba kawai a kan maganar matar da zan aura za ka ja mata kunne, ta ce bata son raini in ya so yanzu zan kira wacce zan aura ɗin sai na faɗa mata ka bani haƙuri in ta haƙura to" Baba tsabar son zuciya bai ma ji zafin maganar Nasir ba ya ce
"Amma Sadiya an yi sakarai kishiya ai abokiyar zama ce, kuma ita a gidan ubanta ba mata huɗu ta tashj ta gani ba, ka bata haƙuri za a ja mata kunne" ,Nasir ya amsa yana kashe wayar, don dama jiya daga gidan Baba gidan Hajiya ya je ya faɗa musu komai sai dai su Husna suka ce kar a sake ta saboda gwara ta zauna ta ƙunshi baƙin ciki. Haka Nasir ya kira Meenal ya bata haƙuri yana faɗa mata wai Baban Sadiya yana bashi haƙuri don kamar ma a muryarsa kuka ya ji yana yi, saboda tsabar ƙarya irin ta Nasi, iya kuma Meenal kanta ya mata girma jin ana bata haƙuri kuma yanayin yadda aka ce Baban Sadiyar ya bata haɗuri hakan na nufin Sadiyar bata da wani galihu a wajen ubanta, domin haka ya sa ta ƙara ɗaura ɗamarar yin duk yadda ta so idan ta shiga gidan, don mayar da Sadiya gida da ya yi ba ƙaramin matsayi ta gane tana da shi a wajen Nasir ba don har Hibba ta kira ta tana faɗa mata yadda aka mayar da Sadiyar gida, sosai abin ya faranta mata, sai dai abin da bata sani ba shi lamarin duniya yau naka ne gobe na ɗan uwanka, in dai namiji yana wulaƙanta matarsa to indai ita wacce bata shigo gidan ba tana da hankali to ba murna ya kamata ta yi ba illa jajantawa kanta, tun da duk abin da aka yi wa ta cikin gidan ke ma wataran zai iya miki.
Mama Habiba wacce ta shigo ɗakin Baba ta same shi yana waya ta ce
"Wallahi abin da kake baka kyautawa, kai ba za ka ƙwatawa ƴarka ƴanci ba sai dai ka zubar mata da kima a gidan aure, baka san wannan zubar mata da daraja zai yi a wajen miji da kishiya kai har ma da dangin mijin ba, ai kamata ya yi ka nuna musu ita ma ƴa ce ka nuna ƴarka ta fi ƙarfin wulaƙanci, ka nuna masa tana da gata tana da galihu sannan kuma ko yau ya sakar maka ita za ka iya riƙe ƴarka, amma ya kawo ta gida ya tafi ka kasa samunsa a waya ka ɗauke ta ka matar da ita yanzu ka ari waya ka kira shi yana maka maganar banza. Ai ita mace tana da kima da daraja, kuma kamata ya yi a kowane lokaci a sauarari kukanta a ji matsalolinta da take ciki na gidan aure, a maganace mata matsalarta a ƙalla wannan shi ne gatan da za ta samu, kuma mijin ma ya gane ba shi kaɗai ne gatanta ba anuna masa ta fi ƙarfin wulaƙanci, amma kai da ya maka laifi ya dawo maka da ƴa babu wani dalili me ƙarfi ka zo kana bashi haƙuri shin wannan kaɗai ba zai saka gobe ma ya ƙara ba?K... Miƙewar Baba tsaye a zafafe ya hana ta ƙarasa maganaryana kumfar baki ya ce
"To uwata Habiba faɗa mini yadda zan yi tun da ke ce mijin ni ne matar" Mama Habiba ta ce
"Ni dai ban ce ba amma ita gaskiya dama ɗaci ne da ita" Baba ya ce
"Kin zo kina ta tada jijiyoyin wuya, shin ke kin san ciwon ɗa ma? Ke da baki taɓa sanin zafin ɗaukan ciki da naƙuda ba baki san ya son ɗa yake a zucuyar iyaye ba har kika zo kina wata maganar banza" Jin furucinsa ta tashi tsaye ba tare da ta ce komai ba ta juya ta fice a ɗakin ra saka takalmin ta ta tafi.
Baba kuwa Nasir ya ƙara kira sai Nasir ɗin ya ce babu komai, don dama ita ma Meenal an gama zugata a kan cewa kar ta yarda a saki Sadiyar ta bari su zo su jera don Sadiyar ta fahimci ruwa ba sa,an kwando ba ne.
Hakan ya sa Baba ya ji daɗi a ransa a ƙalla dai daga ƙarshe Sadiya za ta koma ɗakinta tun da ba sakinta aka yi ba, Arfat ya ba wayarta ya je ya samu Sadiyar ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, yana ta batun kar ya sake jin an kawo ƙaranta a kan ta yi wa matar da Nasir zai aura wani laifi don haka ta saka a ranta ba da ita kaɗai zai rayu ba sannan ko bayan an yi auren idan ma cewa Nasir ɗin ya yi take gaishe da matar tasa to take yi ai durƙusawa wada ba gajiyawa ba ne kuma zama lafiya ya fi zama ɗan saki.
Ƙirjinta tamkar an saka dutsi haka take jin zafin maganganun Baba amma ta danne ta amsa masa, saboda yin biyayya ya zama dole tun da bai saɓawa addini ba.
A take ya saka ta shirya ya ce ta kama hanya ta tafi har da bata kuɗin napep ɗari biyar. Tana fita ya tafi kasuwa, ita kuwa dama gidan maƙota ta shiga ta saka yara suna duba mata ana cewa ya tafi ta dawo gidan, sai da la'asar sannan ta tafi saboda Mama Habiba ce ta ce ta yi haka kar ya ga ta koma da safen wani rainin ya biyo baya duk da dai babu rainin da Baba bai ja mata ba.
Babu wanda ma ya kawo ta a ka bare har a faɗa masa cewa bata tafin ba.
JIDDA
Har ya gama waya da Mummy amma Jidda ko motsi bata yi ba bare ya sa ran za ta tashi, ƙara gyara filonsa ya yi ta hanyar daidaita kansa bisa filon, hannunsa ya rungume a ƙirjinsa idanunsa ƙirrr a kan kyakkyawar fuskarta da yake jin babu wata mace da ta kai masa Jiddansa kyau, sosai yake jin sonta da sabuwar ƙaunar ta da ta ƙara dasawa a zucuyarsa a daren jiya yana ƙara huda masa zuciya, lallai ya yarda babu abin da ya fi ga ɗiya mace sama da ta kai mutuncin ta gidan aurenta, saboda hakan ba ƙaramin daraja yake ƙara mata ba wacce ba za ta yanke ba har abada a wajen mijin nata, domin yau sai ya ji kima da darajar Jidda ya wuce na koyaushe a zuciyarsa sannan alƙwari ne ya ɗaukawa kansa cewa zai kula da ita sannan ya mutunta ta don ta sadaukar da komai saboda shi, idan ya ce komai ciki har da aurensa.
Idanunsa suna a kan fuskarta bacci ya ƙara wartarsa, bayan wani lokaci kaɗan Jidda ta ɗan yi motsi sai kuma ta runtse idanunta da ƙarfi kafin ta ɗan buɗe su, ata musu masauki a ko ina ba sai a kan Ibrahim da yake bacci, ita kanta ta ba kanta dariya domin kuwa sai da ta ji gabanta ya ɗan bada rass sakamakon ganinsu a gado ɗaya sai sannan ne ta tuna ashe fa sun yi aure!. Murmusawa ta yi a lokaci guda tana tuno da ƴar uwarta Aliya tana rayawa a ranta cewa Aliya ma ta kwana cikin wannan shauƙin mai wuyar fassaruwa. Zaune ta tashi tana son ta sauka ƙasa don zuwa ta samar da abin da za a yi break fast da shi, tana zura ƙafafunta ƙasa Ibrahim da tun tashin ta zaune motsin ta ya katse masa baccin. Tana dab da sauka sai ta ji an riƙo mata hannu wata kunya ce ta turnuƙe ta tana ta tunanin da wane ido za ta kalle shi, sai ta ji ya ce
"Haka ake tashi daga kan gadon miji babu sanarwa? Ko dai sai na koya miki yadda ake kula da miji?" Ya faɗa yana kama ɗaya hannun nata ya juyo da ita suke fuskantar juna amma yana daga kwance, ita kuma duk kunya ta lulluɓe ta sai kawai ta sunkuyar da kai tana kallon ƙasa sai dai yanayin fuskarta yana nuni da mrmushin da take da alama maganar da ya yi ce ta bata dariya.
Bai jira mai za ta ce ba ya ce
"Ai ni in baki iya kula da ni ba sai na koya muki yadda za ki kula da ni, amma sai kina buyana albashi duk wata" Bata san lokacin da dariya mai sauti ta suɓuce mata ba, bata san mai ya sa su maza basa jin kunya ba. Tana cikin wannan dariya ta ji ya ce
"Wato dariya na baki ko? To tayani in tashi zaune, kin san yana daga cikin ba mijin kulawa matarsa ta kama hannunsa ta tashe shi zaune" Idanu ta runtse ta ma rasa ya za ta yi ko dai ta furta masa da bakinta cewa kunyarsa ta mata shamaki da furta komai sai dai laɓɓanta sun ƙi bata haɗin kai. Yana riƙe da hannuwan nata ya tashi zaune sai dai bai sakar mata da ƙarfinsa ba, sai da ya zaune gwiwarsa tana jingine da jikinta ya ce
"Kar ma ki ce ke kika ɗagani domin ni na tashi kaina, ai ni yanzu na gane bani da gata ita ma Mummy ɗazu da ta kira ni sai faɗa take kar na bar mata ƴa da yunwa, Allah sarki ni babu mai kulani sai dai ko Daddyna" Idanunta a ƙasa ta ce
"Shi ɗin ma Daddyna ne" Bakinta ya ƙurawa ido yadda ta yi maganar tamkar ba daga bakinta maganar ta fito ba, sakin ɗaya hannun nata ya yi ya saka hannunsa ɗaya ya ɗago haɓarta idanunsu suka sarƙe da na juna duk wanda zai ga yadda kallon yake wakana haƙiƙa zai gane soyayya ce mai cike da ƙaunar juna, kulawa sadaukarwa haɗe da tsantsar yarda da juna ce a tattare da masoyan, sun daɗe a haka kowane ɗaya daga cikinsu ba ya son ya ƙifta musayar kallo ne na soyayya yake afkuwa, kowa ya tsinci kansa a yanayin ne ba tare da shiryawa hakan ba.
Ɗaya hannun ya kai ya riƙe gefen fuskarta ya ce
"Jidda ina ƙaunarki da dukkan zuciya da ruhi, hatta gaɓoɓin jikina kowace gaɓa ta san da zaman soyayyarki Jidda" Murmushi ta yi ta ce
"Ni ma ina ƙaunarka" Bata ankara ba ta ji ya saki riƙon fuskarta da ya yi da kuma tallafo haɓarta sai gani ta yi ya ɗaga hannu sama yana godewa Allah, ita ma sai ta tsinci kanta da ɗaga nata hannun tana maimaita duk wata godiya da kirari da ta ji yana yi wa ubangijin talikai.
Wanka suka ƙara yi da ruwa mai ɗumi bayan sun fito yana shiryawa sai suka ji horn hakan ya sa ya gane saƙon Mummy ya iso, yana jin lokacin da me gadin ya buɗe ƙofa.
A saman ta baro shi yana shiryawa ta sakko ƙasa bayan ta saka kayan da ta cire, Ɗakin da aka kaita ta shiga, ita sai yanzu ne ma take ƙarewa falon kallo tamkar a wata ƙasa take da ban. Bayan ya gama shiryawa cikin farar shadda gezna sai sheƙi take tana ƙamshi ga turaruka masu aji da ya feshe jikinsa da su. Nocking ya ji a bakin ƙofar ya sakko cikin nutsuwa yana ɗaura agogo a hannunsa, yana buɗewa mai gadi ya gaishe da shi cikin girmamawa, amsawa ya yi ya karɓa kwandon da ya kawo yana sanar da shi direba ne ya kawo daga gidan Mummy. Faɗwa mai gadin ya yi cewa ya san da zuwan nasa shi kuma ya juya Ibrahim ya rufo ƙofar ya dawo ya nufi kan dining ya ajiye kwandon amma a ƙasa a gaban dining ɗin.
Ɗakin ta ya nufa lokacin tana gaban drower ɗinta bayan ta bar gaban madubi inda ta tsaya shafa kwalakca da humra da sauran body spray da shuwa masu bala,in ƙamshi don kan madubin ya sha jere tamkar an je shago, drower da ta buɗe yadda kaya suke a jere sai da ta ji wani iri yau ita Jidda ce wacce Umma take ƙwace mata duk wasu kaya masu kyau da nagarta idan Abba ya ɗinka musu amma gashi komai ya zama tarihi tun da gashi yanzu kaya masu tsadar da bata tama tunanin ko a mafarki za ya saka irinsu ba.
Tabbas komai na rayuwa idan ka yi haƙuri zai zama tarihi watarana!. Yanzu gashi komai ya wuce, yana sako kanshi ɗakin tsabar ƙamshin turarukan da suka bugi hancinsa hatta sallama suɓuce masa ta yi, kasancewar tamkar wanda aka yi ɓarin turare a ɗakin abin birgewar ma ba za ka taɓa gane wane irin ƙamshin turare ba ne. Jin alamun mutum ya sa ta waiwayo kasancewar tana ɗaure da towel da yake da ta shigo kayan ta cire ta ɗauki wani towel sabo ta ɗaura, ganin ya tsaya a rungume hannunsa yana mata wani kallo bata san lokacin da ta ce
"Sannu da zuwa" Maganr tata ta bashi dariya sai ya ce
"Kin manta kin gaisheni ɗazu yanzu kuma sannu da zuwan ta mene ne?" Bata amsa ba din ita kanta ta ba kanta dariya. Bata ankara ba sai ta ganshi ya zo dab da ita ya kama dantsen hannunta duka biyu sai gani ta yi ya janyo ta ya zaunar da ita a bakin gado, wucewa gaban drower ya yi ya tsaya yana ta ƙarewa kayan ciki kallo amma sai ta ga ya rufe, wata ya buɗe sai kawai ta ga ya ɗakko wata riga daga gani ba za ta wuce gwiwa ba sannan sai aka mata ƙaramin hannu, daga gaban rigar akanyi hoton heart babba daga ƙara aka rubuta GIRL da manyan baƙi.
Miƙo mata kawai ya yi ya ce
"Ita nake so ki saka" Karɓa ta yi a ranta tana cewa
"Ka ji kaɗan ka ji da yawa, ni Jidda dama a gidan auren miji ne yake zaɓa maka kayan da za ka saka?" Ta tambayi kanta sai ta ji yana cewa
"Ba zan ɓoye miki ba Jidda tun da na shigo ɗakin nan na tsinci kaina a wani yanayi mai wuyar fassara, sai dai ina tausaya miki kasancewar daren ki na farko ne kuma na yi dogon zango amma ba don haka ba, da sai kin mayae da ni ruwa" Kallon rashin fahimta ta masa ya ɗora da faɗin
"Ina shigowa da na shaƙi ƙamshin turaren nan sai ya sakani a wani yanayi, tabbas turare yana taka muhimmiyar rawa wajen haifar da yanayi a tsakanin mace da namiji, shi ya sa aka haramtawa mace ta saka turare ta fita waje maza suna jin ƙamshin, dalilinnda ya sa ake rubuta mata alhakin zina saboda ƙamshi yana tada sha'awa ne duk wani namiji idan ya ji ƙamshin turaren zai ji sha,awarta" Kai kawai take kaɗawa bayaninsa yana shigarta duk da mafi yawan mata sun yi watsi da wannan maganar suna cin karensu babu babbaka, musamman da ya kasance yanzu har kabbasamata suke yi a kayansu, su gama turara kaya su saka su fita sun manta da haramcin hakan.
Yana faɗa mata ya buɗe ɓangaren bra da panties ya ɗakko mata fararen set ya bata, bra ɗin pant ɗin, ganin tana wani juyawa kamar kunya take ji sai ya fita yana dariya, ta saka tare da ɗora rigar da ya zaɓo mata, jin yana kiranta ta fito tana amsawa wani mugun kyau ya ga rigar ta mata hakan ya sa ya ga tamkar dama don ita aka yi rigar tabbas aure rahma ne, Allah azurta kowa da mace da kuma miji na gari.
ALIYA
Wani irin bugawa da ƙarfi zuciyarta ta yi har numfashin ta yana barazanar mata wahalar shaƙa, jin furucin Amataullahi, a take bakinta ya bushe babu ko ɗigon lemar da za ta sanya laɓɓanta da suka yi gaggawar bushewa su jiƙu. Bata san tana da zafin nama ba sai da ta ganta tsaye ƙiƙam a kan ƙafafunta da zuwa lokacin sun fara karkarwar gaza ɗaukar gangar jikinta ba komai ne abin da ya razana ta haka ba illa furucin Amatullahin da ta ce tarayyarta da Kasim sau ɗaya zai ruguza mata abubuwa dubu, sannan in har a tarayyar da aka yi an samu ƙaruwa hakan yana nufin zai barta da jelar ciki da reno ma'ana shikenan ya yi sanadin rugujewar burikanta ciki kuwa har da mallakar Ibrahim matsayin miji da kuma zama kishiyar Jidda don ta mata gashin ƙuma!.
"Hannunta yana dafe da ƙirjinta ɗayan kuma tana riƙe da wayar da take kunnenrta ta ce
"Na shiga uku Amatullahi, wallahi ya yi tarayya da ni" Amatullahi ta ce
"Wato ya kalamance ki da kalamansu na maza ko