Showing 12001 words to 15000 words out of 178828 words

Chapter 5 - RUWA CIKIN COKALI COMPELET BOOK BY MAMAN AFRAH.txt

18 Dec 2025

1478

ta saka wani kayan ta ɗakko kayan ta da ta ɗora a kan ƙofa da safe ta haɗa da wanda ta je makaranta da shi ta wanke ta shanya. Ganin rana ta yi sanyi ta sharo ɗakin nasu duk da babu datti, tsakar gidan ta fito ta share tas ta kwashe. Kayan wanke-wanke ta haɗa ta wanke, bata gama gyaran gidan ba sai da la,asar lis.

Butoci ta ciccika ta ajiye, lokacin Aliya suna ɗaki ita da ƙawarta Amatullahi.

Tahowa ta yi za ta kai kwando kicin cikin rashin sani ta bige Umma da ta fito daga kicin, a ƙufule Umma ta ɗaga hannu za ta wanke fuskar Jidda da mari, a daidai nan Abba ya shigo da sallama, turus ya yi yana kallon Umma...


MAMAN AFRAH
09925576222


*🩺 GHT HERBAL SOLUTIONS 🩺*
*Maganin da ke dawo da lafiya, da izinin Allah!*

Muna sayar da ingantattun magunguna na zamani da aka gwada kuma suka shaida aiki.


*Duk wannan cutar ana warke wa sosai mutum ya dawo nml*

*Ga wasu daga cikin cututtuka da muke da magani a kai:*
✅ Ulcer
✅ Hawan jini
✅ Ciwon zuciya
✅ Ciwon Suga (Diabetes)
✅ Ciwon daji
✅ Ciwon koda & hanta
✅ Zazzabi mai tsanani
✅ Ciwon gabobi & ciwon jiki
✅ Ciwon ido & kunne
✅ Asma, tarin fuka & mura
✅ HIV
✅ Matsalar rashin haihuwa
✅Gyaran data
✅Na kurajen fuska
✅Na rage kiban
✅Na Saka kiba
✅Na infection
🟢 Da sauran su...

*Me ya bambanta GHT?*
🌿 Magungunan mu halal ne kuma an tsaftace su.
🔬 Sun wuce binciken lafiya da gwaji.
🌟 Suna da matukar tasiri – an samu sauki ga dama-dama.
🧕🏽 Muna kula da sirrin marasa lafiya.
🚚 Muna da isar da magani kai tsaye (Delivery available).

*Kira yanzu ko shiga group ɗinmu don karin bayani da order:*
📞 [08161316781]

*GHT — Magani cikin Sauki da Aminci*
*“Lafiyar ku shine babban burinmu”*
[10/11, 9:47 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/B6ZgynXRCc3LWNggTkzg7X


*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)


NA


MAMAN AFRAH


. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*

BOOK 1

PAGE 5️⃣

*ZALIKA*

Zaune suke a ƙaton falon da ya gaji da haɗuwa, hira suke sama-sama kowanne yana danna wayarsa. Mubin ne ya jingina da jikin kujera yana ajiye wayarsa a kusa da shi ya kalli Zalika ya ce

"Ina son magana da Baffa amma wallahi tsoro nake" Baki Zalika ta taɓe da kamar ba za ta yi magana ba sai kuma ta ce

"Maganar mai? Kaima da ka shafawa kanka lpia da wannan tunanin ka san dai ko ma wace magana ce Baffa ba saurarenka zai yi ba gwara ma ka faɗawa Mamy, don ni yanzu na cire faɗawa Baffa abu ma saboda ba saurarena zai yi ba" Ta faɗa tana maida hankalin ta kan waya.

Ajiyar zuciya ya sauke ya ce

"Ni ba wata magana nake so mu yi ba kawai dai ina so mu zauna mu tattauna, ina nufin mu yi hira irin na ɗa da uba" Ya faɗa idanunsa suna yin jawur tamkar zai yi kuka hatta a muryarsa raunin hakan ya bayyana.

Zalika ta ce

"Uhum in ji mai ciwon haƙori, ni wallahi har mantawa ma nake da Baffa idan magana ko damuwa ta same ni, kuma ko da na ji shauƙin son magana da shi a matsayinsa na mahaifina ina kawar da hakan domin na san abu ne mai wahala, shi ya nuna ba ya buƙata to mu ma mai zai hana mu danne zuciyarmu?" Iska Mubin ya fesar haɗe da sakin ajiyar zuciya ya ce

"Ni wallahi ina kasa jurewa wani lokacin, abin yana birgeni kuma yana bani sha'awa idan na je gidan abokaina na gansu suna hira ana raha da mahaifinsu amma mu mun mallaki komai na rayuwa amma mahaifinsu bashi da lokacinmu, sannan ba wai ayyukan ne suka masa yawan da ba zai sauraremu ba, shi fa tun asali ma haka yake babu ruwansa da lamarin ƴaƴansa, sai dai Mamy ta maye mana gurbin mahaifi da mahaifiya" Mubin ya faɗa cike da damuwa.

Mamy da take laɓe tana jin su duk sai jikinta ya yi sanyi, tabbas ta san kowane ɗa yana da burin mahaifinsa ya tattuna da shi ya ji damuwoyinsa, amma su basu san daɗin mahaifinsu ba gashi dai yana raye amma sun zama marayu ta ɓangarensa, ita kanta ba ya zama da ita, ƴaƴansu sai ita za ta kula da su, kama daga tarbiyarsu da zama da su ta ji abin da yake damunsu ko shawara fa sauransu.


Shi abin da ya ɗauka guda ɗaya shi ne idan ya ajiye kayan abinci da kuɗi to ya gam da fannin iyali, ya ɗaura ragamar tarbiya da komai a wuyan mahaifiyarsu a cewarsa shi uba ɗaukan nauyin gidan ne kawai ya rataya a wuyansa, ita kuma uwa ita ce za ta basu tarbiya, bai san cewa tarbiya ba ta mutum ɗaya ba ce, tarbiya ta uwa da uba ce duka, ba zai yiwu a ce uwa kaɗai ta ɗauki wannan ragamar ba, don tarbiya ta kowa ce.


A hankali ta fara takowa daga inda take dama a ɗan koridon bedroom ɗinta na ƙasa ta tsaya take jin hirarsu da take dakar mata zuciya. Tana tahowa tana ƙarewa falon kallo yadda aka kashe dukiya a gidan amma kuma an samu naƙasu a wajen gudanar da zaman gidan, ta rasa mijin ta wane irin mutum ne shi kaifi ɗaya da ba ya sauyawa daga kan aƙidarsa.

Tana zuwa cikin falon ta buɗe baki cike da kulawa, fuskarta washe kamar gonar auduga ta yi sallama cike da kulawa da nuna soyayya da ƙauna ga yaran nata, Zalika ce ta amsa ita ma tana murmushi saɓanin Mubin da ya sadda kai bai amsa sallamar ba kuma bai kalli Mamy ba. Duk da Mamy ta ji babu daɗi a ranta na ganin yanayinsa kuma ta san damuwarsa domin ta ji abin da suke tattaunawa, ko da a ce bata ji ba to dama ta san damuwar ƴaƴan nata tun da basu da wata matsala a rayuwa sai ta mahaifinsu, matsala ce wacce tun asali aka tashi da ita kuma ta yi ƙoƙarin kawo gyara da maslaha amma abin ya ci tura!.

Idanunta ne suka nemi fitar da ruwa, amma ganin Zalika ta mayar da hankalinta kwacakom kanta sai ta yi ƙoƙarin dannewa, faɗaɗa fara,arta ta yi ta ƙaraso falon ta zauna tana mai cewa

"To ko dai falon iya ƴan uwa ake buƙata a ciki ni na zo na kawo kaina" Ta faɗa cike da wasa rana son kawar da damuwar da ta gani shimfiɗe a fuskar Mubin, amma har lokacin bai ɗago ba kuma bai yi magana ba. Zalika ce ta ce

"Kai Mamy har ma da wani hirar ƴan uwa da za a ce uwa ba za ta zo ta ji ba, bayan ke kaɗai ce ginshinƙin mu ke kike kulamu ke kike ɗauke duk wani nauyin da zukatanmu suka yi" Ta faɗa tana kallon fuskar mahaifiyar tata.

Mamy ta gane mai qannan kalaman na Zalika suke nufi amma kuma bata son ta ɗora ƴaƴanta a ragamar da za su cigaba da ganin laifin mahaifinsu duk da ta san yanzu sun yi wayo sun fahimci komai game da halayyar mahaifinsu, duk da a baya ma tun suna yara suna iya ganewa domin suna tamabayarta bare kuma yanzu da suka mallaki hankalin kansu.

Cikin zolaya ta sake cewa

"To ai na ga ɗan uwanki ko ɗaguwa bai yi ya kalleni ba, ba dole na ce ko zancen da ya shafi ƴan uwa kuke yi ba" Ta ce tana kallon Mubin.

Mubin wanda rauninsa ne yake son bayyana kamar ba namiji ba abin da ya sa ya ƙu ɗago fuskarsa ba ya so Mamy ta ga yana cikin damuwa kuma ya san damuwarsu damuwarta ce ko kaɗan bata sukuni a duk lokacin da ɗayansu ba ya cikin walawal, sannan abu ɗaya ne ya hana shi yin magana shi ne va ya son muryarsa ta fallasa abin da yake cikin zuciyarsa.

Mamy da take kallonsa cikin sanyin murya ta ce

"Mubin ɗina" Zuciyarsa ce ya ji ta ƙara karaya ya fara tunanin cewa wannan kalmar tana faranta masa rai fite da tunanin mai tunani, sai dai tabbas daga ɓangare ɗaya yake jinta wato ɓangaren mahaifiyarsa, zai so a ce ya ji daga mahaifinsa ma amma ina tun da yake bai taɓa ganin wani sassauci ko kulawa da soyayya daga mahaifi ba. Idan ya ga abokansa suna yabon mahaifinsu a status ko dun ɗora hoton mahaisin suna my hero, farin cikinmu Allah ja da kwana mahaifinmu, wasu suke faɗin mahaifina abokina, wata ta ɗora bani da aboki ko abokin shawara sai mahaifina. Waɗannan kalaman suna sosa masa zuciya abu ne da bai samu ba abu ne da yake ganin mahaifinsa ya tauye musu jin daɗi da kulawa.

Mamy a karo na biyu ta ce

"Mubina ɗina taurarona" Bai san lokacin da ya ɗago kansa ba ya zubawa mahaifiyarsa jajayen idanunsa tamkar ranar ya fara arba da fuskarta, kallonsa suke daga ita har Zalika, idanunsa jajawur fuskarsa cike da damuwa ƙarara, a gefe ɗaya idanunsa suna kwararar da wasu hawaye. Yana ɗagowa sai ya buɗe bakinsa dakyar ya haɗa laɓɓansa ya ce

"Mai ya sa sai mu? Mai ya sa daga ni sai ƙanwata ne muka rasa wannan damar Mamy? Mai ya sa mahaifinmu babu ruwansa da bamu kulawa Mamy, kullum fuskarsa a ɗaure, bama ganin dariyarsa tamkar ba a taɓa halitta tausayinmu a zuciyarsa ba" Zalika ita ma da Mubin ya sosa zuciyarta domin ita ma ƙarfin hali kawai take yi, kalamansa sun tada mata mikin da ke cikin zuciyarta a take nata idanun suka shiga tara ƙwalla, domin ta san a rayuwa babu mai gane damuwarka sai wanda yake cikin irin halin da kake ciki, ma'ana yanzu da take jin kalaman Yayanta da kuma ganin ruwan hawayensa suna kwaranya sai ta ji duk duniya babu wanda zai fahimci damuwarsa sama da ita domin ita ma tana damuwa makamanciyar tasa.


Mamy kuma idanunta ta ɗauke daga kallon Mubin ba tate da ta furta ko uffan ba, ba tare da ta bashi amsa ko da ɗaya ba ce daga cikintambayoyin da ya jero mata ba, amma har ga Allah ji take tamkar ta rushe da kuka ko ta samu sauƙi da salama a zuciyarta a kan halin da take ganin ƴaƴanta a ciki, saboda ta san ita kaɗai ba za ta basu kulawar ɓangare biyu ba ko da ta yi ƙoƙarin hakan su dole zuciyarsu za take wasi-wasi a kan lamuran cikin gidan nasu wanda mahaifin nasu ne sila.

Danna zuciyarta ta yi domin a matsayinta na mahaifiya a gare su babu buƙatar ta nuna rauninta a wannan waje domin damuwar za ta musu illa, hakan ya sa ta ɗago ta yi murmushin yaƙe wanda ya fi kuka ciwo ta ce

"Kowane ɗan adam yana da jarawarsa a rayuwa, sai dai idan ya jure watarana komai zai zama labari, komai zai zama tarihi tamkar ba a taɓa yi ba" Ta faɗa yana ruƙo hannun Mubin ta dawo da shi kusa da ita ya zamana suna zaune a tare Mamy a tsakiya su kuma kowa yana gefenta hannuwanta ta sanya ta dafo kafaɗunsu ta ce

"Ku zama masu jajircewa, ku zama masu riƙe ibada tare da jajircewa a dukkan lamuran rayuwarku, kar ku bari wani abu yale rage muku jin daɗin rayuwa, duk wanda ya riƙe Allah to tabbas ba zai yi nadama ko da na sani ba" Ta faɗa tana juyawa ɓangare Zalika ta kalle ta, ta sake juyawa ɓangare Mubin ta kalle shi, su duka har lokacin da ruwan hawaye a saman fuskar kowa.

Zalika ce ta ce

"Mamy wallahi wani lokacin sai inmke ganin kamar ba Baffa ba ne ya haife mu, to ko yana da wata matar a wani waje da wasu ƴaƴan shi ya sa su yake musu walwala mu yake ƙume mana fuska?"

Kafin Mamy ta yi magana Mubin ya yi karaf ya ce

"Ko dariya ba ya yi, sai fushi da hantararmu kamar dai ba ya son mu, ai na san idan mu kaɗai ne ƴaƴan nasa to zai so shi ma yake zaunawa da mu ko ya bamu kulawa"

Mamy ta ce

"Sau nawa zan faɗa muku ku yi haƙuri ne wai? Na ce muku akwai lokaci yana tafe wataranan mahaifinku zai zama kamar kowane mahaifi"

Zalika ta ce

"Allah ya sa amma dai ina ga sai bayan mun bar wannan duniyar don Baffa ba na jin akwai ranar da zai sauya, ko ya canja ra'ayi.


Mamy ce cike da harzuƙa ta ce

"Wai ya kuke so in yi ne?"

Mubin ya ce


" Mamy mun san kin yi ƙoƙari kuma kina kan yi amma dai ni na san tarbiyya ba ta uwa kaɗai ba ce. Uba yana da rawar gani mai girma a kan iyalansa idan ya nuna ƙauna da kulawa, ya saurari yaransa, zai fi sa su girma da kwanciyar hankali da ƙima, dan aka bar uwa ita kaɗai, yara za su rasa ginshikin ɓangaren uba amma ki yi haƙuri" Mubin ya faɗa yana saka hannu ya ɗauke hannun Mamy daga kafaɗarsa ya miƙewa ba tare da ya ce uffan ba ya bar falon.




*JIDDA*

Gabaɗaya jikinta karkarwa ya fara ganin Umma ta ɗaga hannu za ta sharara mata mari, saboda ta san zafin hannun Umma idan har ta mare ka sai ka gwammace kiɗa da karatu. Domin tana da zafin hannu don hannun ta tamkar hannun wani namiji babu laushi ko kaɗan . Karkarwar da jikinta ya fara kwandon yana neman suɓucewa, Umma wacce sai da hannunta ya kusa isa fuskar Jidda sannan ta hangi Abba ya taho daga hanyar ƙofar gida don alamar farin yadin jikinshi ta hango, sosai faɗuwar gaba ta ziyarce ta amma saboda kissa da kisisina da iya bariki irin na Umma a take ta shiga kokawa da ƙwaƙwalwarta, don ganin ta ƙirƙiri abin da zai gusar da wannan mugun ganin da Abban ya kusa yi.

Cike da tsantsar baki ta saki wata ƴar bazawarar dariya, hannun nan da ta yi niyyar marin Jidda da shi sai ta ƙarasa gefen fuskar Jiddar a hankali ta shafi kuncin Jidda ɗata hannun kuma sai ta riƙe haɓar Jiddar tana cewa

"Allah ya miki albarka Jidda ya baki miji na gari inda za ki huta, ubangiji ya baki ƴaƴa masu miki ɗawainiya kamar yadda kike mini, Allah jiƙan itayenki da rahma" Wannan kalaman na Umma ne ya sa Jidda wacce ta rikice take jiran saukar zazzafan marin na Umma da sauri ta buɗe idanunta tun daga lokacin da ta ji Umma ta shafa fuskarta haɗe da haɓarta amma jin kalaman na Ummar ya ankarar da ita akwai abin da yake faruwa.

Wani yawu Jidda ta haɗiye muƙut, ganin fuskarta ta tsira daga mari, Abba kuwa wanda ya yi mutuwar tsaye da ganin ɗaga hannun Umma mamaki da al'ajabi suka saukar masa ya fara tunanin mene ne halan yake shirin faruwa, sai dai lokacin guda Umma ta sauya masa akalar tunaninsa daga mummunan zaton da ya fara mata zuwa kyakkyawan zato da yake mata a kullum domin kyawawan halayenta da take nunawa a gabansa da kuma rashin nuna bambanci tsakanin Jidda yarinyar da yake riƙo da kuma ƴarta ta cikin ta wato Aliya.

Wata nannuyar ajiyar zuciya ya sauka tare da fata ɗaga sagaggun ƙafafunsa don tun lokacin, da ya ga Umma ta ɗaga hannu ta nufi fuskar Jidda ya ji komai ya tsaya masa cak!.

Baki ya buɗe cike da raha ya yi sallama, a lokacin Umma ta riƙe da gefen kaɗar Jidda, Jidda kuwa sai a lokacin ta gane dalilin da ya sa Umma ta fada aiwatar da ƙudurinta a kanta, yanzu ta fahimci ashe zuwan Abba ne ya dakar da Ummar daga marinta.

Umma kuma cike da nuna bata san da zaman Mai gidan nata a inda yake ba, ta juya da sauri tana ƙara faɗaɗa fara'arta ta shiga amsa masa sallama, tare da ɗauke hannu daga saman kafaɗar Jidda da ta riƙe tana mai cewa

"Maza an Jiddona a je a kai kanukan kicin" Cike da ƙarfin hali Jidda ta amsa mata da faɗin

"To" Tana nufar kicin don har lokacin bata dawo daga duniyar tsoro da fargabar marin da Umma ta yi niyyar mata ba. Umma tana sakin Jiddar ta juya da fara'arta ta irin mutanen kirki masu dattako ta nufi Abba tana ta karɓi ledojin hannunsa tana faɗin


"Sannu da zuwa sannu da zuwa, sannu da zuwa jan gwarzo, uba na gari ga ƴaƴansa miji na gari ga matarsa, Allah bada tsawon rai da kwana mai amfani, an dawo daga hidima da ƙoƙarin nemawa iyali abinci da za su ci, Allah yi jagora ya sauƙaƙa maka hanyar nema" Ta ringa jero addu'ar tana gaba yana biye da ita yana ta amsawa da

"Amin ya rabbil alamin" Ɗakinsa ya shiga, sai da ya zauna a bakin gado ta ƙara masa sannu da zuwa sannan ta fito da ledojin ta damƙawa Jidda a kan cewa komai a ajiye shi a mazauninsa, fruit ɗin kuma ta yanka. Ruwa ta kaiwa Abba banɗakinsa na ɗaki sai da ya shiga wankan ta fito, suna haɗa ido da jidda wacce take zaune da kayan fruit a gaba tana saka su a wata roba mai ruwa tana wankewa, wata gagarumar harara ta jefawa Jidda kamar idanunta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login