Showing 297001 words to 300000 words out of 322641 words

Chapter 100 - DEEN Complete Hausa Novels By Arewa Novels.txt

27 Nov 2025

6205

ma dole don Zainab batanan ko tananan bazan bari kaganta ba don kallon fuskarkama na iya tadomata wani ciwon, so go Zainab batanan, bata garinnan, bata qasarnan koma tananan babu abinda zatayi maka saboda she belongs to someone else now, kotananan bakada hurumin ganinta because she's now someone's wife...she's married"


dagowa yayi ya kalleshi saikuma yadanyi murmushi yana girgiza kai

"daddy I understand bakason komai yasake hadamu da zee, I know abinda kakeyi shine abinda kowanne mahaifi da akayima abu irin wanda nayimaka zaiyi, nasan bakason naganta ne don karna huremata kunne or something like that, please daddy koda agabanka ne ka kirata please hqr Kawai zanbata na nemi yafiyarta"

dan murmushin takaici daddy
"wato ga maqaryaci ko? you think kowa maqaryaci ne kamar kai? believe it or not Zainab is someone else wife dama cemaka akayi tarasa manemane data nace sai kai? mtcheew bala muje" yafada yana qoqarin komawa cikin motar

saikuma yasake juyowa kan Deen dake kallonshi still kamar statue yana qoqarin fassara me daddy kecewa

"for the last time kabarmin kofar gidana for your own good amma"

yana kaiwa nan yashige motar dama bala yashiga suka shiga ciki leaving Deen standing like a tree


kasa gane me daddy ke nufi yayi, jiyayi kamar wani yare yayimashi dabaya fahimta

Zainab? Zainab is married? haba impossible

Kawai daddy beson yaganta ne shiyasa yace hakan amma babu yadda za'ayi ace Zainab tayi aure

da wannan tunanin Deen yadanji zuciyarshi tayi sanyi

qara daga kai yayi ya kalli gate din gidan dakeda tsayi sosai yana tunanin behind this gate akwai muradin ranshi aciki, baxai iya tafiya ba dukda warning dinda daddy yayimashi, he has come this far don Kawai yaganta kozaiji sauqin abinda zuciyarshi kemashi so duk yadda za'ayi duk tsawon lokacin dazai jira saiya jira don baxai zo abanza ba


haka yakoma gefe yasamu dakali ya zauna yana kallon gate din kamar za'a iya budemashi at any moment

haka yaita zama under the scorching sun yana jiran tsanmmani ga wata iriyar yunwa dake kwakularshi don dik yau beci wani abin kirki ba


yana lura da yadda every now and then maigadi ke dan bude qaramin kofar gate din ya leqoshi saikuma yakoma

bece komai ba bekuma tashi ba saima hoping dayake allah yasa daddy yaji tausayinshi ya yarda yaga zee din


ahaka yana zaune marece yayi sosai don har rana tafara alamun faduwa wata mota ta qaraso kofar gidan

dagowa yayi yana bin motar da kallo batareda ya motsq daga inda yake ba

wasu maza biyu cikin shigar shirt and trouser suka sauko daga motar suka nufoshi

har lokacin be motsa ba har suka qaraso wajenshi suna bin juna da kallo

batareda sunce mashi komai ba daya daga cikinsu yakara wayar hannunshi kunne yana cigaba da kallon Deen

"eh alhaji.. gashi nan mun iso... eh mun taddashi.. ok to shikenan" saiya katse wayar sannan yaqara fuskantarshi

"young man meyasa kakeson proving stubborn? mai gidan nan ya buqaci kabarmashi kofar gida amma you stubbornly remain there, did you know what you're getting yourself into?" inji mutumin


Deen dai bece komai ba sai cigaba da kallonshi dayake daga zaune

dayan yazaro ID card yanuna mashi yace
"mu yan sanda ne alhaji yakiramu nan ne don muyi getting rid of you from his house, so for your own good katashi katafi batareda mun tilastaka ba"

sai a lokacin Deen ya bude baki ahankali yace
"zan tafi, amma please kubari naganta... saboda naganta Kawai nataho daga inda nake mai nisa,.I promised idan naganta zan tafi koda bazaku bari nayimata magana ba"

"bakaji yace tayi aure ba? she's married kuma batama qasar kwata2 bare kaganta so is better you leave" inji nafarkon

"tana ciki sir, I know tana ciki Kawai bayaso naganta ne..."

daidai nan aka bude qaramar qofar gate daddy yafito wanda kallo daya zakamashi kasan ranshi a matuqar 6ace yake

"meye kuke jira haka baku tafi dashi ba? eh?"

"alhaji abinda muke niyyar yi kenan, muna qoqarin fahimtar dashi yarinyar bata gidan ne" inji daya daga cikin yansandan

"harsai kun fahimtar dashi? wazai maka qarya anan? wayai maka kama da qaramin mutum anan? who did you think you are da Zainab bazata auri wani ba bayan kai? gani kake don tanasonka bazata iya rayuwa,babu kai ba? inma haka kake gani you're totally wrong, she proved you wrong tunda gashi tayi exactly abinda kake ganin bazata iya ba, tayi moving on tayi aure tana abroad living happily, nobody needs you now so disappear"

Deen dake hawaye tunda daddy yafara magana ya girgiza kai ahankali

"daddy I know I hurt you guys and you're trying to hurt me back too, daddy ko iya nan ka tsaya naji kwatankwaci ko fin abinda nasaku ji, don allah ka sassautamin hakanan, kayi hqr kabari naganta nasan tana nan, Zainab bazata auri wani ba.. kada allah yasa hakan yafaru"

sakin baki daddy yayi yana kallonshi tunda yafara saikuma ya kada kai yace
"saidai atari gaba don hakan yariga yafaru, Zainab saidai wata ba 'yata ba don tayimaka nisa and if you think am lying ga wadannan..." yafada yana watsamashi wasu yan cards

"check and see, fatan hakan zaibaka amsar ka"

bin cards din qasan Deen yayi da kallo saikuma ya tsugunna yayi picking dinsu yatashi yana dubasu


kanshi yayi wani mummunan sarawa lokacin dayayi arba da invitation cards wanda sunan zee ke rubuce 6aro 6aro ajiki amatsayin bride under it kuma sunan namiji ne wanda tashin hankali besa ya iya riqewa ba


"yanzu ai zaka yarda ko tunda kagani da idonka, Zainab is married..happily don haka ka kama gabanka allah ya hadaka da rabonka"

"impossible.." Deen yafada in whisper yana cigaba kallon cards din hannunshi da gajiyayyun idanunshi

"but it is, it's possible don gashi ma kagani.. please officers send him away banason ganinshi anywhere near here"

sakin cards din Deen yayi yanufo daddy dasauri

"no.. daddy please don't do this to me, please" yafada da muryarshi datafi kama da rad'a yana nufo daddy saidai kafin ya iso officers din sun tareshi ganin zai turesu yawuce yasa suka rirrikeshi

"ku sakeni! get your hands off me!" yafada cikin daga murya yana fizgewa da qarfi saidai sun riqeshi gamm

"don't do this to me daddy... please" yasake fada cikin very cracked voice

"kubarmin kofar gida dashi" inji daddy da ko kadan halin da Deen keciki be ta6ashi ba illa wani farinciki da satisfaction dayakeji na ya ramama zee abinda yayi mata

"NO.. Zainab! Zainab!! Zainab please come out am here!!"
yafada cikin daga murya sosai yana qoqarin wucewa gate din gidan amma mutanen sun rirrikeshi

"take him away" inji daddy


"don't do this to me..." yafada qirjinshi na heaving


haka suka janye Deen dake maimaita 'don't do this to me' cikin muryarshi dake fita dakyar suka sashi a motarsu qarama ba irinta yan sanda ba

maimakon ya cigaba da struggling kamar yadda suka zata saigani sukayi ya kife fuskarshi akan.front seat yadafe saitin zuciyarshi da hannu bibbiyu yana sauke numfashi masu nauyi hakan yasa dayan dan sandan saurin zagayawa yashiga mazaunin driver dayan kuma na taredashi abaya riqeda bindiga suka ja motar suka wuce


ajiyar zuciya daddy ya sauke bayan tafiyarsu sannan yajuya yakoma ciki yana fatan yatafi kenan don idan yadawo he won't take it likely with him

saida yaqara bigema su bala da masu gadi warning cewa kada maganar dawowar Deen yasake yayi leak har yaje kunnen mummy sannan yawuce ciki don dama dalilin dayasa bebi da hayaniya ba kenan don beson yajawo hankalin mummy tasan meke faruwa don tsaf zata ruguzamashi shiri


a bangaren Deen kau tunda yakifa kanshi a tafukkan hannunshi be dagoba har suka iso idan suka ja suka tsaya

bubbude kofoffin sukayi suka fita sannan mutumin baya ya fiddoshi ya watsar gefen titi

"go away for your own good, idan kasake komawa we'll make sure you rot in jail" inji dayan sternly

komawa sukayi cikin motar suka ja suka barshi nan


kasa koda motsi yayi a inda yake yashe azaune, misalta abinda zuciyarshi ke going through lokacin abune mai matuqar wuya

jiyake he's world is turning upside down

sai lokacin yasan ashe kuka ma rahama ne don kasayi yayi sai ajiyar zuciya dayake saukewa kawai, tsakanin zuciyarshi da maqoshinshi yarasa wane yafimashi yaji yajin ciwo

har akayi magrib akayi isha'i yana nan zaune inda suka barshi gefen titi

yakasa ko motsawa hannayenshi still dafe dake zuciyarshi dayakejin tanamashi wani bala'in zafi


daga baya ne yasamu yatashi dakyar yafara tafiya,cikin jan qafaffu

tafiya yake batareda sanin inda zashi ba


***




A bangaren kaka kau tunda marece take jiran dawowar Deen amma shiru

wasa wasa har magrib tayi har akayi isha'i shiru hakan yasa hankalinta ida tashi

babu shiri tafito daga gidan don nemanshi ita da daya daga cikin mazan gidan nasu

sosai hankalinta yatashi dukda kwantar mata da hankali da mutumin keyi, gashi babu waya a hannun Deen bare akira aji

abinda yafi dagamasu hankali shine sanin dasukayi kasuwar dayake aikin ana rufeta ne shidda da rabin marece kuma daga nan beda wurin zuwa sai gida don saima yadawo yake sake fita sallar magrib

ganin lallashin da mutanen gidan keyima kaka da kwantar mata da hankalin beyi yasa suka fito din tareda wannan mutumin don cigitawa don suna zaman mutunci sosai da sabbin maqoftansu


gidansu wani saurayi dake qasan layinsu sukaje wanda shima yana zuwa aiki akasuwa saidai ba aikinsu daya da Deen ba

cikin sa'a suka taddashi be dade da dawowa sallar isha'i ba

anan suka tareshi suka gaisa sannan suka tambayeshi don allah ko duk yau yaga Deen akasuwa

amsamasu yayi da shidai gaskiya duk yau bega Deen ba kuma ba laifi ya bibbi ta shagonsu

nan suka sake tambayarshi ko yasan wani daga cikin wadanda suke aiki a shagonsu Deen

saida yadanyi tunani sannan yace eh yasan wani amma ba nan unguwar yake ba

nan suka roqeshi yakaisu ko yaimasu kwatance saiyace to bari yashiga gida yafito saiya rakasu

haka kau akayi babu dadewa saurayin yafito suka hau abin hawa sukaje unguwar dukda bawani nisa ke akwai ba cikin sa'a suka iske wanda sukaje nema a rumfar wani mai shayi

saurayin daya kawosu yaje yakirashi suka dawo wajensu kaka suka gaisa sannan suka tambayeshi yaga Deen yau

amsamasu yayi cewa gaskiya duk yau besa Deen a ido ba don bemazo aiki ba don har jajenshi saida akayi awurin kasancewar basu saba ganin yayi fashin zuwa aiki ba


nanfa hankalin kaka yaqara dugunzuma, kan kace me harta fara kuka tana cewa ina Deen zai shiga cikin garinnan da duka duka ko wata basuyiba acikinshi? ina zata fara nemanshi?


ataqaice dai haka suka koma gida cikin damuwa suka gayawa mutanen gidan nan suma hankalinsu yatashi, duk inda suke tunanin zasu ganshi sunje amma shiru babu shi

qarshe dai nearest police station sukaje suka bada report din 6atanshi inda akayi musu alqawarin bincikashi sannan suka koma gida


ranar yadda kaka taga rana haka taga dare kuka kau tun tanayi har muryarta yabar fita


Washegari ma haka suka tashi da heavy heart, mutanen gidan dayake sunada kirki sosai su sukaita tausar kaka da har wani hiri hiri tayi saboda tashin hankali

ranar ma haka suka dasa neman Deen amma shiru har police station din suka koma suma ba labari


haka suka wuni cikin jimami mutane nadan shigowa sunama kaka jaje, daga baya ma har sanarwa sukakai gidan radio da taimakon su mazajen gidan



sai wajajen isha'i kowa na waje an zazzauna kan tabarma matan gidan sunsa kaka atsakiya sunata qoqari wajen kwantar mata da hankali sukaji sallamar wasu maza daga bakin kofa

amsawa duk sukayi suna bada izinin shigowa wasu maza suka shigo suna cewa ga wannan yaron da ake nema can waje asume


kafin kowa yatashi kaka ta tashi don tunkafin su ida maganar tayi zumbur tamiqe tanufi waje agigice mutanen na maramata baya

daga qarshen dakalin kofar gidan nasu tahangi tarin mutane hakan yasa tanufi wajen tana kuka sosai


ratsa mutanen tayitayi harta qaraso gaban wurin inda taga Deen kwance daya daga cikin mazajen gidan na shafamashi ruwa a fuska

agigice kaka tazube gabanshi tajawoshi ajikinshi tana rusa kuka kamar ranta zai fita

ganin dik shafa ruwan da akayimashi be farkaba yasa mazajen wajen shawarar akaishi asibiti Kawai

haka kau akayi cikin qanqanin lokaci aka samu abin hawa suka saka Deen da har lokacin ke unconscious aciki sai kaka da daya daga cikin mazajen gidan hayansu suka kama hanyar asibiti


suna isa babu 6ata lokaci aka amshesu saboda ganin yanayin dasuka kawo Deen, nan da nan aka hau bashi taimakon gaggawa

tun kaka na kuka har hawayen idanun suka kafe haka sukaita jira waje cikin tashin hankali suna jiran tsanmmani


saida likitoci sukafi awa akanshi sannan suka fito inda suka nemi ganin iyayen yaron

kaka da mutumin sukabi likitan har office dinshi inda anan yake gayamasu halin da Deen yake ciki cewa jininshi yahau sosai ga ciwon zuciya dake barazanar kamashi

sosai hankalin su kaka yasake tashi inda ganin hakan ne yasa likitan kwantar masu da hankali cewa insha komai zaiyi daidai sannan ya rubuta masu magungunna da injections dasuke buqata

haka suka fito daga office din likitan kaka still takasa daina kuka gani take kamar zata rasa Deen ne

lokacin har dayan mijin matan gidan hayansu yaqaraso shima inda da taimakonsu aka siya duk abubbuwan da aka buqata don kaka bawani kudi gareta ba

anan kaka ta kwana tareda Deen wanda da alamu allurar barci sukayi mashi, fuskarshi tayi fayau tafada sosai gwanin tausayi


be farka ba sai Washegari wajajen taran safe

yana tozali da fuskar kaka da tunda yabude ido tayi wajenshi tana kiran sunanshi yafashe da kukan daya kasayi tun a Katsina

kuka yake sosai yana fadin yarasa zee shikenan yarasa zee har abada

ganin yadda yake kukan yasa hankalin kaka sake tashi babu shiri tayi waje don kiran likita


koda suka dawo ma kukan suka tadda yanayi yana shikenan yarasa zee, dakyar Dr yashawo kanshi yaqara yimashi wani allurar barcin wanda yasashi komawa to slumber nan take


sosai kaka tadinga kuka tana kallon Deen daya dawo abin tausayi duk saitaji wani feeling na guiltiness zuciyarta tayimata mugun nauyi sanin cewa kowanne hali Deen yashiga itace sila


lokacin da Deen yasake farkawa beyi kuka ba wannan karon saidai kallo daya zakamashi kasan he's really in pain

he looks so sad and down

and that day mark the beginning of his sorrowful life


kwanansu biyar aka sallamesu saidai kwata2 Deen ya chanza yakoma kamar bashi ba

he's no more the cool and happy Deen, farinciki yayi qaura a rayuwarshi Kawai rayuwa yakeyi batareda yasan dadinta ba

baya murmushi, shirunshi ya ninka nada yakoma wani iri gashinan dai

baya fita saida dalili wanda mostly zuwa masjid ne ko shiga toilet amma daga ba haka ba kodayaushe yana qunqume cikin daki kamar matar kulle

wannan sabon sauyin na Deen ba qaramin sake dagulama kaka lissafi yayiba, wani irin tausayinshi takeji tana kuma rashin kyautawarta na hukuncin data yanke tunfarko, tasan ko mai yafaru itace sila hakan yasa takejin guiltiness sosai

kaka fara jaraba sana'a tayi da yan kudin hannunta don tunda Deen yadawo beqara fita da sunan zuwa kasuwa ba gashi komai nasu qasa yakeyi hakan yasa kaka tattara yan kudinta tafara sana'ar toya fanke dasafe

cikin ikon allah saigashi allah yasama abin albarka don kaka koyaya tayi abu dasunan sana'a sai allah ya albarkaci abin ya buda mata

tun tanayi mutanen cikin gidan kawai na siye har yan waje suma suka gane suna shigowa saye

cikin ikon allah saigashi suna samu suna rufawa kansu asiri da sana'ar


saida Deen yafi wata a yanayin dayake ciki sannan yafara dan samuwa

da taimakon addu'o'i da kaka ke sashi aciki kullum dakuma rubutun dangana datake bashi yaji sauqin abinda yakeji yakuma yi deciding yayi moving on dukda abu ne mai matuqar wuya agareshi

yakasa mantawa da memories din rayuwarshi da zee abaya, jiyake da ana tariya daya tariyo rayuwarshi ta baya sun dawwama acikinta amma hakan be yiwuwa


ganin wahala da fadi tashin da kaka kemasu itakadai don rufama kansu asiri yasa Deen yake shawarar cigaba da fita nema don he can't watch her struggling all alone


ranar daya shirya zaya koma kasuwa farinciki awurin kaka baya misaltuwa don jitake kamar taita rawa don murnar yaronta yafara dawowa

haka taita samashi albarka ta rakashi har waje tana qara godewa allah azuciyarta tana addu'ar allah yasa qarshen wahalar kenan, sosai tayini cikin farinciki don tasan koba komai dan fitan nan dazai dinga yi zai taimaka wajen ragemashi damuwarshi sosai


sosai co-workers dinshi na kasuwan sukayi murnar dawowarshi don babu laifi sundan saba dashi kuma duk sunji abinda yasameshi hakan yasa sukaita mashi ya qarfin jiki yana amsamusu da faint smile dinshi dayanzu yazama shade to his sorrowful state

babu 6ata lokaci yakoma aikinshi kamar da saidai kwata2 yanzu bayajin dadin aikin kamar farko kawai yiyake maganin zaman banza amma har a zuciyarshi aikin bemashi ba bawai don ba'a samu ba Kawai dai yafison yayi wani aikin daya kasance dole akwai experience yakasance aikin hannu daxaka koya ka iya ba wannan da qarfi Kawai yake buqata ba yana son aikin dake buqatar basira kamar dai wancan na capentary dayakeyi a Katsina

hakan yasashi fara neman workshop workshop na capentary don komawa irin aikinshi nada amma duk inda yaje babu vacancy

haka ya cigaba da aikin dakonshi a gefe yana neman aikin capentary amma tsit kakeji

watarana yazo wucewa zaitafi kasuwa yabi tawata gareji daya saba bi idan zai tafi kasuwa, saiya tsinci kanshi da tsayawa ya qurawa wurin ido yana kallon kanikawan dake buge.bugen karafuna

haka Kawai yaji aikin nasu yashiga ranshi farat daya hakan yasa ya qarasa wajen yana kallon mutanen wajen

sallama yayima mutanen wajen wanda hakan ya maido hankalinsu akanshi

amsamashi sukayi suna binshi da kallo hakan yasashi dan sakarmasu murmushi

"erm...dan allah ina ogan garejin nan? nima garejin nakeson fara zuwa idan akwai vacancy, inason fara irin aikinku ne"

kallon juna mutanen da duk samarine sukayi sai daya yace
"kutt... wlh nayi tunanin balarabe ne dafarko, nan jira kawai nake yafara cemana *Hal anta majnunun*"

dariya kingin suka kwashe daita sannan daya yace
"majnunu fa mahaukacine Dogo, kodai anyi asarar kudin laraba ne"

daya yace
"Yo ai dama mahaukacinne, dama kajen haquri yayi da beyi magana ba dasai balaraben ya tambayeshi koshi majnunun ne don akallo daya akegane hakan"

"kai wlh qaryane don ubanka, dani dakai wayafi ruwan mahaukata?" inji nafarkon

haka suka cigaba da caftar mai cikeda ban dariya sukama manta da Deen dake tsaye yana kallonsu

ganin hakan yafara shawarar koya tafine? saikuma yace bari dai yasake masu magana hakan yasashi sake cewa

"don allah.. yana nan ne ogan?"

sai a lokacin suka sake dagowa

"eh to yanzu dai bayanan amma ko yananan dakyar zai daukeka muma kanmu complain yake munyi yawa" inji wani

"sannu.. ina ruwanka da yanke hukunci akaran kanka,kabari yaga ogan mana yagayamashi idan ma munmashi yawan, bansan iyayi... kai balarabe kaje kadawo anjima idan yadawo saika sameshi" inji dayan

"to da yaushe kenan?" inji Deen dake kallonsu

"anjima kadan bayan azahar kadawo nasan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login